Sashe 78
Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kayan wasa kuwa na dubban nairori bata jin kyashin saya masa ko na nawa ne har ma wanda yafi karfin shekarun shi irnsu automatic motorbike da kekunan yara musamman take yo odar su daga Germany duk don Maigidannata. Inda shi kuma Daddy bashi da wani aboki kaman wannan Alameen Alameen Bello. In kaji shi yana bashi labari sai ka rantse da wani cikakken mai hankali ne yake magana ba da yaro dan shekaru biyu ba.
Faisal ya zauna ya kifa fuska cikin tafukan sa, yayinda Alameen ke dabdalarsa a dokin wuyansa. Antin ta karaso rike da tambulan cikke da sassanyar madarar shanu fresh ta mika masa. Ba tare da yayi musu ba ya amsa ya shanye wata niima da sanyi suka sauka a zuciyarsa. Jijiyoyin kansa duk sun mike rada-rada a kansa haka tsigar jikinshi sai tashi yake, tabbacin zazzabi ke neman kama shi.
Ba ta katse shi ba har saida ya samu nutsuwa don kansa, kana cikin sanyin murya ya ce,
“Aunty, kin ji abinda Daddy ya yanke a kaina?�
Ta ce, “Ya hanaka tafiyar ba? Ni ma ban ga dalilin tafiyar ba�
Ya ce, “Tafiya ni na fasa da kaina, cewa yayi in kawo matar aure cikin kwanaki goma ko ya aura min maman Alameen karami. Sabida Allah Anti yaya ma Daddy zai yi wannan bahagon tunanin? Sabida Allah an yi mun adalci kenan? Cikin mu wa aka taba zabawa matar aure? Yaya zaayi in iya hada rayuwa da matar da Alameen ya mutu ya bari ba don baya so ba, sai don mutuwa da tayi mishi yankan kauna? Wannan ai cin amana ne da tozartawa.
Wallahi ko yarinyar da Alameen ya furta ya na so, bazan iya aure ba balle matar sa. Komi son da nake mata kuwa zan iya jurewa. Don na tabbata in shine ya san ina son mace, da ko itace autar mata daga ranar bai kara sonta. Zai hakura ya bar mini domin shi dan uwa ne mai dimbin karimci da sadaukarwa.
Na zo ne in roke ki alafarma ki hana Daddy wannan kudurin nasa, ni kuma nayi alkawarin yin biyayya ga duk matar da ya zaba mini matsayin abokiyar rayuwata ta har abada, amma ni ba zan auri Ihsan ba.�
Ta yi murmuishi ta ce, “Na ji uzurinka Faisal, kuma da yardan Allah zanyi kokarin in ganar da shi. Amma da sharadin zaka amsa min wata tambaya guda daya da zan yi maka. Kayi min alkawarin zaka fada min gaskiya ni kuma na yi maka alkawarin ba zaka auri Ihsan ba!�
Cikin sauri ya ce, “Wace tambaya ce Anti? Wallahi zan amsa miki iyakar abinda na sani.�
Ta ce, “Shhhh, ka daina saurin rantsuwa akan abinda baka da tabbas.�
Ya ce, “Wallahi Anti zan gaya miki.�
Rantsuwar da yazo yana dana sanin yinta kamar yadda ta gargadeshi a farko.
Ta tattara hankalinta gabadaya gareshi cikin murryar manyantaka da bada umarni tace menene hakikanin abinda ke damunka, tsakaninka da mahaliccin ka?
Cikin juyayi da dana sanin alkawarinsa ya ce,
“Anti soyayyah ce ta ke azabtar dani. Shekaru dai-dai har goma sha daya. Amma alhamdulillahi a yanzu ta kusa karasani nima in bi dan uwana in huta da azabar ta.
To amma matsalata shine bana so tayi galaba a kaina, kamar yadda tayi galaba akan dan uwana.
So nake in nuna mata banbancin mu na cewa ni mai iya controlling zuciyata ne sabanin shi da zuciyar ke juya alamuransa.
Idan na barta ta yi galaba a kaina sauran yan uwana ma bazata kyalesu ba, haka zatayi ta bin mu daya bayan daya tana kashewa har sai ta karar damu. Don haka bazan barta tayi galaba a kai na ba.�
Murmushi tayi ta ce,
“Wace yarinya ce kake so shekarun da suka wuce, ba kuma zaka taba iya aure ba har ka bar mu domin ta?�
Cikin kaduwa da matsanancin mamaki ya ce, “Anti wa ya gaya miki wannan maganar?�
Ta ce, “Bai zama dole ka sani ba, ka yi alkawarin amsa min tambayata ne kawai amma ba kai ka dinga tambayata ba. Sabida haka ka ji tsoron Allah ka idasa cika alkawarin ka.�
Ya sunkuyar da kansa kasa, in banda zufa ba abinda ke ketowa daga koina a sassan jikin shi, duk kuwa da A/C da fanka da ke ta aiki a falon. Ya yi dana sanin saurin rantsuwar sa. Nauyi da kunyar idanunta duka sun masa mayafi. Muryar sa can kasan makoshin sa tamkar ba tashi ba, ya ce,
“Anti Inteesar din ki ce!�
Ba tare da alamun wani mamaki ko girgiza da furucinsa ba ta ce,
“To yanzun ka daina son nata ne?�
Ya girgiza kai har yanzu bai dago ba, ji yake har abada bazai iya kara hada idanu da ita ba, a sanyaye ya ce,
“Ya zaai na daina sonta? Ita din ce dai har yau bata bar ni na huta ba kuma har gobe ba zan taba iya auren ta ba!�
Ta ce, “Hujjah?�
Ya ce, “Hujjata a da shine kasancewar mu uba daya. Hujjata a yanzu kuwa Alameen ya so ta. Ni kuma bazan taba yin tarayya da shi a son komi ba ban hakura na bar mishi ba. Don na san da a ce ya san ina sonta, da tuni ya hakura ya bar mini.�
Saura kadan dariya ta kwace mata amma ta cije,
“Ta girgiza kai tana murmushi�
Ta ce, “Wannan ba hujja ba ce ba Faisal. Don haka tashi je ka. Cikin kwanaki goma ka yi tunanin abinda ya dace da kai. Ko dai samawa zuciyarka abinda ta dade tana so don dorewa rayuwa mai inganci ko kuma auren matar yayan ka.
Ina mai tabbatar maka har yau, har gobe Saratu na son ka. Soyayyarta da Alameen wata kaddara ce daga Allah amma kai kadai take so tun tana mitsitsiyar ta. Ta damu da kai sosai, zata iya yin komi a domin ka. Gareta duk yadda rayuwa ta zo, a karbeta. Don haka ne ta karbi soyayyar Alameen.�
Sau da dama tana yiwa komi na rayuwarta uzuri da Faisal da Daddy Makarfi. Ta baka wata daraja da muhimmanci a rayuwarta irin wanda bata baiwa kowa a duniya ba. Duk halin da kake ikrarin ka shiga a wancan lokacin, ina mai tabbatar ma itama ta shiga kwatankwacin sa koma fiye da naka. Ta damu da kai sosai. Ta na matukar kishinka fiye da yadda baka zato.
A duk halin da take ciki, na farin-ciki ne ko na bakin ciki kai take tunawa tace Allah Sarki Ya Faisal! Da yana nan da kaza-da kaza, da kaza bata faru ba, da kaza ta faru. Ta fi kowa bakin ciki da tafiyar ka ni nasan wannan, amma ita tsammani ta ke ban gane ba.
Ya girgiza kai har yanzu kan shi a sadde, ya ce,
“Anti wannan kauna ce ba soyayyah ba. Intisar kauna ta kawai take, amma bata so na!�
Ta ce, “Babban jigon soyayya shine kauna. Kai ba namiji bane? Baka san yadda zaka yi ka gina soyayyar ka a zuciyar matar da kake so ba? Sai ka zuba ido ka zama dan kallo kana muku-muku cikin daki? To zauna nan kallon ruwa har sai kwado yayi maka kafa.
Ina mai tabbatar maka Intisar ta shigo wani matakin da take tsananin bukatar soyayyar da namiji a yanzu, komai na iya faruwa da rayuwar ta balle a inda su ke da babu kowa a tare da su sai Allah da ya halicce su. Bar ganin ta yarinya mai kamun kai, da yawan yaya mata basa iya tsallake wannan stage din (adolcence). A jiya da na lissafa jibi ne zata cika shekaru ashirin da haihuwa. Faisal me kaka jira da rayuwar ka? Ina ganin lokaci yayi da ya kamata ku fuskanci alkibla sahihiya.�
Kwana yayi yana nazarin zantuttukan da suka yi da Anti a daren jiya. Sai dai har zuwa lokacin ya kasa tsayarwa da kansa wata sahihiyar shawara. Ya kasa daina ganin Saratu a matsayin mai dimbin laifi a gare shi. Laifin da yake jin har abada ba zai iya yafe mata ba!
Hakan nan zuciyar ta ki bada goyon baya, ta ki daina bugawa a kowanne second da so da kaunar Inteesar, shi kam ya rasa inda zai tsoma rayuwarshi ya ji sanyi.
Ya kasa zabarwa kansa komi cikin zabin da aka bashi. Abinda yake da tabbaci kawai shine ko zai mutu ba aure, ba zai auri matar Alameen ba, kamar yanda ba zai iya auren yarinyar da Alameen ya furta yana so ba kome zaayi da shi kuwa, balle Intisar din da har abada ba zai daina ganinta a matsayin azzaluma ba a cikin soyayya, mayaudariya mai son kanta da yawa kuma maciyiya amanar kauna.
Laifuffukan ta gareshi basu da iyaka kuma tananinsu ma bata lokaci ne. Ya dai barta da duniya da abinda ke cikin ta kadai sun isa su koya mata hankali.
How much do you like this story?
5/16/22, 07:35 - Ummi Tandama😇: ______________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book four
*@Takori*
Page7ï¸âƒ£
Ranar litinin Ihsan ta tashi zuwa Miami inda zata halarci kwas na tsawon shekaru uku madadin karatun ta, yaronta Alameen karami ta bar shi ne karkashin kulawar kakanninsa. Duk wasu shirye shiryen tafiyar Ihsan Dr. Rehab ne yayi mata Allah kadai ya san kudurin shi na alkhairi kan wannan mace mai kyakkyawar zuciya ta marigayin amininshi.
Zaman lafiya da a ke a gidan Makarfi tsakanin Hajiya Nafi da Anti Saratu abin sai ya burge ka, ya kuma baka mamaki tamkar ba wani sabani da ya taba shiga tsakanin su. Lallai duniya makaranta, ta koyar da Hajiya Nafi darussan rayuwa kala daban-daban. Hakannan harkokin kasuwancin ta daya fara durkushewa sabida rashin kwanciyar hankali a yanzun ya fara farfadowa. Yayinda Aunty Saratu ta a je aiki kwata-kwata ta rungumi auren ta da hannu bibbiyu, da fatan cikawa da imani kadai.
Ambasada Bashir Sambo, sun dawo gida bayan ritayar sa a embassy. Katafaren gidan da ya kwashe shekaru biyar yana ginawa yana nan cikin anguwan Lamido Crescent dake cikin birnin Kano. Gida ne na gani a bada labari da duk fadin anguwar babu wanda ya kama kafar sa, tamkar an dauko shi ne kacokam daga kasar France an aza a filin wajen.
Faisal ya zauna ya kifa fuska cikin tafukan sa, yayinda Alameen ke dabdalarsa a dokin wuyansa. Antin ta karaso rike da tambulan cikke da sassanyar madarar shanu fresh ta mika masa. Ba tare da yayi musu ba ya amsa ya shanye wata niima da sanyi suka sauka a zuciyarsa. Jijiyoyin kansa duk sun mike rada-rada a kansa haka tsigar jikinshi sai tashi yake, tabbacin zazzabi ke neman kama shi.
Ba ta katse shi ba har saida ya samu nutsuwa don kansa, kana cikin sanyin murya ya ce,
“Aunty, kin ji abinda Daddy ya yanke a kaina?�
Ta ce, “Ya hanaka tafiyar ba? Ni ma ban ga dalilin tafiyar ba�
Ya ce, “Tafiya ni na fasa da kaina, cewa yayi in kawo matar aure cikin kwanaki goma ko ya aura min maman Alameen karami. Sabida Allah Anti yaya ma Daddy zai yi wannan bahagon tunanin? Sabida Allah an yi mun adalci kenan? Cikin mu wa aka taba zabawa matar aure? Yaya zaayi in iya hada rayuwa da matar da Alameen ya mutu ya bari ba don baya so ba, sai don mutuwa da tayi mishi yankan kauna? Wannan ai cin amana ne da tozartawa.
Wallahi ko yarinyar da Alameen ya furta ya na so, bazan iya aure ba balle matar sa. Komi son da nake mata kuwa zan iya jurewa. Don na tabbata in shine ya san ina son mace, da ko itace autar mata daga ranar bai kara sonta. Zai hakura ya bar mini domin shi dan uwa ne mai dimbin karimci da sadaukarwa.
Na zo ne in roke ki alafarma ki hana Daddy wannan kudurin nasa, ni kuma nayi alkawarin yin biyayya ga duk matar da ya zaba mini matsayin abokiyar rayuwata ta har abada, amma ni ba zan auri Ihsan ba.�
Ta yi murmuishi ta ce, “Na ji uzurinka Faisal, kuma da yardan Allah zanyi kokarin in ganar da shi. Amma da sharadin zaka amsa min wata tambaya guda daya da zan yi maka. Kayi min alkawarin zaka fada min gaskiya ni kuma na yi maka alkawarin ba zaka auri Ihsan ba!�
Cikin sauri ya ce, “Wace tambaya ce Anti? Wallahi zan amsa miki iyakar abinda na sani.�
Ta ce, “Shhhh, ka daina saurin rantsuwa akan abinda baka da tabbas.�
Ya ce, “Wallahi Anti zan gaya miki.�
Rantsuwar da yazo yana dana sanin yinta kamar yadda ta gargadeshi a farko.
Ta tattara hankalinta gabadaya gareshi cikin murryar manyantaka da bada umarni tace menene hakikanin abinda ke damunka, tsakaninka da mahaliccin ka?
Cikin juyayi da dana sanin alkawarinsa ya ce,
“Anti soyayyah ce ta ke azabtar dani. Shekaru dai-dai har goma sha daya. Amma alhamdulillahi a yanzu ta kusa karasani nima in bi dan uwana in huta da azabar ta.
To amma matsalata shine bana so tayi galaba a kaina, kamar yadda tayi galaba akan dan uwana.
So nake in nuna mata banbancin mu na cewa ni mai iya controlling zuciyata ne sabanin shi da zuciyar ke juya alamuransa.
Idan na barta ta yi galaba a kaina sauran yan uwana ma bazata kyalesu ba, haka zatayi ta bin mu daya bayan daya tana kashewa har sai ta karar damu. Don haka bazan barta tayi galaba a kai na ba.�
Murmushi tayi ta ce,
“Wace yarinya ce kake so shekarun da suka wuce, ba kuma zaka taba iya aure ba har ka bar mu domin ta?�
Cikin kaduwa da matsanancin mamaki ya ce, “Anti wa ya gaya miki wannan maganar?�
Ta ce, “Bai zama dole ka sani ba, ka yi alkawarin amsa min tambayata ne kawai amma ba kai ka dinga tambayata ba. Sabida haka ka ji tsoron Allah ka idasa cika alkawarin ka.�
Ya sunkuyar da kansa kasa, in banda zufa ba abinda ke ketowa daga koina a sassan jikin shi, duk kuwa da A/C da fanka da ke ta aiki a falon. Ya yi dana sanin saurin rantsuwar sa. Nauyi da kunyar idanunta duka sun masa mayafi. Muryar sa can kasan makoshin sa tamkar ba tashi ba, ya ce,
“Anti Inteesar din ki ce!�
Ba tare da alamun wani mamaki ko girgiza da furucinsa ba ta ce,
“To yanzun ka daina son nata ne?�
Ya girgiza kai har yanzu bai dago ba, ji yake har abada bazai iya kara hada idanu da ita ba, a sanyaye ya ce,
“Ya zaai na daina sonta? Ita din ce dai har yau bata bar ni na huta ba kuma har gobe ba zan taba iya auren ta ba!�
Ta ce, “Hujjah?�
Ya ce, “Hujjata a da shine kasancewar mu uba daya. Hujjata a yanzu kuwa Alameen ya so ta. Ni kuma bazan taba yin tarayya da shi a son komi ba ban hakura na bar mishi ba. Don na san da a ce ya san ina sonta, da tuni ya hakura ya bar mini.�
Saura kadan dariya ta kwace mata amma ta cije,
“Ta girgiza kai tana murmushi�
Ta ce, “Wannan ba hujja ba ce ba Faisal. Don haka tashi je ka. Cikin kwanaki goma ka yi tunanin abinda ya dace da kai. Ko dai samawa zuciyarka abinda ta dade tana so don dorewa rayuwa mai inganci ko kuma auren matar yayan ka.
Ina mai tabbatar maka har yau, har gobe Saratu na son ka. Soyayyarta da Alameen wata kaddara ce daga Allah amma kai kadai take so tun tana mitsitsiyar ta. Ta damu da kai sosai, zata iya yin komi a domin ka. Gareta duk yadda rayuwa ta zo, a karbeta. Don haka ne ta karbi soyayyar Alameen.�
Sau da dama tana yiwa komi na rayuwarta uzuri da Faisal da Daddy Makarfi. Ta baka wata daraja da muhimmanci a rayuwarta irin wanda bata baiwa kowa a duniya ba. Duk halin da kake ikrarin ka shiga a wancan lokacin, ina mai tabbatar ma itama ta shiga kwatankwacin sa koma fiye da naka. Ta damu da kai sosai. Ta na matukar kishinka fiye da yadda baka zato.
A duk halin da take ciki, na farin-ciki ne ko na bakin ciki kai take tunawa tace Allah Sarki Ya Faisal! Da yana nan da kaza-da kaza, da kaza bata faru ba, da kaza ta faru. Ta fi kowa bakin ciki da tafiyar ka ni nasan wannan, amma ita tsammani ta ke ban gane ba.
Ya girgiza kai har yanzu kan shi a sadde, ya ce,
“Anti wannan kauna ce ba soyayyah ba. Intisar kauna ta kawai take, amma bata so na!�
Ta ce, “Babban jigon soyayya shine kauna. Kai ba namiji bane? Baka san yadda zaka yi ka gina soyayyar ka a zuciyar matar da kake so ba? Sai ka zuba ido ka zama dan kallo kana muku-muku cikin daki? To zauna nan kallon ruwa har sai kwado yayi maka kafa.
Ina mai tabbatar maka Intisar ta shigo wani matakin da take tsananin bukatar soyayyar da namiji a yanzu, komai na iya faruwa da rayuwar ta balle a inda su ke da babu kowa a tare da su sai Allah da ya halicce su. Bar ganin ta yarinya mai kamun kai, da yawan yaya mata basa iya tsallake wannan stage din (adolcence). A jiya da na lissafa jibi ne zata cika shekaru ashirin da haihuwa. Faisal me kaka jira da rayuwar ka? Ina ganin lokaci yayi da ya kamata ku fuskanci alkibla sahihiya.�
Kwana yayi yana nazarin zantuttukan da suka yi da Anti a daren jiya. Sai dai har zuwa lokacin ya kasa tsayarwa da kansa wata sahihiyar shawara. Ya kasa daina ganin Saratu a matsayin mai dimbin laifi a gare shi. Laifin da yake jin har abada ba zai iya yafe mata ba!
Hakan nan zuciyar ta ki bada goyon baya, ta ki daina bugawa a kowanne second da so da kaunar Inteesar, shi kam ya rasa inda zai tsoma rayuwarshi ya ji sanyi.
Ya kasa zabarwa kansa komi cikin zabin da aka bashi. Abinda yake da tabbaci kawai shine ko zai mutu ba aure, ba zai auri matar Alameen ba, kamar yanda ba zai iya auren yarinyar da Alameen ya furta yana so ba kome zaayi da shi kuwa, balle Intisar din da har abada ba zai daina ganinta a matsayin azzaluma ba a cikin soyayya, mayaudariya mai son kanta da yawa kuma maciyiya amanar kauna.
Laifuffukan ta gareshi basu da iyaka kuma tananinsu ma bata lokaci ne. Ya dai barta da duniya da abinda ke cikin ta kadai sun isa su koya mata hankali.
How much do you like this story?
5/16/22, 07:35 - Ummi Tandama😇: ______________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book four
*@Takori*
Page7ï¸âƒ£
Ranar litinin Ihsan ta tashi zuwa Miami inda zata halarci kwas na tsawon shekaru uku madadin karatun ta, yaronta Alameen karami ta bar shi ne karkashin kulawar kakanninsa. Duk wasu shirye shiryen tafiyar Ihsan Dr. Rehab ne yayi mata Allah kadai ya san kudurin shi na alkhairi kan wannan mace mai kyakkyawar zuciya ta marigayin amininshi.
Zaman lafiya da a ke a gidan Makarfi tsakanin Hajiya Nafi da Anti Saratu abin sai ya burge ka, ya kuma baka mamaki tamkar ba wani sabani da ya taba shiga tsakanin su. Lallai duniya makaranta, ta koyar da Hajiya Nafi darussan rayuwa kala daban-daban. Hakannan harkokin kasuwancin ta daya fara durkushewa sabida rashin kwanciyar hankali a yanzun ya fara farfadowa. Yayinda Aunty Saratu ta a je aiki kwata-kwata ta rungumi auren ta da hannu bibbiyu, da fatan cikawa da imani kadai.
Ambasada Bashir Sambo, sun dawo gida bayan ritayar sa a embassy. Katafaren gidan da ya kwashe shekaru biyar yana ginawa yana nan cikin anguwan Lamido Crescent dake cikin birnin Kano. Gida ne na gani a bada labari da duk fadin anguwar babu wanda ya kama kafar sa, tamkar an dauko shi ne kacokam daga kasar France an aza a filin wajen.