Sashe 73
Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ba komi take tunani ba illa a yau kam zata sabawa Daddy, bazata iya tafiya wajen mahaifiyar tata ba, ba ta je ta ga me yayi mata katanga da Alameen ba! Bata je taga halin da Daddyn ke ciki ba, wanda rabon da su neme ta an fi karfin wata uku, kai ba Daddy kadai ba, hatta Hidayah da Hunainah ba wanda ya kara yi mata waya, ba wanda ya aiko mata da ko sakon best-wishes akan jarrabawar ta, wanda ba haka ne tsarin rayuwar yaran ba; duk wani abu na farin ciki ko na fatar alkhairi su kan taya junan su.
Ta duba inbox din ta na e-mail ba bu sakon kowa sai na kawayenta yan sauran kasashe. Duk wayar da ta kira cikin danginta hagu da daman is not available me hakan ke nufi?
A karo na farko tun bayan rabuwarsu a dakinta, ranar da ta zamo rana ta karshe da bata sake ganin shi ba, illa wannan murmushin da yayi mata irin wanda bai taba yi ba, kuma wanda har abada ba zai goge daga zuciyarta ba.
Ta shiga lallatsa nambobinsa tare da tambayar kanta to in ma kin sameshi me zaki ce da shi? Alameen don me ka gujeni ko don me baka nemana? Don ka daina so na ko don na kasance azzaluma a cikin soyayya?
Kamar kullum yau ma an ce da ita is not available. Ba ta hakura ba dai, ta budo dan guntun templete text kamar haka long time no see ta aika masa. Fiye da awa daya, bai dawo mata da (reply) ba.
Ta kifa kanta cikin cinyoyin ta cikin yanayi na tashin hankali da matsananciyar faduwar gaba. A karo na biyu ta kara kokarin kiran layin Ambassada wannan karon ta samu ta shiga cikin saa, bugun farko ya amsa inda ya shiga bata hakurin rashin nemanta da baa yi yace alamura sun cudewa kowa, kuma suma sun yi tafiya sai kwanan baya suka dawo. Mamarta kuna bata da lafiya laulayin ciki ke wahalar da ita shi yasa ta rufe waya.
Ta bukaci tana so ne a canza mata booking zuwa Nigeria. Ya ce maiyasa kike son maida hannun agogo baya? Ya an gama komi tahowa kawai ya rage ki ce a canza, kuma Daddy zai yi fada tunda shi ya ce ki zo ki zauna da mahaifiyar ki, har sai yace ki dawo da kansa. Sai ta saka masa kuka mai karya zuciya, ta ce
don Allah Abban Hunainah ka taimake ni, ka yi min rai hankali na yayi gida, in ya so idan na je na ga Daddy sai in dawo koda kwana daya ne, ni dai hakannan na ke jin babu dadi, kuma hankali na ba zai taba kwanciya ba muddin ban je naga halin da Daddy ke ciki ba. Ka taimake ni kayi wa Daddy bayani yadda ba zai ce na ki jin maganarsa ba. Ni dai ji na ke a jiki na Daddy bashi da lafiya.
Ya ji idanuwan sa sun ciko da kwallah amma yayi kokarin maida su. Ya ce alright, Saratu, zan kira Daddyn yanzu muyi maganar, in ya ce ki taho zan kira air-port din yanzu. Amma ki kwantar da hankalin ki Daddynki lafiyar shi kalau ko jiya mun yi hira da shi.
Ta yi ajiyar zuciya mai karfi. Bayan kamar awa daya ya sake kiran ta, ya ce shikenan sai gida gobe Insha Allah, Daddyn ya ce da kanshi zai je air-port taryen ki. Sai ta yi murmushi.
How much do you like this story?
5/14/22, 09:27 - Ummi Tandama😇: ____________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book four
*@Takori*
Page4ï¸âƒ£
Hakan kuwa a kayi, ta fito daga jirgin MEA International sanye da doguwar riga kirar Oman, ta yane kanta da kankanin mayafin panorama kalar baki da ratsin toka-toka, yayinda abnormal idanuwanta ke saye cikin farin medicated din ta mai kama da gidan biro sabida sirinta. Kafar ta bakin takalmi ne mai tsayi sosai kuma mai tsari da ban shaawa, babu wani make-up a tare da kasaitacciyar fuskar ta, sai wannan kyawun ziryan mara algus da kyale-kyalen zamani Ta na rataye da matsakaiciyar jakar hannu, siraran labbanta dauke da murmushi kayatacce ga Daddynta data fara yin tozali da shi.
Ranta yayi dadi da ganin wannan taron dangi da aka yi dominta. Ga dai shakikiyarta Hidayah rike da hannun mijinta Najibullahi, ga Antin ta, ga Aunty Ihsan, ga Bello, Nasir, Yasir, Idris, Furkan da Khalil uwa-uba babban Yaya Faisal Bello Makarfi. To amma duk wannan gayya ta hanga, ta duba bata hango zahran cikin taurarin ba, ba ta hango haske maganin duhun zuciyar ta ba (bata hango Alameen din ta ba).
Duk da haka ta daure, ko a fuska bata nuna ba, tabi kowa da runguma, amma data zo kan Ihsan sai da ta dan dakata kadan kamar mai nazarin wani abu, kana ta daure ta rungumeta itama, sai ta ji wani abu mai tsini ya tokare ta wanda babu ko tantama ciki ne mai girma sosai.
Ji tayi wani abu yazo ya tokare a makoshin ta. A yau kam ta samu kanta tana mai kishin Ihsan fiye da koyaushe a rayuwar ta.
Ko kamin ta iso kan Faisal shi har yayi gaba ya bude mota ya shiga yana jiran su, daman shi ya yi driving dinsu cikin babbar mota Jeep baka mai tudu da tsayi. Hannunta cikin na Daddynta, hakannan kujera daya suka zauna. Sai a lokacin ta lura da muguwar ramar da kowannen su yayi, ba kuma wanda ya yarda ya kara hada ido da ita, kai ba ma wannan ya dame ta ba kamar muguwar hararar da Faisal ke jefa mata a duk sanda su kai kuskuren hada idanu ta cikin mudubin motar.
Karewa ma babu mai yin ko kwakkwaran motsi a motar tamkar ruwa ya cinye su. Tun tana kai zuciya nesa tana tausar zuciyar ta da cewa ai koma meye tunda gani a gidan zan ji ne har ta kasa controlling tashin hankalin ta kawai sai ta fashe da kuka, cikin siririyar muryar ta mai tsuma zuciya tace ku sauke ni, ku sauke ni a titin nan tunda duk bakin-ciki kuke da dawowa ta, zan koma inda na fito.
Daddy ya yi murmushi ya kama hannunta na dama yace,
“Waye mai bakin-ciki da dawowar ki Saratu, gayamin sunan shi yanzu in sauke shi, ya nemi wani uban daban amma ba naki ba, umh waye shi Intisar gaya mun ki gani in baa sauke shi ba?�
Ita dai bata bar kukanta ba, haka Ihsan da Hidayah kuka suke cikin mayafansu, kuka mara amo bare sauti sai radadi a zuci.
Koda suka iso gida ma bata sake zani ba, kowa yayi nasa waje, Faisal ya wuce da Daddy office Najib da Hidayah sun wuce gidansu a Maitama, Ihsan ma ta wuce dakinda aka ware mata, inda anan ne take zanan takaba da rainon cikinta don Daddy yace bazata rabu da su ba har sai ta haihu, dan ta ko yar ta yayi wayo daga nan tana da zabi a rayuwar ta. Mahaifinta ya amince da hakan amma Ann cewa tayi wahala ce bata ishe ta ba.
Dawowar Intisar gidan sai ya zama tamkar wani fami ne bisa ciwon da ya fara samun sauki ga kowa a gidan. Wai Antin ta mai tarairayar ta da rasa ina taka saka ina-taka aje da ita a duk lokacin da ta dawo hutu, ita ce yau mai kakalo aiki don kawai kada ta zauna da ita ko na minti daya ne a dakin, kai daga karshe ma da taga kukan da Intisar din ta soma na neman karya mata zuciya itama ta fashe da kukan duk irin kokarin ta kuwa, sai ta gudu sassan Daddy Intisar din bata kara ko jin duriyar ta ba.
Aah, wai me ke shirin faruwa ne? Ta kasa baiwa kanta amsa, me ya kawo Ihsan gidan har daki aka ware mata cikin sassan Anti, ina Alameen?
Sai a lokacin ne ta daga idanunta cikin gilashinta, ta kai duba ga katon hoton shi window-size da ke makale a falon tun kamin ta tafi, babu hoton an dauke shi. Ta sunkuyar da kai, haka kawai ta ji mummunar faduwar gaba ta same ta, jinni ya daskare daga gudun da yake yi cikin jikin ta. Kada Allah yasa abinda zuciyarta ta sinsina ya tabbata. Kada Allah ya sa a ce da ita a yau babu Alameen. Ka da Allah ya nuna mata wannan ranar!
Ta kai hannu ta share kwarmin idanunta a dai-dai lokacin da Khaleel ya shigo, daga bakin kofa ya sanar da ita Daddy na kiranta, ba kuma tare daya kara ce da ita komi ba ya juya ya fita.
Ta mike cikin rashin kuzari, tamkar kazar da kwai ya fashewa a ciki ta doshi main falon su. Kowa na zaune, da yawa kansu a sunkuye, kadan ne suka dube ta. Ta yi mamakin duk wannan taron da a kayi mata na menene?
Ta kai dubanta ga Mamarta, domin neman Karin bayani, amma kamar dazu tayi ignoring hada ido da ita. Daddy ya mike da kan sa har inda take ya kamo hannunta, ya zaunar da ita a gefen sa.
Ya ce mu karanta salati goma sha daya ga Annabi (S.A.W), mu karanta kulhuwallahu kafa (3) zuwa makwancin sa, mu kara godiya ga Allah da yayo mu Musulmi maabota Imani da yadda da Kaddara.
Bayan sun shafa ya dubi Intisar da tashin hankali ke zane baro-baro bisa kyakkyawar fuskar ta tamkar ta daura hannu a ka ta ce wayyo Allah! Ya dubeta da sassamyan duba mai sa nutsuwa ga dan adam ya ce,
“Saratu!�
Ta dago ta dube shi da dukkan idanu amma bata amsa ba, idanunta fiki-fiki a warwaje. Ya yi murmushi yace zaki iya gaya mun me da me Ubangiji Allah yayi miki a rayuwarki, kama daga lokacin haihuwar ki zuwa yau da kika dawo?
Ta shiga girgiza kai da sauri, hawayen ta na zuba bisa cinyar ta ta ce,
Ta duba inbox din ta na e-mail ba bu sakon kowa sai na kawayenta yan sauran kasashe. Duk wayar da ta kira cikin danginta hagu da daman is not available me hakan ke nufi?
A karo na farko tun bayan rabuwarsu a dakinta, ranar da ta zamo rana ta karshe da bata sake ganin shi ba, illa wannan murmushin da yayi mata irin wanda bai taba yi ba, kuma wanda har abada ba zai goge daga zuciyarta ba.
Ta shiga lallatsa nambobinsa tare da tambayar kanta to in ma kin sameshi me zaki ce da shi? Alameen don me ka gujeni ko don me baka nemana? Don ka daina so na ko don na kasance azzaluma a cikin soyayya?
Kamar kullum yau ma an ce da ita is not available. Ba ta hakura ba dai, ta budo dan guntun templete text kamar haka long time no see ta aika masa. Fiye da awa daya, bai dawo mata da (reply) ba.
Ta kifa kanta cikin cinyoyin ta cikin yanayi na tashin hankali da matsananciyar faduwar gaba. A karo na biyu ta kara kokarin kiran layin Ambassada wannan karon ta samu ta shiga cikin saa, bugun farko ya amsa inda ya shiga bata hakurin rashin nemanta da baa yi yace alamura sun cudewa kowa, kuma suma sun yi tafiya sai kwanan baya suka dawo. Mamarta kuna bata da lafiya laulayin ciki ke wahalar da ita shi yasa ta rufe waya.
Ta bukaci tana so ne a canza mata booking zuwa Nigeria. Ya ce maiyasa kike son maida hannun agogo baya? Ya an gama komi tahowa kawai ya rage ki ce a canza, kuma Daddy zai yi fada tunda shi ya ce ki zo ki zauna da mahaifiyar ki, har sai yace ki dawo da kansa. Sai ta saka masa kuka mai karya zuciya, ta ce
don Allah Abban Hunainah ka taimake ni, ka yi min rai hankali na yayi gida, in ya so idan na je na ga Daddy sai in dawo koda kwana daya ne, ni dai hakannan na ke jin babu dadi, kuma hankali na ba zai taba kwanciya ba muddin ban je naga halin da Daddy ke ciki ba. Ka taimake ni kayi wa Daddy bayani yadda ba zai ce na ki jin maganarsa ba. Ni dai ji na ke a jiki na Daddy bashi da lafiya.
Ya ji idanuwan sa sun ciko da kwallah amma yayi kokarin maida su. Ya ce alright, Saratu, zan kira Daddyn yanzu muyi maganar, in ya ce ki taho zan kira air-port din yanzu. Amma ki kwantar da hankalin ki Daddynki lafiyar shi kalau ko jiya mun yi hira da shi.
Ta yi ajiyar zuciya mai karfi. Bayan kamar awa daya ya sake kiran ta, ya ce shikenan sai gida gobe Insha Allah, Daddyn ya ce da kanshi zai je air-port taryen ki. Sai ta yi murmushi.
How much do you like this story?
5/14/22, 09:27 - Ummi Tandama😇: ____________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book four
*@Takori*
Page4ï¸âƒ£
Hakan kuwa a kayi, ta fito daga jirgin MEA International sanye da doguwar riga kirar Oman, ta yane kanta da kankanin mayafin panorama kalar baki da ratsin toka-toka, yayinda abnormal idanuwanta ke saye cikin farin medicated din ta mai kama da gidan biro sabida sirinta. Kafar ta bakin takalmi ne mai tsayi sosai kuma mai tsari da ban shaawa, babu wani make-up a tare da kasaitacciyar fuskar ta, sai wannan kyawun ziryan mara algus da kyale-kyalen zamani Ta na rataye da matsakaiciyar jakar hannu, siraran labbanta dauke da murmushi kayatacce ga Daddynta data fara yin tozali da shi.
Ranta yayi dadi da ganin wannan taron dangi da aka yi dominta. Ga dai shakikiyarta Hidayah rike da hannun mijinta Najibullahi, ga Antin ta, ga Aunty Ihsan, ga Bello, Nasir, Yasir, Idris, Furkan da Khalil uwa-uba babban Yaya Faisal Bello Makarfi. To amma duk wannan gayya ta hanga, ta duba bata hango zahran cikin taurarin ba, ba ta hango haske maganin duhun zuciyar ta ba (bata hango Alameen din ta ba).
Duk da haka ta daure, ko a fuska bata nuna ba, tabi kowa da runguma, amma data zo kan Ihsan sai da ta dan dakata kadan kamar mai nazarin wani abu, kana ta daure ta rungumeta itama, sai ta ji wani abu mai tsini ya tokare ta wanda babu ko tantama ciki ne mai girma sosai.
Ji tayi wani abu yazo ya tokare a makoshin ta. A yau kam ta samu kanta tana mai kishin Ihsan fiye da koyaushe a rayuwar ta.
Ko kamin ta iso kan Faisal shi har yayi gaba ya bude mota ya shiga yana jiran su, daman shi ya yi driving dinsu cikin babbar mota Jeep baka mai tudu da tsayi. Hannunta cikin na Daddynta, hakannan kujera daya suka zauna. Sai a lokacin ta lura da muguwar ramar da kowannen su yayi, ba kuma wanda ya yarda ya kara hada ido da ita, kai ba ma wannan ya dame ta ba kamar muguwar hararar da Faisal ke jefa mata a duk sanda su kai kuskuren hada idanu ta cikin mudubin motar.
Karewa ma babu mai yin ko kwakkwaran motsi a motar tamkar ruwa ya cinye su. Tun tana kai zuciya nesa tana tausar zuciyar ta da cewa ai koma meye tunda gani a gidan zan ji ne har ta kasa controlling tashin hankalin ta kawai sai ta fashe da kuka, cikin siririyar muryar ta mai tsuma zuciya tace ku sauke ni, ku sauke ni a titin nan tunda duk bakin-ciki kuke da dawowa ta, zan koma inda na fito.
Daddy ya yi murmushi ya kama hannunta na dama yace,
“Waye mai bakin-ciki da dawowar ki Saratu, gayamin sunan shi yanzu in sauke shi, ya nemi wani uban daban amma ba naki ba, umh waye shi Intisar gaya mun ki gani in baa sauke shi ba?�
Ita dai bata bar kukanta ba, haka Ihsan da Hidayah kuka suke cikin mayafansu, kuka mara amo bare sauti sai radadi a zuci.
Koda suka iso gida ma bata sake zani ba, kowa yayi nasa waje, Faisal ya wuce da Daddy office Najib da Hidayah sun wuce gidansu a Maitama, Ihsan ma ta wuce dakinda aka ware mata, inda anan ne take zanan takaba da rainon cikinta don Daddy yace bazata rabu da su ba har sai ta haihu, dan ta ko yar ta yayi wayo daga nan tana da zabi a rayuwar ta. Mahaifinta ya amince da hakan amma Ann cewa tayi wahala ce bata ishe ta ba.
Dawowar Intisar gidan sai ya zama tamkar wani fami ne bisa ciwon da ya fara samun sauki ga kowa a gidan. Wai Antin ta mai tarairayar ta da rasa ina taka saka ina-taka aje da ita a duk lokacin da ta dawo hutu, ita ce yau mai kakalo aiki don kawai kada ta zauna da ita ko na minti daya ne a dakin, kai daga karshe ma da taga kukan da Intisar din ta soma na neman karya mata zuciya itama ta fashe da kukan duk irin kokarin ta kuwa, sai ta gudu sassan Daddy Intisar din bata kara ko jin duriyar ta ba.
Aah, wai me ke shirin faruwa ne? Ta kasa baiwa kanta amsa, me ya kawo Ihsan gidan har daki aka ware mata cikin sassan Anti, ina Alameen?
Sai a lokacin ne ta daga idanunta cikin gilashinta, ta kai duba ga katon hoton shi window-size da ke makale a falon tun kamin ta tafi, babu hoton an dauke shi. Ta sunkuyar da kai, haka kawai ta ji mummunar faduwar gaba ta same ta, jinni ya daskare daga gudun da yake yi cikin jikin ta. Kada Allah yasa abinda zuciyarta ta sinsina ya tabbata. Kada Allah ya sa a ce da ita a yau babu Alameen. Ka da Allah ya nuna mata wannan ranar!
Ta kai hannu ta share kwarmin idanunta a dai-dai lokacin da Khaleel ya shigo, daga bakin kofa ya sanar da ita Daddy na kiranta, ba kuma tare daya kara ce da ita komi ba ya juya ya fita.
Ta mike cikin rashin kuzari, tamkar kazar da kwai ya fashewa a ciki ta doshi main falon su. Kowa na zaune, da yawa kansu a sunkuye, kadan ne suka dube ta. Ta yi mamakin duk wannan taron da a kayi mata na menene?
Ta kai dubanta ga Mamarta, domin neman Karin bayani, amma kamar dazu tayi ignoring hada ido da ita. Daddy ya mike da kan sa har inda take ya kamo hannunta, ya zaunar da ita a gefen sa.
Ya ce mu karanta salati goma sha daya ga Annabi (S.A.W), mu karanta kulhuwallahu kafa (3) zuwa makwancin sa, mu kara godiya ga Allah da yayo mu Musulmi maabota Imani da yadda da Kaddara.
Bayan sun shafa ya dubi Intisar da tashin hankali ke zane baro-baro bisa kyakkyawar fuskar ta tamkar ta daura hannu a ka ta ce wayyo Allah! Ya dubeta da sassamyan duba mai sa nutsuwa ga dan adam ya ce,
“Saratu!�
Ta dago ta dube shi da dukkan idanu amma bata amsa ba, idanunta fiki-fiki a warwaje. Ya yi murmushi yace zaki iya gaya mun me da me Ubangiji Allah yayi miki a rayuwarki, kama daga lokacin haihuwar ki zuwa yau da kika dawo?
Ta shiga girgiza kai da sauri, hawayen ta na zuba bisa cinyar ta ta ce,