Sashe 75
Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kalaman sa masu dadi da sanyaya zuciya na dawo mata tar-tar a sharp kwakwalwar ta, haka hoton kyakkyawar fuskarsa garai-garai a idanunta. Ta san idan ta ce ma ta yi barci a wannan daren, to karya ne. Ta kuma yaudari kanta.
5/14/22, 09:27 - Ummi Tandama😇: ______________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book four
*@Takori*
Page5ï¸âƒ£
Bayan Watanni Biyu
Dr. Rehab Mohammed, aboki nagari kuma amini na kwarai ga marigayi Dr. Alameen Bello, ya iso kasar Nigeria a safiyar wata litinin, tuni dama Daddyn ya san da zuwansa, don haka ya tura Yasir ya taho dashi da ga air-port.
Ya samu Daddyn a ofis ne inda suka kara yiwa juna taaziyya. Ya shiga fidda takardu da file-file yana yiwa Daddyn bayanin su dalla-dalla, kama daga takardun gidan marigayin da ke Miami da wani fili daya saya ya fara gini a Florida, shares din shi (hannun jari) na bankuna, takardun asibitin shi Meritime na kwakwalwa da suke kokarin rufewa, zuwa takardu na kananan kadarori kamar bungalows guda biyu daya saya a Vienna, da dakin shan magani cikin meritime da wasu kudade da yake bin Baptist Health Care dake Miami.
Akwai kuma kudi na musamman da suka tasamma naira miliyon goma da su abokanen aikinsa suka bawa iyalinshi sadakah, ba don komi ba sai don dinbin alherinshi da taimakon da yayi masu a rayuwar shi tare da su wanda a cewar su har abada bazasu manta ba.
Daddy ya amsa ya yi mishi godiya mai tarin yawa, yace amma kafin ya tafi, ya jira ya yi shawara da matar shi tunda mahaifiyar shi bata da lafiya.
An zauna da Ihsan a ranar wadda kanta ke sunkuye cikin abaya. Daddy ya shaida mata abinda kenan ya kuma danka mata komi na Alameen ya ce ya bar mata duniya da lahira ita da abinda zata Haifa, illa kason mahaifiyar shi da za a cire. Ihsan na hawaye tace ta amsa, amma itama ta barwa abinda zata haifan, bata son komi na Alameen domin bata taba tunanin ta ci gadon Alameen ba.
Burin ta har kullum shine shi ya bizne ta. Don haka in an cire na Hajiyar Daddy ya cigaba da kulawa da jikarsa ko jikansa dukiyarshi a hannunshi. Alfarma daya take nema su yi mata shine Rehab yayi kokarin maido Meritime cikin Nigeria kamar yadda Alameen ya dade da wannan burin kuma har ya mutu da burin a zuciyar shi.
Tace ya riga ya nemi iznin assasa asibitin daga federal ministry of health tun dawowar su, takardun komi suna nan a gidan su, tuni ginin yayi nisa, haka ko bayan rasuwar shi maaikatan basu daina ba, domin ya riga ya biya su kudin su. Tana so Rehab ya taimaka mata ya cigaba da jagorantar asibitin koda yana can Miami ne. Akwai karatu da zata karo na tsawon shekaru ukku kacal idan ta dawo zata cigaba da jagorantar Asibitin kamar yadda Alameen ke son yayi Allah bai bashi iko ba.
Abinda zata haifa tana da burin in mace ne ko namiji? To zai yi karatu irin na Baban sa, ya jagoraci Meritime, tana fatan ko bayan ran ta Daddy ya taimaka mata wajen cikar barin ta, wanda Alameen ya dade da yiwa rayuwar sa amma rayuwar tayi mishi gaggawa.
Rehab ya daga ido ta cikin farin mudubin idon sa ya dubeta. Yayi mamakin yadda cikin bakar fata aka samu irin wannan soyayya ta tsakani da Allah tsakanin mace da mijinta tamkar a kasar haihuwarshi (India). A da, ya dauki matan bakar fata a matsayin masu kwadayi da son abin duniya kadai; basu san mecece soyayya ta gaskiya ba. Amma a yau Ihsan Abubakar, ta shayar da shi mamaki.
Ba shakka rayuwa ta kada Ihsan ta shigar da ita taitayin ta, ta yarda ita din ba komi bace face kyal-kyal banza, da zaka tafi ka barta ka shirya ko baka shirya ba. Ta zama mai tsoron Allah da gudun duniya abinda Alameen ya dade yana nusar da ita bata gane ba sai da ta faru a kanta.
A karshen satin Faisal ya iso daga Lagos, sanye yake da kufta da wando na bakar lallausar shadda getzner. To tabbattaccen kamshinsa na (5,000 Doller) kadai daya gauraye ilahirin gidan ya sanar da mutanen gidan isowarsa as usual. Ya saya kwayar idanuwan shi cikin bakin dark glasses ta yadda baka iya ganin halin da kwayar idon shi ke ciki.
Babu shakka mutuwar dan uwansa ta dokeshi inda duk ya dauki laifin ya daura akan baiwar Allah da bata ji-ba-bata gani ba, itama ta kanta ta ke Intisar.
Inda abinda ya tsana da gani a rayuwarshi a yau to Saratu Intisar ce. Yana ganin ta as a wicked lover kuma har abada baya jin zai yafe mata.
Baya ga tagayyara tashi zuciyar tare da daidaita farin cikinsa, ba kuma tare data kara waiwayar shi a rayuwarta ba don sanin shi din a mace yake ko a raye? Ta koma ga zuciyar dan uwan sa, ta illata ta gabadaya da ciwon da har abada bazai warke ba. Duk hakan bai ishe ta ba, sai da ta yi sandaiyyar danganar shi da karkashin kasa, inda baa dawowa.
A yanzu kam ya na mai tantama da alamarin ta, tare da furucin da nahaifiyar su ta dade ta nayi a kanta na cewa, shin ko ita din, mayya ce?
Ya samu Daddy zaune bisa kujera yana nazarin labarun da ake watsowa daga tashar CNN a akwatin talbijin din jikin bango (plasma) dake falon. Yar lelen na gefe rike da karamin Alkurani izfi sittin bugun Misra tana karantawa. Kallo daya ya yi mata ya kawar da kanshi haka itama, da ganin mugun ramar da kowannen su yayi. Zuciyar ta ne ya bata wani irin bugu, don sai ya zamo mata Alameen sak a ranar bankwanar su illa shi din yafi Alameen haske da kauri kadan.
Tamkar bai taba sanin ta ba, bashi kuma da masaniyar kasancewar ta a wajen ya doshi Daddy suka gaisa, suka shiga hira ta abinda ya shafe su. Cikin karfin hali ta juyo tace ina wuni Ya Faisal? Da sauri ya amsa sabida dukan da zazzakar muryarta ta yiwa zuciyarsa, ba tare daya dubeta ba ya ce lafiya, yaya gida? Da haka ya maida hankalin shi kan zancen da suke da Daddy cewa ranar litinin zai tafi da Hajiya asibtin Meritime da ke Miami domin har zuwa lokacin babu wani cigaba akan alamarinta a asibitin kwakwalwa na Kaduna.
A lokacin Daddy ya ji matukar kunyar dan nasa kan biris din da yayi da alamarin mahaifiyarsu, ko ya ta ke bai taba tambayar wani a cikinsu ba. Ya sadda kai ya ce
kun yi maganar da Dr. Rehab ne? Ya ce Eh, shi da kansa mun je ya ganta, shi ya kawo shawarar mu tafi da ita can din in Allah ya yarda zasu yi iyaka kokarinsu. Daddy ya ce Allah ya taimaka, in akwai wani matsala sai kayi gaggawar sanar dani, ya ce babu wata matsala don shi Rehab din ne ya dau nauyin komi daga aljihunsa. Ta tashi ta bar masu falon cike da tukuki da kunar da zuciyar ta ta shiga yi kan irin wulakancin da Ya Faisal ya tsiri yi mata ba tun yau ba.
A washegari takardun ta na karatu suka fito suka tadda Daddyn a ofis, sabida kyawun sakamakonta hade yake da gurbin karatu daga Jamioi har ukku sai wanda ta zaba. Jamiar (Ummul-Kura) da ke Madinah sun bata gurbi a fanning pure and applied chemistry yayin da (King Abdul-Aziz University) da ke Riyadh suka bata biochemistry inda (Al-Azhar) da ke Egypt suka bata (doctorate) gurbi a medicine and surgery. Duka cikin ukun nan babu na yarwa babu kuma wanda ba raayin ta ba. Don haka da Daddyn ya bata zabi tace ta bar mishi wuka da nama ya zaba mata wanda duk ya ga ya dace da ita.
Ranar da Faisal ya daga da mahaifiyarsa kasar Amurka nema mata maganin tabin kwakwalwa data samu. Ranar ne itama ta daga Egypt tare da Najib da Hidayah da Daddyn ya wakilta suyi mata rakiya, bayan sun kammala duk wani shige da fice da ya kamata aka bata lokacin da zata fara shiga aji, wato daya ga watan Junairu na sabuwar shekara mai kamawa, kimanin watanni biyu kenan kamin lokacin.
Sun hadu da Hunainah a can wadda tuni ta zama yar gari, don haka ita ta nuna musu garin suka ci shi. Najib da Hidayah kam wani sabon honey moon din aka bude. Yayinda ita kuma ke tare da Hunainah kodayaushe, tana koka mata rayuwar ta da ta ishe ta, komi bakikkirin take ganinsa, bata jin dadin komi.
Ta gaya mata ita ta yanke rai da samun farin-ciki a rayuwarta, komi da ta ke yi tana yi ne cikin karfin hali da inganta Imani. Babban abin da ya dameta ya kuma kara dagula lissafinta da jin dadin ta shine gabar da Faisal ya daura da ita, ita ba yarinya ba ce, ta tabbata Faisal ya daura alhakin mutuwar dan uwansa da baya da kamar shi a duniya ne a wuyan ta. Ta ce cikin karyayyar zuciya da radadin zuci mara misaltuwa.
“Hunainah a da na so Faisal, na so shi a cikin rashin sanin shi din ko me nene a gareni. Hakannan dai nike son shi sabida shi mai kyautayi ne da tausayi, kuma gwani wajen nuna kulawa da nuna kauna a gareni.
To kin san zuciya an halicce ta ne a bisa kaunar mai kyautatawa a gareta, to hakan ne ya faru da ni a lokacin. Na so shi a sailin da ban san ma menene son ba, son shi nake, amma ban san son shin na ke ba, kawai na san ni mai tsananin kishi ce a kanshi ta yadda bana son ko da wasa in ji ko in ga wata mace ta rabe shi.
Babu ranar da ta fiye min tashin hankali tamkar ranar da ya ke yi mun hirar budurwar sa Ronke Adeyemi. A ranar na tabbatarwa kaina ina son Faisal, so na soyayya a matsayin yana yayana da muke uba daya?
5/14/22, 09:27 - Ummi Tandama😇: ______________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book four
*@Takori*
Page5ï¸âƒ£
Bayan Watanni Biyu
Dr. Rehab Mohammed, aboki nagari kuma amini na kwarai ga marigayi Dr. Alameen Bello, ya iso kasar Nigeria a safiyar wata litinin, tuni dama Daddyn ya san da zuwansa, don haka ya tura Yasir ya taho dashi da ga air-port.
Ya samu Daddyn a ofis ne inda suka kara yiwa juna taaziyya. Ya shiga fidda takardu da file-file yana yiwa Daddyn bayanin su dalla-dalla, kama daga takardun gidan marigayin da ke Miami da wani fili daya saya ya fara gini a Florida, shares din shi (hannun jari) na bankuna, takardun asibitin shi Meritime na kwakwalwa da suke kokarin rufewa, zuwa takardu na kananan kadarori kamar bungalows guda biyu daya saya a Vienna, da dakin shan magani cikin meritime da wasu kudade da yake bin Baptist Health Care dake Miami.
Akwai kuma kudi na musamman da suka tasamma naira miliyon goma da su abokanen aikinsa suka bawa iyalinshi sadakah, ba don komi ba sai don dinbin alherinshi da taimakon da yayi masu a rayuwar shi tare da su wanda a cewar su har abada bazasu manta ba.
Daddy ya amsa ya yi mishi godiya mai tarin yawa, yace amma kafin ya tafi, ya jira ya yi shawara da matar shi tunda mahaifiyar shi bata da lafiya.
An zauna da Ihsan a ranar wadda kanta ke sunkuye cikin abaya. Daddy ya shaida mata abinda kenan ya kuma danka mata komi na Alameen ya ce ya bar mata duniya da lahira ita da abinda zata Haifa, illa kason mahaifiyar shi da za a cire. Ihsan na hawaye tace ta amsa, amma itama ta barwa abinda zata haifan, bata son komi na Alameen domin bata taba tunanin ta ci gadon Alameen ba.
Burin ta har kullum shine shi ya bizne ta. Don haka in an cire na Hajiyar Daddy ya cigaba da kulawa da jikarsa ko jikansa dukiyarshi a hannunshi. Alfarma daya take nema su yi mata shine Rehab yayi kokarin maido Meritime cikin Nigeria kamar yadda Alameen ya dade da wannan burin kuma har ya mutu da burin a zuciyar shi.
Tace ya riga ya nemi iznin assasa asibitin daga federal ministry of health tun dawowar su, takardun komi suna nan a gidan su, tuni ginin yayi nisa, haka ko bayan rasuwar shi maaikatan basu daina ba, domin ya riga ya biya su kudin su. Tana so Rehab ya taimaka mata ya cigaba da jagorantar asibitin koda yana can Miami ne. Akwai karatu da zata karo na tsawon shekaru ukku kacal idan ta dawo zata cigaba da jagorantar Asibitin kamar yadda Alameen ke son yayi Allah bai bashi iko ba.
Abinda zata haifa tana da burin in mace ne ko namiji? To zai yi karatu irin na Baban sa, ya jagoraci Meritime, tana fatan ko bayan ran ta Daddy ya taimaka mata wajen cikar barin ta, wanda Alameen ya dade da yiwa rayuwar sa amma rayuwar tayi mishi gaggawa.
Rehab ya daga ido ta cikin farin mudubin idon sa ya dubeta. Yayi mamakin yadda cikin bakar fata aka samu irin wannan soyayya ta tsakani da Allah tsakanin mace da mijinta tamkar a kasar haihuwarshi (India). A da, ya dauki matan bakar fata a matsayin masu kwadayi da son abin duniya kadai; basu san mecece soyayya ta gaskiya ba. Amma a yau Ihsan Abubakar, ta shayar da shi mamaki.
Ba shakka rayuwa ta kada Ihsan ta shigar da ita taitayin ta, ta yarda ita din ba komi bace face kyal-kyal banza, da zaka tafi ka barta ka shirya ko baka shirya ba. Ta zama mai tsoron Allah da gudun duniya abinda Alameen ya dade yana nusar da ita bata gane ba sai da ta faru a kanta.
A karshen satin Faisal ya iso daga Lagos, sanye yake da kufta da wando na bakar lallausar shadda getzner. To tabbattaccen kamshinsa na (5,000 Doller) kadai daya gauraye ilahirin gidan ya sanar da mutanen gidan isowarsa as usual. Ya saya kwayar idanuwan shi cikin bakin dark glasses ta yadda baka iya ganin halin da kwayar idon shi ke ciki.
Babu shakka mutuwar dan uwansa ta dokeshi inda duk ya dauki laifin ya daura akan baiwar Allah da bata ji-ba-bata gani ba, itama ta kanta ta ke Intisar.
Inda abinda ya tsana da gani a rayuwarshi a yau to Saratu Intisar ce. Yana ganin ta as a wicked lover kuma har abada baya jin zai yafe mata.
Baya ga tagayyara tashi zuciyar tare da daidaita farin cikinsa, ba kuma tare data kara waiwayar shi a rayuwarta ba don sanin shi din a mace yake ko a raye? Ta koma ga zuciyar dan uwan sa, ta illata ta gabadaya da ciwon da har abada bazai warke ba. Duk hakan bai ishe ta ba, sai da ta yi sandaiyyar danganar shi da karkashin kasa, inda baa dawowa.
A yanzu kam ya na mai tantama da alamarin ta, tare da furucin da nahaifiyar su ta dade ta nayi a kanta na cewa, shin ko ita din, mayya ce?
Ya samu Daddy zaune bisa kujera yana nazarin labarun da ake watsowa daga tashar CNN a akwatin talbijin din jikin bango (plasma) dake falon. Yar lelen na gefe rike da karamin Alkurani izfi sittin bugun Misra tana karantawa. Kallo daya ya yi mata ya kawar da kanshi haka itama, da ganin mugun ramar da kowannen su yayi. Zuciyar ta ne ya bata wani irin bugu, don sai ya zamo mata Alameen sak a ranar bankwanar su illa shi din yafi Alameen haske da kauri kadan.
Tamkar bai taba sanin ta ba, bashi kuma da masaniyar kasancewar ta a wajen ya doshi Daddy suka gaisa, suka shiga hira ta abinda ya shafe su. Cikin karfin hali ta juyo tace ina wuni Ya Faisal? Da sauri ya amsa sabida dukan da zazzakar muryarta ta yiwa zuciyarsa, ba tare daya dubeta ba ya ce lafiya, yaya gida? Da haka ya maida hankalin shi kan zancen da suke da Daddy cewa ranar litinin zai tafi da Hajiya asibtin Meritime da ke Miami domin har zuwa lokacin babu wani cigaba akan alamarinta a asibitin kwakwalwa na Kaduna.
A lokacin Daddy ya ji matukar kunyar dan nasa kan biris din da yayi da alamarin mahaifiyarsu, ko ya ta ke bai taba tambayar wani a cikinsu ba. Ya sadda kai ya ce
kun yi maganar da Dr. Rehab ne? Ya ce Eh, shi da kansa mun je ya ganta, shi ya kawo shawarar mu tafi da ita can din in Allah ya yarda zasu yi iyaka kokarinsu. Daddy ya ce Allah ya taimaka, in akwai wani matsala sai kayi gaggawar sanar dani, ya ce babu wata matsala don shi Rehab din ne ya dau nauyin komi daga aljihunsa. Ta tashi ta bar masu falon cike da tukuki da kunar da zuciyar ta ta shiga yi kan irin wulakancin da Ya Faisal ya tsiri yi mata ba tun yau ba.
A washegari takardun ta na karatu suka fito suka tadda Daddyn a ofis, sabida kyawun sakamakonta hade yake da gurbin karatu daga Jamioi har ukku sai wanda ta zaba. Jamiar (Ummul-Kura) da ke Madinah sun bata gurbi a fanning pure and applied chemistry yayin da (King Abdul-Aziz University) da ke Riyadh suka bata biochemistry inda (Al-Azhar) da ke Egypt suka bata (doctorate) gurbi a medicine and surgery. Duka cikin ukun nan babu na yarwa babu kuma wanda ba raayin ta ba. Don haka da Daddyn ya bata zabi tace ta bar mishi wuka da nama ya zaba mata wanda duk ya ga ya dace da ita.
Ranar da Faisal ya daga da mahaifiyarsa kasar Amurka nema mata maganin tabin kwakwalwa data samu. Ranar ne itama ta daga Egypt tare da Najib da Hidayah da Daddyn ya wakilta suyi mata rakiya, bayan sun kammala duk wani shige da fice da ya kamata aka bata lokacin da zata fara shiga aji, wato daya ga watan Junairu na sabuwar shekara mai kamawa, kimanin watanni biyu kenan kamin lokacin.
Sun hadu da Hunainah a can wadda tuni ta zama yar gari, don haka ita ta nuna musu garin suka ci shi. Najib da Hidayah kam wani sabon honey moon din aka bude. Yayinda ita kuma ke tare da Hunainah kodayaushe, tana koka mata rayuwar ta da ta ishe ta, komi bakikkirin take ganinsa, bata jin dadin komi.
Ta gaya mata ita ta yanke rai da samun farin-ciki a rayuwarta, komi da ta ke yi tana yi ne cikin karfin hali da inganta Imani. Babban abin da ya dameta ya kuma kara dagula lissafinta da jin dadin ta shine gabar da Faisal ya daura da ita, ita ba yarinya ba ce, ta tabbata Faisal ya daura alhakin mutuwar dan uwansa da baya da kamar shi a duniya ne a wuyan ta. Ta ce cikin karyayyar zuciya da radadin zuci mara misaltuwa.
“Hunainah a da na so Faisal, na so shi a cikin rashin sanin shi din ko me nene a gareni. Hakannan dai nike son shi sabida shi mai kyautayi ne da tausayi, kuma gwani wajen nuna kulawa da nuna kauna a gareni.
To kin san zuciya an halicce ta ne a bisa kaunar mai kyautatawa a gareta, to hakan ne ya faru da ni a lokacin. Na so shi a sailin da ban san ma menene son ba, son shi nake, amma ban san son shin na ke ba, kawai na san ni mai tsananin kishi ce a kanshi ta yadda bana son ko da wasa in ji ko in ga wata mace ta rabe shi.
Babu ranar da ta fiye min tashin hankali tamkar ranar da ya ke yi mun hirar budurwar sa Ronke Adeyemi. A ranar na tabbatarwa kaina ina son Faisal, so na soyayya a matsayin yana yayana da muke uba daya?