← Book details Unaisa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 78

Sashe 7

Unaisa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A islamiyyar da Anna ke zuwa tayi wata kawa Anty Nana, wannan Anty Nana kusan kullum tana gidan mu saboda Allah ya Mata yawo, danma ita Anna ba Zama take ba Dan ta koma harkar Saida gwanjo, Amma Kuma ta taka muhimmiyar rawa wajen ganar da Anna hanyar da zata bi, ta Kuma nausar da ita yadda rayuwa take a wañnan zamanin. haihuwar Hunainah wadda ta kasance auta Kuma ta hudu a gurin Anna, Wambai take zuwa tayi tsince tsince ta dawo gida ta siyar daga baya Kuma da likafa ta cigaba se ta siyo Kaya sosae ta jibge a gida, a shekarar da Hunainah ta cika biyu Ina Anna ta Zama wata daban Dan kuwa dealer Kaya take budewa ta siyar ta hada kudin ta. Ga saka da muke Mata, wadda makarantu da dama a kusa damu mu muke musu saka ni da Nuzla, Allah ya albarkaci kasuwancin matar nan se gashi ta hada kudi ta siyar da wani fili da ta taba siya acan bayan mu ta saya gida ta saka Yan haya. Wannan Anty Nana tace Mata ta Kara hada kudi ta saya gida idan ba Haka ba watarana zata rasa inda zamu zauna, kamar Wasa Anna ta hada komai da take dashi ta siyar tabi shawarar Anty Nana ta saya gida Amma a wañnan watan abinci ma se da kyar take iya siya Mana, dole ta samu wani gida take musu girki, idan zata dawo zata taho Mana da abinci muci. Mun Sha wahala sosae ba da Wasa ba, bana mantawa da weekend idan ta tafi gidan aikin ni Kuma se na karbo wankin mutane na zauna nayi na Kai can gidan na shanya su bani kudi, Wanda nake amfani dashi na siyawa Badi'a da Hunainah abinci da rana, mu Kuma se mu hakura har se ta kawo, ga Badi'a da son Madara yadda Bata San Babu ba, Duk abinnan Bata sani ba se watarana ta dawo unexpected ta sameni nida Nuzla min zage muna wankau, ranar seda ta fasa min jikina saboda dukan, a cewar ta ita zatayi Fadi tashi ta samo Mana Abu Amma mu we don't have that right, tun daga ranar ban sake wannan gigin ba. A wañnan shekarar komai yayi tsanani, sau da dama Zan ganta tana kuka idan Hunainah na kukan Yunwa a Haka a daddafe wata ya cika kudin aikin ta Suka iso ta siya Mana kayan abinci, da aka Bata kudin hayar gidan ta se ta koma sanaar ta ta gwanjo, rayuwa ta Dan Zama a bit stable.

Inada shekara Sha biyar, Nuzla nada Sha biyu, Badi'a na da tara ita Kuma Hunainah nada bakwai Haka muke. Wani safiya ta asabar anyi hutu both islamiyya da Boko. Tunda muka tashi Anna ta bar min sallahun ta tafi gidan aikin ta muyi abinci muci, duk Wanda yazo nemanta muce ta tafi ungiwa Dan ba kowa yasan tana aikatau ba, an dai San tana fita tun safe se yamma take dawowa. Hakan yasa muka dakko holiday homework din mu, na fara koyawa Hunainah tracing kafin na koma Kan Badi'a, na Gama da ita na dawo Kan Nuzla da tace min ta kasa composing poem da aka saka ta tayi, na zauna da kyar na Mata sannan na koma Kan nawa, Haka abin yake kullum, Allah ma yasa dukkan mu kokari ne damu shiyasa wahalar take raguwa. Bayan mun Gama Nuzla ta hado kayan da mukai amfani dashi kanana ta wanke mana tas ni Kuma na daura Mana danwake da zamuci for breakfast, kawai se muka ji sallamar Baba, dukka muka amsa ya dawo bayan shekara da shekaru. Muka Masa sannu da zuwa ya shige daki abin shi ya barmu. Nuzla ta dubeni tace

" Adda ya zamuyi Anna Bata nan"

Nayi shiru Ina tunani nace

" Kawai muce ta je suna ko?"

Se muak gyada Kai, seda na sauke abinci sannan na bawa Badi'a ta Kai masa, se yace tace min nazo, na saka hijabi na Dake Kan igiya na Shiga dakin Yana zaune Yana ta jefa danwake a bakin shi, a raina nace kamar ya bada kudin flour se wani ci yake.

" Ke Baki San kice min sannu da zuwa ba? Yara duk Babu tarbiyya"

Nayi kasa da kaina Ina jin Babu dadin yace min bamuda tarbiyya, a ganina duk kokarin da Anna keyi ganin ta tarbiyantar damu daidai Amma shi da ko kadan Bai bada gudunmawa ba zaice Haka, se hawaye ya fara zubo min, Bai ma lura ba yace

" Ina iyar ku?"

Na dan diririce Ina share hawayen fuskata nace

" Ta...taje suna can Brigade"
.
Ya gyada Kai yace na tafi, Babu musu kuwa na fice Ina sakin ajiyar zuciya. Seda muka Gama cin abinci sannan Badi'a tayi wanke wanke a hankali kamar marar laka, Haka take ita din ajebo ce of highest order! Shiru shiru Anna Bata dawo ba har shida shi Kuma se tambaya ta yake Yi se yaushe zata dawo nace ai bansan me yasa Bata dawo ba. Hankalina ya tashi ganin har Bayan ishai, har Hunainah da Badi'a sukai bacci Bata dawo ba se wajen Tara naji sallamar ta, nayi wuf na tafi zaure , a matukar gajiye Haka fuskarta ta nuna nace

"Anna me ya faru yau kin dade?"

Ta danyi tsaki tana Mika min kayan hannun ta tace

" Wallahi aikin ne se a hankali, me gidan ne yayi Baki Dole seda muka Kara daura wani abincin"

A hankali nace

" Anna wannan mutumin ya dawo"

Tace

" Waye?"

Nace

" Baba fa"

Se ta dafe kirjinta nace

" Amma nace Masa suna kikaje, mu shiga Kar yaga na Dade"

Mun jiyowa se muaki kicibis da bawan Allah ya nade hannun sa Yana kallon mu, ya saka hannu ya kwada min marin da shi ne karon farko Kuma Karo na karshe da aka marenu, kafin nakai hannuna, Anna ta riko ni tana fadin

" Me yasa zaka mare ta? Laifin me tayi maka"

Ya Mata wani bansan kallo yace

" Ke kin Isa kice wani Abu, mayaudariya Maci Amana. Dama ance fita kike Yi idan bana nan. Ga Yara nan dukka sunyi wata irin Kama.."

" Yahai! Ka tsaya da duk abinka akai na Amma karka Bata min nasabar Yara na, me yasa bazan fita ba? Ka bar Mana abinda zamu ci ne? Ka tafi uwa duniya ka barni da Yara da auren ka. Wallahi Yahai ko zaka Fadi ka mutu a gabana bazan taba yafe maka ba"

Ya daga hannun sa ya dauke ta da Marin da seda ta sake ni, na saki kuka Ina rike hannun ta ji nayi duk duniyar tana juya min,

" Na fada Yahai, bazan yafe maka ba Koda shi kadai ne abinda zaka je aljanna wallahi se de kaje wuta, idan kana ganin banida gata banida kowa ka sani Allah shi ne gata na, Kuma zakI daka sanin abinda ka Mana"

" Tunda har kinsan na fada ki fada to se ki je na sake ki saki daya, saki biyu!! Babu ni Babu ke, ki tafi can da Yayanki"

Wannan shi ne mafarin komai, shi ne silar bunkasar mu yayinda ta Zama ta rushewar sa!

Unaisa is not free, pay N300 to 3091721807 A'isha kwalam Hassan first Bank of Nigeria and send evidence of payment to 09063467258
[5/11, 6:00 AM] Hauwa Galadima: 🧕 UNAISA 🧕

*G*

Ayshatuuu

Se lokacin ta gane abinda Anty Nana je nufi da maganar ta, ta Kama hannuna muka shiga ciki Ina kuka, tana Yi Nuzla nayi, ta kwashe kayan mu Ina Taya ta, a Daren bamu runtsa ba ta kwashe kayan ta, ta Jirge gado da komai nata asuba nayi Muna sallah ta dauki mayafin ta ta fice, kafin bakwai ta dawo da me mota da Kuma Anty Nana se makwabciyar mu umma da suek shiri ta shigo, munata baccin gajiya a parlor, seda ta kwashe komai nata tas sannan ta kwashe mu muka tafi, Allah ya rufa Mana asiri ta saya wannan gidan da sede muje karkashin gada mu zauna. Muka koma sabuwar unguwa anan cikin Kano, gidan karami ne me dakuna biyu se bandaki da Kuma kitchen kwaya daya, se shago Wanda kofar shi take a waje. Anna tasa aka rufe kofa aka dawo da kofar ciki, tsakar gidan karami ne da rijiya ta ruwa. Haka Suka Taya ta ta shirya komai da se yamma lis sannan aka Gama Suka tafi. Daki daya tasa kayan gadon ta da wardrobe, dayan shagon tasa kujerun ta, se dayan tasa Mana katifar mu da jakunkunan makarantar mu. Da daddare muka kwanta, duk farkawar da nake tana zaune a sallayya tana kuka, seda mukai wajen kwana uku sannan ta hada kanmu muka tafi Masaya bisa shawarar Anty Nana. Muna zuwa ko karasawa gidan dagaci bamuyi ba, aka dinga Mata Ihu tsintacciyar mage Bata mage,Ashe dama mu din ba yayan Yahai bane yawo takeyi, Haka ta dinga kuka muna Taya ta ta juyo muka dawo Kano. Ka guji macen da akai wa laifi. Kafin mu koma makaranta ta rage damuwar ta, ta samo Mana makaranta sabuwa kusa damu, kullum ta zauna se tace Mana

" Unaisa, Nuzla, Badi'a da Hunainah.."

Wadda ba lallai tana fahimtar maganar da Anna keyi ba.

"...Duk wannan abinda nakeyi Dan ku nakeyi, Ina son kuyi karatu ku fitar Dani kunya, Ina son yadda mahaifin ku ya wulakanta ku, dangin shi Suka ki karbar ku, kusa su zo da kansu su roki gafarar ku Yayana, ku wanke min bakin cikin shekara goma Sha shida na kunsa a wajen mahaifin ku. Daga yau ni kawar ku ce, ko menene kuzo ku fada min"

Wannan kalaman nata seda muka haddace shi a kwakwalwar mu, se ya zamana rayuwata gani nake Dan ita nake, komai nake se na tuna wannan maganar tata. Ance zafin nema baya kawo samu inji BAHAUSHE, gaskiya ba Haka bane Dan kuwa kafin shekara ta rufa Anna tayi gaba se de ka tada Kai kallo, mussamman kasancewar mu farkon tarewa a unguwar ya zamana kusna ta kafa kanta a Sanaa. Kayan gwanjo har daga saudiyya ake Aiko Mata ta Zama babbar mace mu kanmu se rayuwa tayi afuwa sosae, Amma kullum tana tuna Mana kada mu manta wahalar da muka Sha, kada Kuma mu manta kanmu.

Bayan shekara uku
Chapter 7 · 0% Book details