Sashe 63
Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abinda nake so da ke shine ki tsaya ki gina rayuwarki a bisa tubala na kwarai, in ba hakaba ba mamaki bada jimawa ba soyayya ta ruguzata. Al’ameen ya fiki wayo, daga shi har matarshi ba tsaranki bane a budewar kai da ilmi.
Don haka ki tsaya ki nemawa kanki madogara mai kyau tukunna, wanda shine wannan ilimin mai matukar wuya. Idan kika sameshi samun Aminu ba zai maki wuya ba haka in kika barshi ke da banza a cikin su daya kuke, don sai kin raina kan ki a cikinsu.
Ni in son raina ne ma Allah bana son ki auri mai mata irin Ihsan, ki dubi yadda take hauka akan mijinta fa, ke ‘yar nan, mind yourself (ki shiga taitayinki)�. Ahaf! Ai kamar Antin ta shiga ranta taga abinda take shiri komawa makaranta, tayi murmushi tare da saurin rufe ido, maganganun Antin take aunawa abisa sikeli daya bayan daya, wanda dama duk tayi tunaninsu, babu wanda bata ga gaskiya a ciki ba, ta ce a raunane.
“Na gode Aunty.�
Ta rufe wayar, sai yanzu ya fuskanci da wa take magana, bata ko dubeshi ba ta murda kofar da zata hadaka da dakin ta daga falon Anti, yayi hamzarin murda keys ya zare ya tura aljihun bayan wandon ‘basachi� dake jikinsa ya ce.
“Me Anti Hajjo ke gaya maki a waya, kike godewa kina kuma kara yi mun asaran hawayen da nake ganin daraja da kimar su fiye da na kowa?�
Wasu ubansu harara da ta watso mai ya bashi mamaki don bai taba ganin tayi ba, ga idanun sunyi jawur sai ta kara kyau a idon shi, ko da yake so ne hana ganin aibi, ya ce, “Inteesar� da muryar nan da ke karya lagonta, ta kassara kuzarin ta, amma a yau ko gezau, har yanzu hararar shi ta ke ba kakkautawa.
Ya soma taki har inda take tsaye tamkar sassakakken gunki, ta soma ja da baya kamar wadda taga abin tsoro da kyama, ta san ba karamin aikin shi ba ne ya kamata da kokawa kawai don ya sata yin magana, cikin tsiwa da yatsina ta bude dan bakinta tana mai nunashi da dan manuninta ta ce,
“Wallahi Al’ameen ka sake ka tabani yau zan fasa ma kaine, in bar inyamurar matarka da jiyyar da baka taba yi ba.� Bai fasa dosarta ba ya ce,
“Jinya kuma wacce ce ba’ayi ba? Sai dai kar a kuma, idan jinya ta ciwon son halimah ce, to ayi ta yi kar a tashi. Kar ki kara kira mun mata inyamura, yadda kike musulma diyar musulmi, haka itama take.� dai-dai lokacin da ta dangana da bangon karshe na falon, shi kuma bai fasa bin ta ba, ta ce,
“Wallahi zan kirawo Anti, tayi ma kashedin shiga harkana, ka nemo Halimar ka can amma ni Intisar ce, ka manta ka taba sanina a rayuwarka, ina gaya maka, ina kara gaya maka� ya toshe mata baki. Ya ja hannunta na dama da karfi har bisa seater dake tsakiyar falon, ta karfin tsiya ya zaunarta ya ce,
“Ke in ma Daddy zaki kirawo babu laifi. Amma sai na gama maganar da zan yi. Kin san me ya kawo ni?
Zuwa nayi in gaya maki ranar da duk wannan maganannen bakin ya kara kuskuren cewa bazai aureni ba don uwata, wallahi sai na kakkarya ki.�
Cikin tsiwar da bai san ta iya ba ta ce,
‘Ka karya ni? To ka ji ka sani ko da can da ka makantani, don ban da wayo ne, amma yanzu wallahi sai dai ayi ‘yar bibbiyu� saura kadan da dariya ta kwace masa, to amma shi kansa yasan bai kyauta ba, jiya ya mareta yau ya gaya mata kakkausar magana, shi da ke neman wanke dattin da Hajiya ta yayyaba masu daga idanunta.
Ya dire gwiwoyinsa bisa carpet abinda bai taba yiwa wata ‘ya mace a rayuwarsa ba, a yayinda ita kuma take zaune cikin kujera ta cika fam, kiris take jira ta fashe.
Ya langabe kai gefe guda gwanin ban tausayi, yayi kamar ya share mata hawayen da suka soma surtu, sai kuma yafasa. Ya ce,
“Inteesarr!�
Yadda ya kira sunan cikin murya mai karkarwa da kauri (husky) kadai ya birkita Saratun, bata jin ko dan yatsanta zata iya motsawa. Ya ce,
“I ‘am sorry, terribly sorry! Wallahi ni, wasa nake maki, in karya ki in ce na karya wa kenan?
Jiya kuma zuciya ce ta debe ni, kin san bata da kashi, abinda kika fadi cikin mutane ya bata mun kwarai. Ni kaina ban san ya akai ba, Pls, 4 give me…� Ya karasa a raunane, kana ya matso ‘yar kwallah, ya maida ta bisa kujerar ya ce,
“Wallahi Intisar nasan Hajiya ta bata miki, to amma ni meye laifina? Ni ban ji tsoron abinda hakan zai janyo man ba daga gareta na furta ina sonki? Sannan kuma bakya tausaya mun halinda zan shiga in na rasa ki kwata-kwata, ki tuna baya?�
Ta sadda kai kawai, bata son jin wannan abun da take ji game da Aminu, bata son wadannan ‘feelings� din da take ji game da shi masu tada tsigogin jikinta a duk lokacin da suke tare, to amma Al’ameen din kamar wani mayen karfe ne, wuyarta yayi mata magana da wannan muryan nashi mai jan mutum uwa lantarki duk wani ‘weakness� din ta ya gama samunshi.
Ta tabbata nisa da shi shine abu mafi a’ala a gareta in har tana son cimma kudurirrikanta akan Haj. Nafi, wadanda daga ita sai zuciyarta sai mahaliccinta suka san na mene, amma ba don bata son shi ba.
Karya ne ko fatar bakinta ta fada, to bacin rai ne. Shi kadai take so har cikin tsokar zuciyarta, har gangar jiki zuwa kwakwalwarta babu inda baya girgiza da kaunar Al’ameen da sha’awar komi nashi, ita kadai ta san me take ji da yakin da take yi da zuciyarvta a duk lokacin da yai kuskuren kai hannunshi gareta koda yatsar hannunta ne kuwa amma ta rantse, ta kuma ta rantse ko son sa zai kasheta, ko duk duniya zata taru a kanta, bazata aure shi ba!
A ganinta ta hakanne kadai zata rama abinda sukai mata shi da mahaifiyarsa wanda har abada bazata manta ba, ba zata yafe mata ba kuma ba zata daina tunawa ba.
Bata san wannan hukuncin da ta yanke yai tsauri ba, domin son da Al’ameen ke mata Allah kadai ya san iyakarsa; ba na wasa bane, ya wuce ayi ramuwar gayya akansa yayi masa tsauri bazai iya dauka ba. Da kyar in bata yi kuskure ba, da kyar in hukuncinta ba zai zamo nadama mara amfani a gareta ba.
Ya cira hannunta ya aza bisa kirjinshi, tana iya jin nannauyan bugun da zuciyarsa ke yi akai-akai, jikinta ya soma sanyi, ya ce,
“Ki ji Intisar, kiji irin bugun da zuciyar nan ke yi a domin ki, saboda ke ne take ciwon da har abada bazata daina ba, ba kya tausayi na Intisar ba kya sona yanzun? Allah na rantse, in muka cigaba da tafiya a haka wata rana�. Wata rana bugawa zatayi gabadaya ta fashe kowa ya huta, ki taimake ni ki agaje ni, ki daina la’akari da laifin da ba nawa ba kina hukunta ni dashi don Allah?�
Ita dai ta zamo ‘pale� ko motsi ta kasa balle tayi kokarin yin wani abu, ta rasa abinda ke mata dadi shi kuma bakinshi bai yi shiru ba da gaya mata irin halin da zai shiga in ya rasata. Har ya kai ga kwantar da kansa bisa kafadunta.
Cikin wannan halin Faisal ya turo kofar falon ya shigo, fes idon shi a kan su, ya juya da sauri yana cewa, “Excuse me plz. Ya Aminu ban sani ba!�.
Ta mike a gigice ta banka dakin Anti, ta kifa kai bisa gado ta soma rera kuka sabo fil. Ina rowan mai neman kuka an jefeshi da dunkulen kashi.
Gabadaya suka zubo mata ido Anti da Ihsan suka yo kanta Anti ta ce,
“To kin gani Ihsan mijinki kullum sai yasa min ‘ya kuka, don haka ki je ki ja kayan ki ku tafi.� Ta sake kuluwa ta shaka ance Al’amin mijin Ihsan, ta sake tsugewa da kuka.
Ihsan ta matsa jikin gadon ta dago kanta ta aza bisa cinyarta tana murmushi tace “Haba little sister na, kin hana mun miji sakat ko tausayinshi ba kya ji, jiya saura kadan ya sakeni, don Allah kiyi hakuri ki bamu hadin kai ko na samu kan Al’ameen nima…�
Ta soma fidda kwalla itama, wani tukuki na cinta a rai, wai yau itace da kanta ke rokon wata ‘yar ficikar yarinya ta so mijin ta, Aminunta data gama shan bakar wahala a kansa, ta sadaukar da komi nata dominsa, take son sa tamkar ta fidda zuciyarta, ayya rayuwa!
Ta daure ta share wasu azababbun hawaye da suka biyo kumatun ta a guje ta ce, “Intisar, Al’ameen ya gaya mun bazamu taba samun kwanciyar hankali ba in har baki yarda da maganar auren ku ba. Don Allah Intisar ki taimake ni.�
Aunty ta juya ta fita, bata iya jure ganin wannan abin tausayi. Ita Ihsan din ce ta ke bata tausayi, ta tabbata ba karamin so takewa mijinta ba, abinda tayi mata da yawa baza su iya ba, dazu akan idonta Aminu ya turo kofa ya rufesu har da mukulli amma sai cewa tayi.
“Allah dai yasa ya shawo kanta. Don na lura Intissar akwai zucciya.�
Intisar ta dago don babatun Ihsan ya isheta, fuskar nan jike sharab da hawaye ta dubeta sosai ta ce,
“Ina ganin mutuncin ki, don haka don Allah don Annabi Anti Ihsan ba ruwan ki, ki rabu da Al’ameen kawai, shi bai ji tausayi na ba sadda yake kwallo dani har na zamo nakasashshiya? Hajiyarsa bata ji tausayi na ba a sadda Daddy ke kwallo da ni ba a gabanta, da sadda take fyaula mun kebur? Take sa min shocking? Ke har da kan ki kike son in auri mijin ki ashe karya kike ba son shi kike ba.
Don haka ki tsaya ki nemawa kanki madogara mai kyau tukunna, wanda shine wannan ilimin mai matukar wuya. Idan kika sameshi samun Aminu ba zai maki wuya ba haka in kika barshi ke da banza a cikin su daya kuke, don sai kin raina kan ki a cikinsu.
Ni in son raina ne ma Allah bana son ki auri mai mata irin Ihsan, ki dubi yadda take hauka akan mijinta fa, ke ‘yar nan, mind yourself (ki shiga taitayinki)�. Ahaf! Ai kamar Antin ta shiga ranta taga abinda take shiri komawa makaranta, tayi murmushi tare da saurin rufe ido, maganganun Antin take aunawa abisa sikeli daya bayan daya, wanda dama duk tayi tunaninsu, babu wanda bata ga gaskiya a ciki ba, ta ce a raunane.
“Na gode Aunty.�
Ta rufe wayar, sai yanzu ya fuskanci da wa take magana, bata ko dubeshi ba ta murda kofar da zata hadaka da dakin ta daga falon Anti, yayi hamzarin murda keys ya zare ya tura aljihun bayan wandon ‘basachi� dake jikinsa ya ce.
“Me Anti Hajjo ke gaya maki a waya, kike godewa kina kuma kara yi mun asaran hawayen da nake ganin daraja da kimar su fiye da na kowa?�
Wasu ubansu harara da ta watso mai ya bashi mamaki don bai taba ganin tayi ba, ga idanun sunyi jawur sai ta kara kyau a idon shi, ko da yake so ne hana ganin aibi, ya ce, “Inteesar� da muryar nan da ke karya lagonta, ta kassara kuzarin ta, amma a yau ko gezau, har yanzu hararar shi ta ke ba kakkautawa.
Ya soma taki har inda take tsaye tamkar sassakakken gunki, ta soma ja da baya kamar wadda taga abin tsoro da kyama, ta san ba karamin aikin shi ba ne ya kamata da kokawa kawai don ya sata yin magana, cikin tsiwa da yatsina ta bude dan bakinta tana mai nunashi da dan manuninta ta ce,
“Wallahi Al’ameen ka sake ka tabani yau zan fasa ma kaine, in bar inyamurar matarka da jiyyar da baka taba yi ba.� Bai fasa dosarta ba ya ce,
“Jinya kuma wacce ce ba’ayi ba? Sai dai kar a kuma, idan jinya ta ciwon son halimah ce, to ayi ta yi kar a tashi. Kar ki kara kira mun mata inyamura, yadda kike musulma diyar musulmi, haka itama take.� dai-dai lokacin da ta dangana da bangon karshe na falon, shi kuma bai fasa bin ta ba, ta ce,
“Wallahi zan kirawo Anti, tayi ma kashedin shiga harkana, ka nemo Halimar ka can amma ni Intisar ce, ka manta ka taba sanina a rayuwarka, ina gaya maka, ina kara gaya maka� ya toshe mata baki. Ya ja hannunta na dama da karfi har bisa seater dake tsakiyar falon, ta karfin tsiya ya zaunarta ya ce,
“Ke in ma Daddy zaki kirawo babu laifi. Amma sai na gama maganar da zan yi. Kin san me ya kawo ni?
Zuwa nayi in gaya maki ranar da duk wannan maganannen bakin ya kara kuskuren cewa bazai aureni ba don uwata, wallahi sai na kakkarya ki.�
Cikin tsiwar da bai san ta iya ba ta ce,
‘Ka karya ni? To ka ji ka sani ko da can da ka makantani, don ban da wayo ne, amma yanzu wallahi sai dai ayi ‘yar bibbiyu� saura kadan da dariya ta kwace masa, to amma shi kansa yasan bai kyauta ba, jiya ya mareta yau ya gaya mata kakkausar magana, shi da ke neman wanke dattin da Hajiya ta yayyaba masu daga idanunta.
Ya dire gwiwoyinsa bisa carpet abinda bai taba yiwa wata ‘ya mace a rayuwarsa ba, a yayinda ita kuma take zaune cikin kujera ta cika fam, kiris take jira ta fashe.
Ya langabe kai gefe guda gwanin ban tausayi, yayi kamar ya share mata hawayen da suka soma surtu, sai kuma yafasa. Ya ce,
“Inteesarr!�
Yadda ya kira sunan cikin murya mai karkarwa da kauri (husky) kadai ya birkita Saratun, bata jin ko dan yatsanta zata iya motsawa. Ya ce,
“I ‘am sorry, terribly sorry! Wallahi ni, wasa nake maki, in karya ki in ce na karya wa kenan?
Jiya kuma zuciya ce ta debe ni, kin san bata da kashi, abinda kika fadi cikin mutane ya bata mun kwarai. Ni kaina ban san ya akai ba, Pls, 4 give me…� Ya karasa a raunane, kana ya matso ‘yar kwallah, ya maida ta bisa kujerar ya ce,
“Wallahi Intisar nasan Hajiya ta bata miki, to amma ni meye laifina? Ni ban ji tsoron abinda hakan zai janyo man ba daga gareta na furta ina sonki? Sannan kuma bakya tausaya mun halinda zan shiga in na rasa ki kwata-kwata, ki tuna baya?�
Ta sadda kai kawai, bata son jin wannan abun da take ji game da Aminu, bata son wadannan ‘feelings� din da take ji game da shi masu tada tsigogin jikinta a duk lokacin da suke tare, to amma Al’ameen din kamar wani mayen karfe ne, wuyarta yayi mata magana da wannan muryan nashi mai jan mutum uwa lantarki duk wani ‘weakness� din ta ya gama samunshi.
Ta tabbata nisa da shi shine abu mafi a’ala a gareta in har tana son cimma kudurirrikanta akan Haj. Nafi, wadanda daga ita sai zuciyarta sai mahaliccinta suka san na mene, amma ba don bata son shi ba.
Karya ne ko fatar bakinta ta fada, to bacin rai ne. Shi kadai take so har cikin tsokar zuciyarta, har gangar jiki zuwa kwakwalwarta babu inda baya girgiza da kaunar Al’ameen da sha’awar komi nashi, ita kadai ta san me take ji da yakin da take yi da zuciyarvta a duk lokacin da yai kuskuren kai hannunshi gareta koda yatsar hannunta ne kuwa amma ta rantse, ta kuma ta rantse ko son sa zai kasheta, ko duk duniya zata taru a kanta, bazata aure shi ba!
A ganinta ta hakanne kadai zata rama abinda sukai mata shi da mahaifiyarsa wanda har abada bazata manta ba, ba zata yafe mata ba kuma ba zata daina tunawa ba.
Bata san wannan hukuncin da ta yanke yai tsauri ba, domin son da Al’ameen ke mata Allah kadai ya san iyakarsa; ba na wasa bane, ya wuce ayi ramuwar gayya akansa yayi masa tsauri bazai iya dauka ba. Da kyar in bata yi kuskure ba, da kyar in hukuncinta ba zai zamo nadama mara amfani a gareta ba.
Ya cira hannunta ya aza bisa kirjinshi, tana iya jin nannauyan bugun da zuciyarsa ke yi akai-akai, jikinta ya soma sanyi, ya ce,
“Ki ji Intisar, kiji irin bugun da zuciyar nan ke yi a domin ki, saboda ke ne take ciwon da har abada bazata daina ba, ba kya tausayi na Intisar ba kya sona yanzun? Allah na rantse, in muka cigaba da tafiya a haka wata rana�. Wata rana bugawa zatayi gabadaya ta fashe kowa ya huta, ki taimake ni ki agaje ni, ki daina la’akari da laifin da ba nawa ba kina hukunta ni dashi don Allah?�
Ita dai ta zamo ‘pale� ko motsi ta kasa balle tayi kokarin yin wani abu, ta rasa abinda ke mata dadi shi kuma bakinshi bai yi shiru ba da gaya mata irin halin da zai shiga in ya rasata. Har ya kai ga kwantar da kansa bisa kafadunta.
Cikin wannan halin Faisal ya turo kofar falon ya shigo, fes idon shi a kan su, ya juya da sauri yana cewa, “Excuse me plz. Ya Aminu ban sani ba!�.
Ta mike a gigice ta banka dakin Anti, ta kifa kai bisa gado ta soma rera kuka sabo fil. Ina rowan mai neman kuka an jefeshi da dunkulen kashi.
Gabadaya suka zubo mata ido Anti da Ihsan suka yo kanta Anti ta ce,
“To kin gani Ihsan mijinki kullum sai yasa min ‘ya kuka, don haka ki je ki ja kayan ki ku tafi.� Ta sake kuluwa ta shaka ance Al’amin mijin Ihsan, ta sake tsugewa da kuka.
Ihsan ta matsa jikin gadon ta dago kanta ta aza bisa cinyarta tana murmushi tace “Haba little sister na, kin hana mun miji sakat ko tausayinshi ba kya ji, jiya saura kadan ya sakeni, don Allah kiyi hakuri ki bamu hadin kai ko na samu kan Al’ameen nima…�
Ta soma fidda kwalla itama, wani tukuki na cinta a rai, wai yau itace da kanta ke rokon wata ‘yar ficikar yarinya ta so mijin ta, Aminunta data gama shan bakar wahala a kansa, ta sadaukar da komi nata dominsa, take son sa tamkar ta fidda zuciyarta, ayya rayuwa!
Ta daure ta share wasu azababbun hawaye da suka biyo kumatun ta a guje ta ce, “Intisar, Al’ameen ya gaya mun bazamu taba samun kwanciyar hankali ba in har baki yarda da maganar auren ku ba. Don Allah Intisar ki taimake ni.�
Aunty ta juya ta fita, bata iya jure ganin wannan abin tausayi. Ita Ihsan din ce ta ke bata tausayi, ta tabbata ba karamin so takewa mijinta ba, abinda tayi mata da yawa baza su iya ba, dazu akan idonta Aminu ya turo kofa ya rufesu har da mukulli amma sai cewa tayi.
“Allah dai yasa ya shawo kanta. Don na lura Intissar akwai zucciya.�
Intisar ta dago don babatun Ihsan ya isheta, fuskar nan jike sharab da hawaye ta dubeta sosai ta ce,
“Ina ganin mutuncin ki, don haka don Allah don Annabi Anti Ihsan ba ruwan ki, ki rabu da Al’ameen kawai, shi bai ji tausayi na ba sadda yake kwallo dani har na zamo nakasashshiya? Hajiyarsa bata ji tausayi na ba a sadda Daddy ke kwallo da ni ba a gabanta, da sadda take fyaula mun kebur? Take sa min shocking? Ke har da kan ki kike son in auri mijin ki ashe karya kike ba son shi kike ba.