Sashe 89
Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A da niyyar shi ya balbale ta da fada amma ganin yadda idanunta suka kada suka yi jajir tabbacin ta ci kuka ta koshi sai kawai ya sake jan wani dogon tsakin, ya juya ya ce
ba kya ji ne? Ana a daura belt kada Allah yasa ki daura ni meye nawa a ciki?
Ta yi murmushi a ranta ta ce in babu naka, meye naka na tasowa daga mazaunin ka? Har suka fito daga jirgin babu wanda ya sake cewa da dan uwan sa uffan.
Tajuddeen na jiransu cikin motar Faisal kirar porsche, ya debe su zuwa NNPC Ktrs. Tsarin gidajen ya burgeta kuma gidan su yafi duk gidajen tsari da sabunta. Tun daga (gate) ta yaba da tsarin rayuwa irin na Faisal mai cike da tsabta, hatta cikin shukokin sa babu rubbish na ganye ko daya koina tsaf-tsaf.
Tsayawa ma fadin irin dukiyar da Daddy, Hajia, Aunty Saratu, Hajiya Hadiza, Hajjo da Amb. Bashir suka narkar a gidan Intisar abin ma sai ya zama kauyanci, duk da anyi mata babban jeren a gidan su na Maitama ne.
Wannan komi a saukake yake (English Parlour) Koina an shinfide mata shi da marbles har jikin bango, wasu irin yan uban su leather seat (Chinese) da Daddy yayo odar su musamman daga China haka chinese-carpet din da ke malale a tsakiyar falon bata taba ganin irin shi ba a duk yawon da take cikin duniya.
Nan ta cillar da jakarta ta zauna cikin kujera cike da gajiya, ga yunwa dake addabar ta. Ta kai hannun ta na dama ta dafe goshinta dake sarawa, yayinda tayi amfani dana hagun wurin dafe cikinta ko ta danne kugin da akuyar cikinta ke ta yi.
Tajudeen ya shigo yana ta mata barkwanci irin nasa, jin sa kawai ta ke amma shi kansa biyu biyu take ganin sa sabida yunwa.
Shima da ya ga ba fuska bai dade ba ya yi masu sallama ya tafi, da alkawarin gobe bayan ofis zai biyo Faisal ya yi mata hira. Faisal matattakalar dake falon yabi zuwa dakunan barci guda uku dake saman bene a ransa yana cewa wai Baby jira take yace da ita ga dakinta? Ai ko tana da aiki, sai dai in ta kwana a falon.
Taga dai zaman haka ba zai mata ba, don in yunwar zata kasheta ba zai kulata ba, sai ta dauki Jakarta ta rataya ta bi hanyar da ya bi, wai ko ta samu kitchen a can, bata sani ba (kitchen) din ma kofarsa na nan cikin falon don dai labule ya rufe ta ne.
Ta kusa kaiwa matattakalar karshe kenan dunduniyar takalminta ta makale daga matattakalar baya ta kuwa sulmiyo daga benen ta baya tana mirginowa (step-by-step) har tsakiyar falon, ta fada kan hannunta na dama ji kake kas, kashin Amarya ya targade.
Da ta daddage ta zuba wata irin kara ba Faisal dake cikin gidan ba, hatta makotansu Franklyn da matarsa Chinyere sai da ta firgitasu suka kuma shigo gidan suna buga musu kofa don su ji ko lafiya?
A lokacin yana tahiyya ne don sallame sallar Isha’i data riskesu a hanya, don haka saida yai sallama kana ya taho yana hada matakala biyu-biyu-hur-hudu, yayi wanka yana sanye da jallabiyya fara sol, ya ciccibeta ya aza bisa rest-chair kamin ya je ya bude kofar su Franklyn su shigo suna tambayar sa what happen with his bride?
Ya ce cikin matsanancin tashin hankali shima bai sani ba, amma yana zatan zamowa tayi daga bene.
Ita ko sai kuka take tana kiran hannunta, wayyo Mamana, wayyo Daddy kun kawo ni inda zan mutu! Kai abin na Intisar har da karawa aya zaki.
Gaba daya ya rikice idan kuma ya kai hannu kan hannun da ake cewa yana ciwon a kwalla mishi wata matsiyaciyar karar da ke kara gigita shi. Chinyere ta ce taimaka mu kama ta Oga mu kai ta asibiti, wannan hannun da kyar in ba karaya ba ce (Faisal Makarfi, shine G.M watau General Manager na NNPC gaba daya da ke rike da reshen Jihar Lagos a yanzu. Gaba daya ya dauketa cancaras tamkar ya dau yar Baby, suka shiga motor Franklyn zuwa wani (private-hospital) da ke kusa da su.
Nan da nan likitan kashi ya karbeta yana dubawa yace ba karaya ba ce, gocewar kashi ne. Nan da nan ya hau gyara tana ihu tana faman kiran Daddy da mama, yau har Hunainah ta sha kira wajen gyaran hannun nan Faisal ya rasa inda zai sa ransa sabida damuwa, bai san hawaye yake ba sai da ya ji dandanon gishiri a bakinsa.
Yayi saurin sharewa da hannun shi kada Franklyn da ake baiwa (order) a ofis yaga kukan G.M gaba daya akan ciwon matar shi. Likitan yayi mata allurai biyu ya kuma umarci a siyo magungunan da ya rubuta yanzun nan a bata idan ta ci abinci.
Sai a lokacin ma ya tuna rabonta da abinci a saninsa tun daren jiya daya shiga dakin Anti neman Najib ya ganta suna ci da Anti Hajjo. Franklyn shi ya tafi sayen maganin nan cikin asibitin inda Chinyere ta ja mota ta koma gida kawo abinci. Har zuwa lokacin kuka kawai takeyi mai cike da kissa, shi kansa kukan bana zafi bane na jin dadin ganin yadda Ya Faisal ya gigice da ciwonta ne, ashe dai still akwai wannan burbushin son ko yaya yake? Ba tayi tsammanin tana da sauran gurbi a zuciyarsa ba in tayi laakari da irin halin ko in kula da yake nuna mata.
Ya zauna a gefen gadon da take kwance, yayi tagumi ya kasa cewa komi, can kuma ya sauke tagumin ya ja kujera dai-dai fuskar ta ya zauna, sannan yai karfin hali yace.
Don Allah Baby kiyi shiru, kin san me Hajiya tace da ni kuwa? Cewa tayi in kika kara kuka a dalilina bata yafe mun ba, kina so bakin uwa ya lalatani? Ta girgiza kai da sauri, sannan ta kama share hawayen. Ya dafe kai da dukkan hannuwan shi biyu, zuciyar shi na wani irin bugu da sauri-da-sauri.
Dai-dai nan Franklyn ya kwankwasa kofar yayi mai iznin shigowa, ya kawo magungunan cikin ledar asibitin da ruwan swan babbar roba, ya ce cikin harshen turanci ranka ya dade akwai masu sayar da gasassun kaji anan tsallake, ko a sayo ne?
Ya ce aah, Chinyere ta ta tafi ta kawo abinci, mu bata minti goma mu gani Franklyn ya juya ya fita yayinda shi kuma ya maida raunannun idanun shi a kanta, har barci ya soma fizgar ta kadan-kadan.
Ya so ace ta bude ido ya tambayeta yadda akai ta fado daga bene, amma itama kamar ta fahimci take-taken shi na neman a shirya shi yasa ta tamke idon ta a zuwan barci take, farin-ciki fal a zuciyarta.
Ta godewa cokalelen takalminta da yayi sanadiyyar fadowarta daga bene da bata san yaushe Faisal zai kula ta bama balle har ya nuna damuwar shi a kanta irin haka, wato shine Aunty Saratu ke cewa ta kirkiri ciwon karya, sannan ne zata gane Ya Faisal din ya damu da ita ko bai damu da ita ba?
Allah sarki Antinta, ashe itama abin ya dameta, kamar yadda ya addabi rayuwarta?
Chinyere tayi nocking ta shigo rike da warmers din abinci kanana guda uku cikin Kwando, da leda cike da apple da lemun zaki manya manya, ta aje bisa dan tebir dake gaban gadon Intisar suna magana da Faisal cikin yarbanci, ta bi bayan mijinta bayan ta jawo masu kofar.
Haka ya zauna shiru ya rasa abinda ke mai dadi, in ya kai hannu da niyyar ya tasheta taci abinci sai kuma ya fasa, don yana tsoron kukan nan nata mara sauti dake girgiza mai zuciya. Nan dai ya zuba mata ido wata irin kauna da soyayya na ratsa shi, ya rasa abinda zai yi. Gaba daya ya mance komi, sai kaunar Intisar din shi dake azalzalarshi a zuci da ruhi, wata da watanni, kwana da kwanaki, shekara da shekaru. Yau gata a matsayin mallakin shi amma ya bari Shaidan yana kada mishi gangi da wani shirme na banza wanda ita ya lura bai dameta ba; abinda ta san dai-dai da rayuwarta ne shi kawai take yi. Bai sanda ya bi ya kwanta a bayanta ba, ya rungumeta cikin wani irin yanayi mara fasaltuwa da bai taba tsintar kanshi a cikin irinsa ba. Ita kam in banda ajiyar zuciya ba abinda take yi, kamin wasu hawaye masu dumi (warm-tears) su malalo ta gefen idonta. Hawayen farin-ciki na karshe a rayuwarta.
Ta bude idanuwanta farrr! A kanshi, ya juyo ta sosai suka dubi juna, yayi wani murmushi da rabon da ta ganshi yayi irinsa tun tana makaranta a Riyadh, ya lumshe idonshi ahankali, ya ce,
“Please forgive me Inti na, ban san me ke damuna ba, ban san abinda ke min ciwo ba. Ba mamaki ina da tabin hankali a kan kaunarki shiyasa na kasa amincewa da ke tun bayan da kike son Alameen.�
Ta toshe mai baki ta soma rero mai kukan da ke azabtar da zuciyar shi.
Ya ce “Please please Inteesar na roke ki, don Allah in zaki azabtar da ni bata wannan hanyar ba, bata wadannan hawayen da kike ta zubarwa a dalilina ba, kuskure ne na san nayi amman kema ai da laifin ki, baki san yadda zaki baiwa matun hakuri ba balle ki nuna kin san abinda yake ciki, ko ki nuna dan I care, aah, ke kanki kawai kika sani. Amma ai kema dai Baby kin san I can’t do without you.�
Ta lumshe idon ta a hankali, wani matsanancin farin-ciki da bata taba ji ba yana ratsa ta, ta ce, “Amma dai Ya Faisal sanin kanka ne ko zan so wani a rayuwata ba zan so shi irin yadda na soka ba? Kuma komai ai mukaddari ne daga Allah, rayuwar mu duka a rubace take a Lauhul-Mahfuz ba mu muke tsarawa kan mu rayuwa ba. Kuma na dauka da kai da Alameen duk abu daya ne, ba banbanci?
ba kya ji ne? Ana a daura belt kada Allah yasa ki daura ni meye nawa a ciki?
Ta yi murmushi a ranta ta ce in babu naka, meye naka na tasowa daga mazaunin ka? Har suka fito daga jirgin babu wanda ya sake cewa da dan uwan sa uffan.
Tajuddeen na jiransu cikin motar Faisal kirar porsche, ya debe su zuwa NNPC Ktrs. Tsarin gidajen ya burgeta kuma gidan su yafi duk gidajen tsari da sabunta. Tun daga (gate) ta yaba da tsarin rayuwa irin na Faisal mai cike da tsabta, hatta cikin shukokin sa babu rubbish na ganye ko daya koina tsaf-tsaf.
Tsayawa ma fadin irin dukiyar da Daddy, Hajia, Aunty Saratu, Hajiya Hadiza, Hajjo da Amb. Bashir suka narkar a gidan Intisar abin ma sai ya zama kauyanci, duk da anyi mata babban jeren a gidan su na Maitama ne.
Wannan komi a saukake yake (English Parlour) Koina an shinfide mata shi da marbles har jikin bango, wasu irin yan uban su leather seat (Chinese) da Daddy yayo odar su musamman daga China haka chinese-carpet din da ke malale a tsakiyar falon bata taba ganin irin shi ba a duk yawon da take cikin duniya.
Nan ta cillar da jakarta ta zauna cikin kujera cike da gajiya, ga yunwa dake addabar ta. Ta kai hannun ta na dama ta dafe goshinta dake sarawa, yayinda tayi amfani dana hagun wurin dafe cikinta ko ta danne kugin da akuyar cikinta ke ta yi.
Tajudeen ya shigo yana ta mata barkwanci irin nasa, jin sa kawai ta ke amma shi kansa biyu biyu take ganin sa sabida yunwa.
Shima da ya ga ba fuska bai dade ba ya yi masu sallama ya tafi, da alkawarin gobe bayan ofis zai biyo Faisal ya yi mata hira. Faisal matattakalar dake falon yabi zuwa dakunan barci guda uku dake saman bene a ransa yana cewa wai Baby jira take yace da ita ga dakinta? Ai ko tana da aiki, sai dai in ta kwana a falon.
Taga dai zaman haka ba zai mata ba, don in yunwar zata kasheta ba zai kulata ba, sai ta dauki Jakarta ta rataya ta bi hanyar da ya bi, wai ko ta samu kitchen a can, bata sani ba (kitchen) din ma kofarsa na nan cikin falon don dai labule ya rufe ta ne.
Ta kusa kaiwa matattakalar karshe kenan dunduniyar takalminta ta makale daga matattakalar baya ta kuwa sulmiyo daga benen ta baya tana mirginowa (step-by-step) har tsakiyar falon, ta fada kan hannunta na dama ji kake kas, kashin Amarya ya targade.
Da ta daddage ta zuba wata irin kara ba Faisal dake cikin gidan ba, hatta makotansu Franklyn da matarsa Chinyere sai da ta firgitasu suka kuma shigo gidan suna buga musu kofa don su ji ko lafiya?
A lokacin yana tahiyya ne don sallame sallar Isha’i data riskesu a hanya, don haka saida yai sallama kana ya taho yana hada matakala biyu-biyu-hur-hudu, yayi wanka yana sanye da jallabiyya fara sol, ya ciccibeta ya aza bisa rest-chair kamin ya je ya bude kofar su Franklyn su shigo suna tambayar sa what happen with his bride?
Ya ce cikin matsanancin tashin hankali shima bai sani ba, amma yana zatan zamowa tayi daga bene.
Ita ko sai kuka take tana kiran hannunta, wayyo Mamana, wayyo Daddy kun kawo ni inda zan mutu! Kai abin na Intisar har da karawa aya zaki.
Gaba daya ya rikice idan kuma ya kai hannu kan hannun da ake cewa yana ciwon a kwalla mishi wata matsiyaciyar karar da ke kara gigita shi. Chinyere ta ce taimaka mu kama ta Oga mu kai ta asibiti, wannan hannun da kyar in ba karaya ba ce (Faisal Makarfi, shine G.M watau General Manager na NNPC gaba daya da ke rike da reshen Jihar Lagos a yanzu. Gaba daya ya dauketa cancaras tamkar ya dau yar Baby, suka shiga motor Franklyn zuwa wani (private-hospital) da ke kusa da su.
Nan da nan likitan kashi ya karbeta yana dubawa yace ba karaya ba ce, gocewar kashi ne. Nan da nan ya hau gyara tana ihu tana faman kiran Daddy da mama, yau har Hunainah ta sha kira wajen gyaran hannun nan Faisal ya rasa inda zai sa ransa sabida damuwa, bai san hawaye yake ba sai da ya ji dandanon gishiri a bakinsa.
Yayi saurin sharewa da hannun shi kada Franklyn da ake baiwa (order) a ofis yaga kukan G.M gaba daya akan ciwon matar shi. Likitan yayi mata allurai biyu ya kuma umarci a siyo magungunan da ya rubuta yanzun nan a bata idan ta ci abinci.
Sai a lokacin ma ya tuna rabonta da abinci a saninsa tun daren jiya daya shiga dakin Anti neman Najib ya ganta suna ci da Anti Hajjo. Franklyn shi ya tafi sayen maganin nan cikin asibitin inda Chinyere ta ja mota ta koma gida kawo abinci. Har zuwa lokacin kuka kawai takeyi mai cike da kissa, shi kansa kukan bana zafi bane na jin dadin ganin yadda Ya Faisal ya gigice da ciwonta ne, ashe dai still akwai wannan burbushin son ko yaya yake? Ba tayi tsammanin tana da sauran gurbi a zuciyarsa ba in tayi laakari da irin halin ko in kula da yake nuna mata.
Ya zauna a gefen gadon da take kwance, yayi tagumi ya kasa cewa komi, can kuma ya sauke tagumin ya ja kujera dai-dai fuskar ta ya zauna, sannan yai karfin hali yace.
Don Allah Baby kiyi shiru, kin san me Hajiya tace da ni kuwa? Cewa tayi in kika kara kuka a dalilina bata yafe mun ba, kina so bakin uwa ya lalatani? Ta girgiza kai da sauri, sannan ta kama share hawayen. Ya dafe kai da dukkan hannuwan shi biyu, zuciyar shi na wani irin bugu da sauri-da-sauri.
Dai-dai nan Franklyn ya kwankwasa kofar yayi mai iznin shigowa, ya kawo magungunan cikin ledar asibitin da ruwan swan babbar roba, ya ce cikin harshen turanci ranka ya dade akwai masu sayar da gasassun kaji anan tsallake, ko a sayo ne?
Ya ce aah, Chinyere ta ta tafi ta kawo abinci, mu bata minti goma mu gani Franklyn ya juya ya fita yayinda shi kuma ya maida raunannun idanun shi a kanta, har barci ya soma fizgar ta kadan-kadan.
Ya so ace ta bude ido ya tambayeta yadda akai ta fado daga bene, amma itama kamar ta fahimci take-taken shi na neman a shirya shi yasa ta tamke idon ta a zuwan barci take, farin-ciki fal a zuciyarta.
Ta godewa cokalelen takalminta da yayi sanadiyyar fadowarta daga bene da bata san yaushe Faisal zai kula ta bama balle har ya nuna damuwar shi a kanta irin haka, wato shine Aunty Saratu ke cewa ta kirkiri ciwon karya, sannan ne zata gane Ya Faisal din ya damu da ita ko bai damu da ita ba?
Allah sarki Antinta, ashe itama abin ya dameta, kamar yadda ya addabi rayuwarta?
Chinyere tayi nocking ta shigo rike da warmers din abinci kanana guda uku cikin Kwando, da leda cike da apple da lemun zaki manya manya, ta aje bisa dan tebir dake gaban gadon Intisar suna magana da Faisal cikin yarbanci, ta bi bayan mijinta bayan ta jawo masu kofar.
Haka ya zauna shiru ya rasa abinda ke mai dadi, in ya kai hannu da niyyar ya tasheta taci abinci sai kuma ya fasa, don yana tsoron kukan nan nata mara sauti dake girgiza mai zuciya. Nan dai ya zuba mata ido wata irin kauna da soyayya na ratsa shi, ya rasa abinda zai yi. Gaba daya ya mance komi, sai kaunar Intisar din shi dake azalzalarshi a zuci da ruhi, wata da watanni, kwana da kwanaki, shekara da shekaru. Yau gata a matsayin mallakin shi amma ya bari Shaidan yana kada mishi gangi da wani shirme na banza wanda ita ya lura bai dameta ba; abinda ta san dai-dai da rayuwarta ne shi kawai take yi. Bai sanda ya bi ya kwanta a bayanta ba, ya rungumeta cikin wani irin yanayi mara fasaltuwa da bai taba tsintar kanshi a cikin irinsa ba. Ita kam in banda ajiyar zuciya ba abinda take yi, kamin wasu hawaye masu dumi (warm-tears) su malalo ta gefen idonta. Hawayen farin-ciki na karshe a rayuwarta.
Ta bude idanuwanta farrr! A kanshi, ya juyo ta sosai suka dubi juna, yayi wani murmushi da rabon da ta ganshi yayi irinsa tun tana makaranta a Riyadh, ya lumshe idonshi ahankali, ya ce,
“Please forgive me Inti na, ban san me ke damuna ba, ban san abinda ke min ciwo ba. Ba mamaki ina da tabin hankali a kan kaunarki shiyasa na kasa amincewa da ke tun bayan da kike son Alameen.�
Ta toshe mai baki ta soma rero mai kukan da ke azabtar da zuciyar shi.
Ya ce “Please please Inteesar na roke ki, don Allah in zaki azabtar da ni bata wannan hanyar ba, bata wadannan hawayen da kike ta zubarwa a dalilina ba, kuskure ne na san nayi amman kema ai da laifin ki, baki san yadda zaki baiwa matun hakuri ba balle ki nuna kin san abinda yake ciki, ko ki nuna dan I care, aah, ke kanki kawai kika sani. Amma ai kema dai Baby kin san I can’t do without you.�
Ta lumshe idon ta a hankali, wani matsanancin farin-ciki da bata taba ji ba yana ratsa ta, ta ce, “Amma dai Ya Faisal sanin kanka ne ko zan so wani a rayuwata ba zan so shi irin yadda na soka ba? Kuma komai ai mukaddari ne daga Allah, rayuwar mu duka a rubace take a Lauhul-Mahfuz ba mu muke tsarawa kan mu rayuwa ba. Kuma na dauka da kai da Alameen duk abu daya ne, ba banbanci?