Sashe 22
A Garin Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Komawa baya ya yi, ya tsayar da motar, tunda ya dora idon shi akan ta ya manta da tunanin da ke a zuciyar shi ,fita ta yi, matar na ta soya qosai, ba mutane sosai a wajen, saboda hantsi ya fara.
"Assalamu alaikum, baba a bani qosai na nera dari,"
"Wa'alaikumussalam, to yarinya ki dan jira ke ga ni dai akwai wasu gaban ki"
"To Baba"
Lawwali ne cikin hade fuska ya nufi wajen zai magana, Sultana ta marairaice ido, ta masa alamar ya bari, yanayin yanda ta yi ya shige shi, amma sai ya koma ya tsaya a gefen ta, Ita kuwa kallon unguwar take, ta na kuma wa, da alamar su na buqatar taimako,yara baja baja ba masu zuwa makaranta, ita fa ta na son makaranta ,ta na bawa makaranta mahimmanci, ta na son ganin yara na zuwa makaranta, ba ta son ta ga yaran da ya kamata ace su na aji, ta gan su su na wasa a unguwannin su.
Wani yaro ne da zai kai shekara goma sha daya, ya keto a guje ya tada qura, saura kadan ya fadi, cikin qiftawar ido Lawwali ya tare shi, sultana kuwa har ta rufe ido, dan kuwa ta saddaqar zai fadin, shiru ta ji, dan haka sai ta bude ido a hankali,
"Ke gani bai fadi ba? Yara irin wannan sun hi ki son jikin su,"
Cikin murmushi ya fadi hakan, Itan ma murmushi ta mayar masa, tare da maida hankalin ta kan yaron da ke raba ido a tsakanin su.
"Me ya sa ka ke wargi ba ka tai makaranta ba?" (Wargi wasa kenan)
"Ba a biya min kuddin makaranta ba"
"Ina ne gidan ku?"
"Shi na can bayan shiyyar ga"
"Me ya kawo ka shiyyar nan?"
"Wargi nittaho wajen diyoyin innata (wasa na taho wajen yaran innata)"
"Ohh su ma ba su tai makaranta ba kenan"
"Uhm"
"Ok to mu tai na ga gidan ku, za ka kai ni?"
"Mi za ki yi gidan mu?"
Dariya ta yi sannan ta ce,
"Zan gaishe da maman ka ne, na ce ta na da yaro mai hankali"
Shiru yaron ya yi, tare da saurin amshe hannun shi zai gudu, Lawwali ya riqe shi, ya daga fuskar shi, ya na kallon dan baqi kyakkyawan yaron,
"Ina za ka tai,ka rake mu gidan ku mana,"
"Mama ta ta mutu masu halbi na sunka halbe ta, baba na shi na inda likita da Goggo ta, an halbe shi a qafar shi guda,likita ya ce za a yanke,ba kowa gidan mu"
Sultana na jin wannan labari sai hawaye ya fara gangarowa saman kuncin ta, Lawwali kuwa ji ya yi kamar an dora masa wani abu mai nauyi a qirjin shi,tun da ya ke bai taba jin haka ba, ko dan bai taba tsayawa ya yi magana da wanda suke illatawa bane?
Gani ya yi Sultana ta ja yaron ta rungume a jikin ta, ko kula da dattin jikin shi ba ta yi ba.
Mutanen da ke wajen kallon ta suke da mamaki, da kuma birgewa, hankalin mutane ya fara yawa kan su Dan haka mota ta ja yaron suka nufa, ta zauna ya na tsaye gaban ta, ta kira Lawwali, ta bude jakar ta ta debi dubu goma ta ce ya bawa mai qosai, ta qara jari.
Sai ga Mai qosai ta debo qosai me yawa ta kawo ma Sultana ta na ta godiya kamar za ta kwanta mata, ita kuma tana nuna ba komai.
Amsar qosan ta yi, itama ta yi godiya, matar ta tafi, ta na ma Sultana addu'a.
"Ina ne makarantar ku? "
"Makarantar mu na can shiyyar mu, yawancin yaran shiyyar mu da na nan shiyyar ita suka zuwa"
"Za ka raka ni a mota ne ko da qafa?"
"Mu dai tai da qafa,"
Ya na dan dariya ya fadi hakan, Sultana ta fahimta ya na tsoro ne, ba ta ga laifin shi ba, zamani ya sauya, jakarta ta dauka da wayar ta, Lawwali ya kulle mota, suka taka.
Har zuwa makarantar yaran, ana ta karatu, makarantar ga ta nan ne dai kawai, kuma a haka ta kudi ce, sallama ta yi, ta nemi ofishin shugaban makaranta aka kai ta, bata fito ba sai da aka lissafa mata adadin yaran da ba su biya kudi ba, ta yi alqawarin biya, suka bata account No,ta tura musu, sannan ta ce a sanar da yaran su ci gaba da zuwa makaranta, za ta dawo ta duba ko sun dawo,sallama ta musu ta tafi
Lawwali mamaki ya hana shi ma bin ta su tafi, anya Sultana jinin Halliru da Ikeelima ce kuwa?
Tsayawa ta yi a gaban shi ta ce,
"In ka qare kallon nawa mu je ko?"
Murmushin gefen baki ya mata, sannan ya ce,
"Ai ke din ce Ran ki shi dade, bayan kyau da ki ke da shi,har da kyauwun zucciya, "
Kunya ce ta kama ta, ta sunkuyar da idanun ta daga kallon shi, su na tafe su na dan yin hira, ta na jin dad'i in ya yabi kyawun ta, bata sani ba ko dan bata saba jin haka bane oho, kawai dai ta san ta na jin dad'i.
Har suka isa mota, yaron na riqe da hannun Sultana,
"To yanzu ina ne asibitin da Baban ka yake?"
"Babban asibiti ne, amma ban san waje ba, Inna Rabi ta tassan waje,Ga gidan ta can, wancan me buhun"
Bata gaji ba, sallama ta yi suka gaisa da matan gidan, gida ne na haya, mai dakuna da yawa ciki,
Har qofar Innar shi Rabi ya kai ta, suka gaisa, ta mata bayanin haduwar ta da yaron, sai a sannan ne ta tuna bata san sunan yaron ba, Innar shi ce ta sanar da ita sunan shi Huzaifah, sultana sanar da ita tayi ta na son ta je duba mahaifin yaron a asibiti, ya za a yi?
"Dama an jima kadan zanna kai musu abinci, mu tai na rake ki"
Nan da nan ta shiga ta saka hijabi, ta kulle qofar ta, suka fita, motar da ta gani su na nufa ce ta dan tsorata ta, Sultana ta ce,
"In ki na ganin akwai matsala ki min kwatance, zan bide su"
Kunya ce ta kama Rabi ganin Sultana ta gano ta.
Nan dai ta shiga suka tafi har asibitin, ta ga mahaifin Huzaifah, ta biya duk wani abu da ake buqata, bayan nashi ma har da na wasu mutum shida.
Alqawarin sake komawa ta yi, watarana asibitin dan taimakawa masu jinyar.
Sai da suka isa office din su, Sultana ta ke nazarin abubuwan da suka faru, tabbas masu neman taimako na asibiti, da irin unguwannin su Huzaifah, unguwannin talakawa, lallai yau ta samu wata babbar nasara a abinda ta ke da buri, alqawarin taimakawa mabuqata da ta dauka da yardar Allah za ta yi qoqarin cika shi duk da ta sani ba zata iya taimakon kaff mutanen garin Zamfara ba, amma zata qoqarta taimakawa wanda ya samu.
(Shin irin su Sultana ne kawai ya kamata su dinga taimakawa talakawa? Ke me kike aikatawa na taimakon wasu? Kai fa? Mu tambayi kammu, a rayuwa kar mutum ya ce sai ya ci ya tada kai sannan zai bawa wasu, da kadan din da muke da shi da shi za mu taimaki wasu, masu kidnapping har gida wasu masu qarfin halin suke zuwa su yi su tafi, masu asiri da maita har gida suke bi su cutar da mutane, me ya sa masu taimakawa mutane ba su bi gida gida? Ba riya bane dan ka yi abu wasu sun gan ka sanda ka ke yi, niyyar ka ita ce ladan ka, baka sani ba da loma daya da zaka bawa wani ya ci Allah ya maka rahama ,mu kyautata niyya yayin yin aikin alkhairi, in dai mugaye za su bi gida gida su kashe, su sace, su cinye,to kuwa kai mai aikin alkhairi kai ka fi cancanta da ka bi gida gida dan kyautatawa, zamanin magabata na gari har gida suke bin wanda za su taimakawa, me ya sa muka daina? Ladan ne Bama so?)
*Tambaya a gare mu baki daya*
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 21:
Tafiya ya ke a cikin duhun dajin da suka yi wa hanyar mota da kan su, saboda yawan shiga da fita, babu hasken komai, sai hasken futilun motar, qarar tsuntsaye, da wasu dabbobin kawai ke tashi, bai tsaya a ko ina ba sai ginin da yake maboyar su, cikin hanzari ya fita daga motar ya shiga wajen, tun daga bakin qofa har ciki masu gadi ne riqe da muggan makamai, gaisuwa kawai suke miqawa wajen Ogan su da suka yi kewar gani kwana biyu, ya so ko da murmushi ne ya musu, amma bacin ran da ya ke ji ya hana shi sake musu fuska, sun kuma fahimci hakan.
Qofar da za ta sada shi da inda aka ajiye Tsohon Gwamana No 5 ya bude masa, bayan ya gaida shi, daga masa kai ya yi kawai ya shige, a wata kujera da aka tanadar masa ya zauna, tare da harde qafar shi daya saman daya, kallo ya kafe mutanen dakin da shi, ya jima ya na kallon su,daga baya ya ce,
"Wab-bud'e shi?"
(Waye ya bude shi)
Shiru wajen ya dauka, cikin bacin rai Lawwali ya zari bindigar qugun No 3 ya harbi qafar Tsohon Gwamna, wata iriyar qara ya saki, tin qarfin shi, jijiyoyin kan shi da na wuyan shi sun fita rudu-rudu, ya na so ya riqe qafar amma ba hali, saboda an daure hannayen shi, cikin rawar murya ya ce,
"Wata yarinya ce, ......na mata ...alqawarin....million goma....in ta kunce ni.."
Wata dariya Lawwali ya saki sannan ya ce,
"Ku je ku kawo min su Sa'adatu, na ji a cikin su wacce mai qarar kwanan ce tab-bude shi"
No 2 ne ya fita cikin sauri, Lawwali kuwa fada ya fara yi,
"Meye amfanin ka a nan Inuwa( No1) kai ne fa babba yanzu, ka na mi da an ka bude shi, ko ka san hitar shi daga nan, daidai yake da tonuwar asirin mu! "
"Assalamu alaikum, baba a bani qosai na nera dari,"
"Wa'alaikumussalam, to yarinya ki dan jira ke ga ni dai akwai wasu gaban ki"
"To Baba"
Lawwali ne cikin hade fuska ya nufi wajen zai magana, Sultana ta marairaice ido, ta masa alamar ya bari, yanayin yanda ta yi ya shige shi, amma sai ya koma ya tsaya a gefen ta, Ita kuwa kallon unguwar take, ta na kuma wa, da alamar su na buqatar taimako,yara baja baja ba masu zuwa makaranta, ita fa ta na son makaranta ,ta na bawa makaranta mahimmanci, ta na son ganin yara na zuwa makaranta, ba ta son ta ga yaran da ya kamata ace su na aji, ta gan su su na wasa a unguwannin su.
Wani yaro ne da zai kai shekara goma sha daya, ya keto a guje ya tada qura, saura kadan ya fadi, cikin qiftawar ido Lawwali ya tare shi, sultana kuwa har ta rufe ido, dan kuwa ta saddaqar zai fadin, shiru ta ji, dan haka sai ta bude ido a hankali,
"Ke gani bai fadi ba? Yara irin wannan sun hi ki son jikin su,"
Cikin murmushi ya fadi hakan, Itan ma murmushi ta mayar masa, tare da maida hankalin ta kan yaron da ke raba ido a tsakanin su.
"Me ya sa ka ke wargi ba ka tai makaranta ba?" (Wargi wasa kenan)
"Ba a biya min kuddin makaranta ba"
"Ina ne gidan ku?"
"Shi na can bayan shiyyar ga"
"Me ya kawo ka shiyyar nan?"
"Wargi nittaho wajen diyoyin innata (wasa na taho wajen yaran innata)"
"Ohh su ma ba su tai makaranta ba kenan"
"Uhm"
"Ok to mu tai na ga gidan ku, za ka kai ni?"
"Mi za ki yi gidan mu?"
Dariya ta yi sannan ta ce,
"Zan gaishe da maman ka ne, na ce ta na da yaro mai hankali"
Shiru yaron ya yi, tare da saurin amshe hannun shi zai gudu, Lawwali ya riqe shi, ya daga fuskar shi, ya na kallon dan baqi kyakkyawan yaron,
"Ina za ka tai,ka rake mu gidan ku mana,"
"Mama ta ta mutu masu halbi na sunka halbe ta, baba na shi na inda likita da Goggo ta, an halbe shi a qafar shi guda,likita ya ce za a yanke,ba kowa gidan mu"
Sultana na jin wannan labari sai hawaye ya fara gangarowa saman kuncin ta, Lawwali kuwa ji ya yi kamar an dora masa wani abu mai nauyi a qirjin shi,tun da ya ke bai taba jin haka ba, ko dan bai taba tsayawa ya yi magana da wanda suke illatawa bane?
Gani ya yi Sultana ta ja yaron ta rungume a jikin ta, ko kula da dattin jikin shi ba ta yi ba.
Mutanen da ke wajen kallon ta suke da mamaki, da kuma birgewa, hankalin mutane ya fara yawa kan su Dan haka mota ta ja yaron suka nufa, ta zauna ya na tsaye gaban ta, ta kira Lawwali, ta bude jakar ta ta debi dubu goma ta ce ya bawa mai qosai, ta qara jari.
Sai ga Mai qosai ta debo qosai me yawa ta kawo ma Sultana ta na ta godiya kamar za ta kwanta mata, ita kuma tana nuna ba komai.
Amsar qosan ta yi, itama ta yi godiya, matar ta tafi, ta na ma Sultana addu'a.
"Ina ne makarantar ku? "
"Makarantar mu na can shiyyar mu, yawancin yaran shiyyar mu da na nan shiyyar ita suka zuwa"
"Za ka raka ni a mota ne ko da qafa?"
"Mu dai tai da qafa,"
Ya na dan dariya ya fadi hakan, Sultana ta fahimta ya na tsoro ne, ba ta ga laifin shi ba, zamani ya sauya, jakarta ta dauka da wayar ta, Lawwali ya kulle mota, suka taka.
Har zuwa makarantar yaran, ana ta karatu, makarantar ga ta nan ne dai kawai, kuma a haka ta kudi ce, sallama ta yi, ta nemi ofishin shugaban makaranta aka kai ta, bata fito ba sai da aka lissafa mata adadin yaran da ba su biya kudi ba, ta yi alqawarin biya, suka bata account No,ta tura musu, sannan ta ce a sanar da yaran su ci gaba da zuwa makaranta, za ta dawo ta duba ko sun dawo,sallama ta musu ta tafi
Lawwali mamaki ya hana shi ma bin ta su tafi, anya Sultana jinin Halliru da Ikeelima ce kuwa?
Tsayawa ta yi a gaban shi ta ce,
"In ka qare kallon nawa mu je ko?"
Murmushin gefen baki ya mata, sannan ya ce,
"Ai ke din ce Ran ki shi dade, bayan kyau da ki ke da shi,har da kyauwun zucciya, "
Kunya ce ta kama ta, ta sunkuyar da idanun ta daga kallon shi, su na tafe su na dan yin hira, ta na jin dad'i in ya yabi kyawun ta, bata sani ba ko dan bata saba jin haka bane oho, kawai dai ta san ta na jin dad'i.
Har suka isa mota, yaron na riqe da hannun Sultana,
"To yanzu ina ne asibitin da Baban ka yake?"
"Babban asibiti ne, amma ban san waje ba, Inna Rabi ta tassan waje,Ga gidan ta can, wancan me buhun"
Bata gaji ba, sallama ta yi suka gaisa da matan gidan, gida ne na haya, mai dakuna da yawa ciki,
Har qofar Innar shi Rabi ya kai ta, suka gaisa, ta mata bayanin haduwar ta da yaron, sai a sannan ne ta tuna bata san sunan yaron ba, Innar shi ce ta sanar da ita sunan shi Huzaifah, sultana sanar da ita tayi ta na son ta je duba mahaifin yaron a asibiti, ya za a yi?
"Dama an jima kadan zanna kai musu abinci, mu tai na rake ki"
Nan da nan ta shiga ta saka hijabi, ta kulle qofar ta, suka fita, motar da ta gani su na nufa ce ta dan tsorata ta, Sultana ta ce,
"In ki na ganin akwai matsala ki min kwatance, zan bide su"
Kunya ce ta kama Rabi ganin Sultana ta gano ta.
Nan dai ta shiga suka tafi har asibitin, ta ga mahaifin Huzaifah, ta biya duk wani abu da ake buqata, bayan nashi ma har da na wasu mutum shida.
Alqawarin sake komawa ta yi, watarana asibitin dan taimakawa masu jinyar.
Sai da suka isa office din su, Sultana ta ke nazarin abubuwan da suka faru, tabbas masu neman taimako na asibiti, da irin unguwannin su Huzaifah, unguwannin talakawa, lallai yau ta samu wata babbar nasara a abinda ta ke da buri, alqawarin taimakawa mabuqata da ta dauka da yardar Allah za ta yi qoqarin cika shi duk da ta sani ba zata iya taimakon kaff mutanen garin Zamfara ba, amma zata qoqarta taimakawa wanda ya samu.
(Shin irin su Sultana ne kawai ya kamata su dinga taimakawa talakawa? Ke me kike aikatawa na taimakon wasu? Kai fa? Mu tambayi kammu, a rayuwa kar mutum ya ce sai ya ci ya tada kai sannan zai bawa wasu, da kadan din da muke da shi da shi za mu taimaki wasu, masu kidnapping har gida wasu masu qarfin halin suke zuwa su yi su tafi, masu asiri da maita har gida suke bi su cutar da mutane, me ya sa masu taimakawa mutane ba su bi gida gida? Ba riya bane dan ka yi abu wasu sun gan ka sanda ka ke yi, niyyar ka ita ce ladan ka, baka sani ba da loma daya da zaka bawa wani ya ci Allah ya maka rahama ,mu kyautata niyya yayin yin aikin alkhairi, in dai mugaye za su bi gida gida su kashe, su sace, su cinye,to kuwa kai mai aikin alkhairi kai ka fi cancanta da ka bi gida gida dan kyautatawa, zamanin magabata na gari har gida suke bin wanda za su taimakawa, me ya sa muka daina? Ladan ne Bama so?)
*Tambaya a gare mu baki daya*
A GARIN MU
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 21:
Tafiya ya ke a cikin duhun dajin da suka yi wa hanyar mota da kan su, saboda yawan shiga da fita, babu hasken komai, sai hasken futilun motar, qarar tsuntsaye, da wasu dabbobin kawai ke tashi, bai tsaya a ko ina ba sai ginin da yake maboyar su, cikin hanzari ya fita daga motar ya shiga wajen, tun daga bakin qofa har ciki masu gadi ne riqe da muggan makamai, gaisuwa kawai suke miqawa wajen Ogan su da suka yi kewar gani kwana biyu, ya so ko da murmushi ne ya musu, amma bacin ran da ya ke ji ya hana shi sake musu fuska, sun kuma fahimci hakan.
Qofar da za ta sada shi da inda aka ajiye Tsohon Gwamana No 5 ya bude masa, bayan ya gaida shi, daga masa kai ya yi kawai ya shige, a wata kujera da aka tanadar masa ya zauna, tare da harde qafar shi daya saman daya, kallo ya kafe mutanen dakin da shi, ya jima ya na kallon su,daga baya ya ce,
"Wab-bud'e shi?"
(Waye ya bude shi)
Shiru wajen ya dauka, cikin bacin rai Lawwali ya zari bindigar qugun No 3 ya harbi qafar Tsohon Gwamna, wata iriyar qara ya saki, tin qarfin shi, jijiyoyin kan shi da na wuyan shi sun fita rudu-rudu, ya na so ya riqe qafar amma ba hali, saboda an daure hannayen shi, cikin rawar murya ya ce,
"Wata yarinya ce, ......na mata ...alqawarin....million goma....in ta kunce ni.."
Wata dariya Lawwali ya saki sannan ya ce,
"Ku je ku kawo min su Sa'adatu, na ji a cikin su wacce mai qarar kwanan ce tab-bude shi"
No 2 ne ya fita cikin sauri, Lawwali kuwa fada ya fara yi,
"Meye amfanin ka a nan Inuwa( No1) kai ne fa babba yanzu, ka na mi da an ka bude shi, ko ka san hitar shi daga nan, daidai yake da tonuwar asirin mu! "