Sashe 10
Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya shiga ba Hajiyar shi hakuri yana gaya mata matsalolin da ya kashe wadanda suka hana shi samun lokacin kansa, amma ta ki sauraron shi ya ce, ‘Ita ma Ihsan din ta sani saboda transfer din aiyukan su duka amma yanzu da ya karya kumallo (breakfast) can zai fara zuwa kafin ko’ina.
Ina! Hajiya ta ki ta ce yanzu-yanzun ya tashi ya tafi ya ci abincin a waje, har tankado keyarsa ta yi daga kofar dakinta, sai ya yi murmushi ya lalubi ‘yan mukullayen motarshi ya tabbatar suna nan cikin aljihun shi sai ya fita. Zuciyarsa cike fal da jin haushin rashin ganin kyakkyawar fuskar Halimar shi a safiyar.
Tafiya yake sannu-sannu bisa kyawawan titunan birnin Tarayya marasa tudu balle gargada. Dressing din da ya yi a yau ya burge kwarai, ga wani dan siririn farin gilashi da ya manna tamkar Ba’indiyen nan Bobby Doel, kira’ar (Khusairi) yake bi cike da nishadi, ya san yau zai gamu da fushin Ihsan din shi da ke ba shi dariya, don da an dan kissing din ta shi kenan ya kare, ko ko don tana son shi ne? Bai sani ba.
Yana bin adireshin da ke jikin katin bai sha wuyar gane gidan ba, tun daga gate ya tabbatar su Ihsan kam ana ji da naira. Maigadi ya yi mai iso Ihsan ta ba shi izini ya kai shi can babban falon saukar bakin babanta. Ta samu Ann tana waya ta ce, ‘Kin ji Al’ameen ko sai yau ya waiwaye ni?�
Ann din ta rufe wayar ta ta dauki malafarta ta kifa a ka, ta ce,
“Fara bashi abinci tukunna, don daga ji sammako ya doko kada ya ce muna tsiya.�
Ta yi dariya ta ce, “Kai Ann, ba ki da dama. Amma ai ko kofar gidan mu mutum ya kalla ya san ko jikokin-jikokinmu, su da tsiya sai da su ji ana labarinta.�
To amma ita kanta Ihsan ta san wannan ba halin Al’ameen din ta ne ba, rainawa mutane kura, ta dai fada ne kawai don ta ga Ann da alama ran ta ya baci da Al’ameen sosai. Ta koma kicin ta bawa yaron su Ike umarnin abinda zai kai masa matsayin karin kumallo (American breakfast) kamar yadda ya fi so a kullum. Daga nan toilet ta yi ta fesa wanka na musamman ta zuba fararen undies kafin ta daura wani masifaffen tattausan lesi cotton fari sol, mai adon kala-kalar duwarwatsu.
Wannan less da shi da babu duk daya don manyan hudojin da ke jikinsa sun wuce misali amma kudi na gugar wuri har naira dubu saba’in kudin mu na nan gida Nijeriya ta saye shi a London, ba don komai ba sai don Al’ameen mutum ne mai son farin abu, ya sha gaya mata in ba farar kwalliya ta yi ba, ba ta burge shi, kuma ya kan so ta don farin ta ba don kyan ta ba.
To wannan ne dalilin da yasa ta sanya shi, haka ko ‘yanmatan Al’ameen jar fata sun fi yawa don dai Allah ya so ta da shi ne kawai duk da yake ita din ma fara ce, amma fari ne na jin dadi ba na halitta ba. To wannan na daga dalilin da yasa ta fiye farar kwalliya don ta lura Aminu fa sai da lallami ake samun shi.
Tun can ba ta daura dankwali bare yau da kwalliyar ta musamman ce. Hakika ta azabtu da rashin ganinsa na ‘yan kwanakin nan, domin ba su taba kaiwa tsawon wannan lokacin ba sa tare ba, tun auren su, ko ofis tana like da kayan ta saboda nurses masu yi masa kallon da bai gamsar da ita ba. Ihsan kenan.
Takalmi flat fari sol dan Thailand ta zura kafafun ta dan dagwas, turare mai suna turare ita kan ta ba ta san kala nawa ta fesa ba, musamman collection na Calvin Klein da Dior, ta yadda har ba za ka tantance kamshin wane turare take ba, wannan duk yana daga cikin koyarwar Al’ameen Bello, domin shi mutum ne mai masifar son kamshi, baya jin kyashin saya masu turare ko na nawa ne.
Musamman zai je Paris don kurum ya sayo masu turare, wadannan na daga cikin dalilan da suka sa har kullum take son shi, take kuma kara kaunarsa a kowanne dakika, domin hakika shi din special ne, haka komai nasa na musamman din ne.
Tun haduwar su bata kara duban wani da namiji a duniya da sunan so ba, shi kadai take so, shi kadai take sha’awa, shi kadai ke burge ta, hakan nan shi kadai ne namijin da zai iya yi mata kowanne irin wulakanci ta shanye. Dr. Ihsan kenan.
Cikin takun kasaita ta wuce Ann ta ce,
“Ba za ki je ku gaisa ba Ann?�
Ann din ta dube ta sama zuwa kasa ta ga yadda ta wani hade kamr mai shirin zuwa dinar babbar aminiya, wani haushi ya kama ta don ita so take ta kashe auren kowa ya huta, don ba ta ga yaron da ya isa ya wulakanta gudan jinin ta ta kyale ba komai tashen nairarsa kuwa, kuma ko dan uban waye shi balle wani shirmen banza likitan kwakwalwa, amma ba ta son ta bata farin cikin Ihsan, don ta lura still tana son mijinta sai ta bi ta da siyasa.
Ta juyar da kai kawai ta ce,
“Ki je kawai ki ji wadda ya zo da ita, zan zo in raina ya yi sanyi, don har yanzu raina a bace yake. Kin kuma sanni ban iya boye bacin raina ba.�
Ta kadai kai ta fita fuskar nan ba annuri sam, ta shiga taka matattakalar da za ta sada ta da falon, kasancewar ainahin ginin falon bakin Dr. Argungu a kasan gidan yake tamkar ka shiga rijiya ne ka tadda sabuwar duniya. Ta sa kai ba ko sallama.
Aminun shima daman ya cika fam, da shanya shin da aka yi fiye da awa biyu kamar wani mai neman aiki a bankin su?
How much do you like this story?
5/7/22, 13:10 - Ummi Tandama😇: ___________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book one
*@Takori*
Page6ï¸âƒ£
Tsaye yake kikam, ya hade hannuwan shi a kirji yana kallon tangama-tangaman hotunan ta kamar ta fito ta yi magana da aka manna a kusurwa biyu na falon tabbacin ana ji da Ihsan kenan, kuma ita daya kenan a gidan tamfar rai ga iyayenta. Ko bude abubuwan da aka jera masa bai yi ba balle ya kai ga ci.
Ta samu kujera can nesa da shi ta harde, ta dauki remote control ta karo karfin A.C ko sannu da zuwa ba ta ce masa ba balle ci kan ka. Shi ne ya gaji da shirun ya bara, ya dubi agogon hannun shi Jovial ya ce,
“Saboda Allah Ihsan haka ake karbar baki ku a gidan ku?�
Ta sake tunzura ta ce, ‘Da aka yi me?�
Ya ce, “Kin san awanni biyu kenan kwarara, ina zaman jiran fitowar wani a cikin ku, amma shi ne sai yanzu ki ka ga damar fitowa?�
Ta yamutsa fuska ta ce a zafafe,
“Aminu, har kana da bakin gaya min haka? For God’s sake, yau kwanakin mu nawa a garin nan amma ka nuna wa iyayena ba ni da wata daraja a idon ka ba ka kuma damu da ni ba, shi ne kuma har za ka nemi gayan magana? Wai haka muke karbar baki, to ni ko iyayena da wa ka ke?� Ta tsatstsare shi da ido.
Al’ameen ya san ba shi da gaskiya, kuma ko a wurin Allah ne ba shi da ita. Dole ya sauke nashi temper n ya samu masangalin kujera ya rage tsawo, ya sanya hannu cikin aljihu ya zaro wayar shi da ke ta tsuwwa a cikin aljihun kaftanin shi, ya dade yana magana da aminin shi Rehab wato babban likitan Meritime yana gaya masa irin muhimman ayyukan da suka gabatar ne a kwanakin, ya ce ya yi kyau ya kuma yaba komai, ya gaya masa akwai motocin sa har yanzu suna port bai san ba a auno su ba, sai jiya ya je da kansa ya auno masa ta jirgin ruwa, amma ta Nijar za su biyo don ba jirgin kaya tun bayan da suka taso, don haka ya je ya fiddo su a Yamai. Suka yi sallama ya maida wayar shi aljihu.
Ya dubi Ihsan da sassanyan kallo ya ga ko kallon shi bata yi, ta maida fuskar ta can wani gefen daban bayan ta daure ta iya daurewa kamar bata san Allah ya yi ruwan tsirar shi ba ma, ransa ya sosu, amma sai ya yi murmushi ya ce,
“Ihsan kenan, dadi na da ke ba kya tsayawa ki ji uzurin mutum sai kawai ki kama fushi, amma ai ke ma dai kin san I missed you very-very much…�
Ya kira kalaman cikin tattausar muryar da ta kusa sa ta gyangyadi, amma da yake tana son ta nuna fushin nata sai ta cije ta kyabe baki a lokaci guda kuma tana girgiza kafa daya kan daya ita ala dole fushi take, duk sai ta ba shi dariya, ya mike har inda take ya mika mata hannuwan shi masu matukar taushi alamar ta tashi su yi sulhu, amman sai ta noke cikin jan aji irin nata, sai ya russuna ya kama hannayen ta duka biyun ya mikar da ita tsaye, suka fuskanci juna cikin ido, ita kallon haushi take masa shi kuma kallon I beg your pardon.
Ta ce, “Me ye haka?�
Amman can karkashin zuciyar ta hucewa take yi, tana kuma kara son mijinta a kowanne dakika, duk wata hanya da ya san zai bi ya wanke laifin shi a zuciyar ta ya san shi, duk da ta san kaunar da ita take masa ta rinjayi wadda yake mata, amma yana kokari a koyaushe ya nuna shi din mai son ta ne, mai gudun bacin ran ta ne.
Bare yanzun da ta yi kewarsa, fiye da yadda bakin ta zai iya fassarawa, sai ta bada kai bori ya hau. Sun dade cikin farantawa junansu tamkar suna gidan su koko bakin beaches na Miami, kafin su zauna su fuskanci juna, jikin ta a barin kafadun shi na dama, ta soma share hawaye da bayan hannu duk ya bi ya rikice ya ce,
“Me ye kuma?�
Ina! Hajiya ta ki ta ce yanzu-yanzun ya tashi ya tafi ya ci abincin a waje, har tankado keyarsa ta yi daga kofar dakinta, sai ya yi murmushi ya lalubi ‘yan mukullayen motarshi ya tabbatar suna nan cikin aljihun shi sai ya fita. Zuciyarsa cike fal da jin haushin rashin ganin kyakkyawar fuskar Halimar shi a safiyar.
Tafiya yake sannu-sannu bisa kyawawan titunan birnin Tarayya marasa tudu balle gargada. Dressing din da ya yi a yau ya burge kwarai, ga wani dan siririn farin gilashi da ya manna tamkar Ba’indiyen nan Bobby Doel, kira’ar (Khusairi) yake bi cike da nishadi, ya san yau zai gamu da fushin Ihsan din shi da ke ba shi dariya, don da an dan kissing din ta shi kenan ya kare, ko ko don tana son shi ne? Bai sani ba.
Yana bin adireshin da ke jikin katin bai sha wuyar gane gidan ba, tun daga gate ya tabbatar su Ihsan kam ana ji da naira. Maigadi ya yi mai iso Ihsan ta ba shi izini ya kai shi can babban falon saukar bakin babanta. Ta samu Ann tana waya ta ce, ‘Kin ji Al’ameen ko sai yau ya waiwaye ni?�
Ann din ta rufe wayar ta ta dauki malafarta ta kifa a ka, ta ce,
“Fara bashi abinci tukunna, don daga ji sammako ya doko kada ya ce muna tsiya.�
Ta yi dariya ta ce, “Kai Ann, ba ki da dama. Amma ai ko kofar gidan mu mutum ya kalla ya san ko jikokin-jikokinmu, su da tsiya sai da su ji ana labarinta.�
To amma ita kanta Ihsan ta san wannan ba halin Al’ameen din ta ne ba, rainawa mutane kura, ta dai fada ne kawai don ta ga Ann da alama ran ta ya baci da Al’ameen sosai. Ta koma kicin ta bawa yaron su Ike umarnin abinda zai kai masa matsayin karin kumallo (American breakfast) kamar yadda ya fi so a kullum. Daga nan toilet ta yi ta fesa wanka na musamman ta zuba fararen undies kafin ta daura wani masifaffen tattausan lesi cotton fari sol, mai adon kala-kalar duwarwatsu.
Wannan less da shi da babu duk daya don manyan hudojin da ke jikinsa sun wuce misali amma kudi na gugar wuri har naira dubu saba’in kudin mu na nan gida Nijeriya ta saye shi a London, ba don komai ba sai don Al’ameen mutum ne mai son farin abu, ya sha gaya mata in ba farar kwalliya ta yi ba, ba ta burge shi, kuma ya kan so ta don farin ta ba don kyan ta ba.
To wannan ne dalilin da yasa ta sanya shi, haka ko ‘yanmatan Al’ameen jar fata sun fi yawa don dai Allah ya so ta da shi ne kawai duk da yake ita din ma fara ce, amma fari ne na jin dadi ba na halitta ba. To wannan na daga dalilin da yasa ta fiye farar kwalliya don ta lura Aminu fa sai da lallami ake samun shi.
Tun can ba ta daura dankwali bare yau da kwalliyar ta musamman ce. Hakika ta azabtu da rashin ganinsa na ‘yan kwanakin nan, domin ba su taba kaiwa tsawon wannan lokacin ba sa tare ba, tun auren su, ko ofis tana like da kayan ta saboda nurses masu yi masa kallon da bai gamsar da ita ba. Ihsan kenan.
Takalmi flat fari sol dan Thailand ta zura kafafun ta dan dagwas, turare mai suna turare ita kan ta ba ta san kala nawa ta fesa ba, musamman collection na Calvin Klein da Dior, ta yadda har ba za ka tantance kamshin wane turare take ba, wannan duk yana daga cikin koyarwar Al’ameen Bello, domin shi mutum ne mai masifar son kamshi, baya jin kyashin saya masu turare ko na nawa ne.
Musamman zai je Paris don kurum ya sayo masu turare, wadannan na daga cikin dalilan da suka sa har kullum take son shi, take kuma kara kaunarsa a kowanne dakika, domin hakika shi din special ne, haka komai nasa na musamman din ne.
Tun haduwar su bata kara duban wani da namiji a duniya da sunan so ba, shi kadai take so, shi kadai take sha’awa, shi kadai ke burge ta, hakan nan shi kadai ne namijin da zai iya yi mata kowanne irin wulakanci ta shanye. Dr. Ihsan kenan.
Cikin takun kasaita ta wuce Ann ta ce,
“Ba za ki je ku gaisa ba Ann?�
Ann din ta dube ta sama zuwa kasa ta ga yadda ta wani hade kamr mai shirin zuwa dinar babbar aminiya, wani haushi ya kama ta don ita so take ta kashe auren kowa ya huta, don ba ta ga yaron da ya isa ya wulakanta gudan jinin ta ta kyale ba komai tashen nairarsa kuwa, kuma ko dan uban waye shi balle wani shirmen banza likitan kwakwalwa, amma ba ta son ta bata farin cikin Ihsan, don ta lura still tana son mijinta sai ta bi ta da siyasa.
Ta juyar da kai kawai ta ce,
“Ki je kawai ki ji wadda ya zo da ita, zan zo in raina ya yi sanyi, don har yanzu raina a bace yake. Kin kuma sanni ban iya boye bacin raina ba.�
Ta kadai kai ta fita fuskar nan ba annuri sam, ta shiga taka matattakalar da za ta sada ta da falon, kasancewar ainahin ginin falon bakin Dr. Argungu a kasan gidan yake tamkar ka shiga rijiya ne ka tadda sabuwar duniya. Ta sa kai ba ko sallama.
Aminun shima daman ya cika fam, da shanya shin da aka yi fiye da awa biyu kamar wani mai neman aiki a bankin su?
How much do you like this story?
5/7/22, 13:10 - Ummi Tandama😇: ___________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book one
*@Takori*
Page6ï¸âƒ£
Tsaye yake kikam, ya hade hannuwan shi a kirji yana kallon tangama-tangaman hotunan ta kamar ta fito ta yi magana da aka manna a kusurwa biyu na falon tabbacin ana ji da Ihsan kenan, kuma ita daya kenan a gidan tamfar rai ga iyayenta. Ko bude abubuwan da aka jera masa bai yi ba balle ya kai ga ci.
Ta samu kujera can nesa da shi ta harde, ta dauki remote control ta karo karfin A.C ko sannu da zuwa ba ta ce masa ba balle ci kan ka. Shi ne ya gaji da shirun ya bara, ya dubi agogon hannun shi Jovial ya ce,
“Saboda Allah Ihsan haka ake karbar baki ku a gidan ku?�
Ta sake tunzura ta ce, ‘Da aka yi me?�
Ya ce, “Kin san awanni biyu kenan kwarara, ina zaman jiran fitowar wani a cikin ku, amma shi ne sai yanzu ki ka ga damar fitowa?�
Ta yamutsa fuska ta ce a zafafe,
“Aminu, har kana da bakin gaya min haka? For God’s sake, yau kwanakin mu nawa a garin nan amma ka nuna wa iyayena ba ni da wata daraja a idon ka ba ka kuma damu da ni ba, shi ne kuma har za ka nemi gayan magana? Wai haka muke karbar baki, to ni ko iyayena da wa ka ke?� Ta tsatstsare shi da ido.
Al’ameen ya san ba shi da gaskiya, kuma ko a wurin Allah ne ba shi da ita. Dole ya sauke nashi temper n ya samu masangalin kujera ya rage tsawo, ya sanya hannu cikin aljihu ya zaro wayar shi da ke ta tsuwwa a cikin aljihun kaftanin shi, ya dade yana magana da aminin shi Rehab wato babban likitan Meritime yana gaya masa irin muhimman ayyukan da suka gabatar ne a kwanakin, ya ce ya yi kyau ya kuma yaba komai, ya gaya masa akwai motocin sa har yanzu suna port bai san ba a auno su ba, sai jiya ya je da kansa ya auno masa ta jirgin ruwa, amma ta Nijar za su biyo don ba jirgin kaya tun bayan da suka taso, don haka ya je ya fiddo su a Yamai. Suka yi sallama ya maida wayar shi aljihu.
Ya dubi Ihsan da sassanyan kallo ya ga ko kallon shi bata yi, ta maida fuskar ta can wani gefen daban bayan ta daure ta iya daurewa kamar bata san Allah ya yi ruwan tsirar shi ba ma, ransa ya sosu, amma sai ya yi murmushi ya ce,
“Ihsan kenan, dadi na da ke ba kya tsayawa ki ji uzurin mutum sai kawai ki kama fushi, amma ai ke ma dai kin san I missed you very-very much…�
Ya kira kalaman cikin tattausar muryar da ta kusa sa ta gyangyadi, amma da yake tana son ta nuna fushin nata sai ta cije ta kyabe baki a lokaci guda kuma tana girgiza kafa daya kan daya ita ala dole fushi take, duk sai ta ba shi dariya, ya mike har inda take ya mika mata hannuwan shi masu matukar taushi alamar ta tashi su yi sulhu, amman sai ta noke cikin jan aji irin nata, sai ya russuna ya kama hannayen ta duka biyun ya mikar da ita tsaye, suka fuskanci juna cikin ido, ita kallon haushi take masa shi kuma kallon I beg your pardon.
Ta ce, “Me ye haka?�
Amman can karkashin zuciyar ta hucewa take yi, tana kuma kara son mijinta a kowanne dakika, duk wata hanya da ya san zai bi ya wanke laifin shi a zuciyar ta ya san shi, duk da ta san kaunar da ita take masa ta rinjayi wadda yake mata, amma yana kokari a koyaushe ya nuna shi din mai son ta ne, mai gudun bacin ran ta ne.
Bare yanzun da ta yi kewarsa, fiye da yadda bakin ta zai iya fassarawa, sai ta bada kai bori ya hau. Sun dade cikin farantawa junansu tamkar suna gidan su koko bakin beaches na Miami, kafin su zauna su fuskanci juna, jikin ta a barin kafadun shi na dama, ta soma share hawaye da bayan hannu duk ya bi ya rikice ya ce,
“Me ye kuma?�