← Book details Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 64 OF 90

Sashe 64

Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Baki sani ba, ni fa tunda fari ba son mijinki nake ba, kaddarar Allah ta hada mu a kichin kuma kaddarar ta raba, don haka ki tafi don Allah ina bukatar hutu, ina maku addu’a Allah ya baku kwanciyar hankalin ba sai tare da ni ba, ke ni ba wani aure da zan yi, da din ma dana amsa masa rashin galihu ne da rashin abin yi, yanzu kuwa ina da abinyi ina da galihu, ba wanda ya isa yayi kwallo da ni ban yi karar sa an fitar mun hakki na ba, ki je ki lallashi abinki ke daya ko ke ba mace bace baki ishe shi ba?�

Ta fiddo mata ido cikin barazana kamar gaske, bayan a zahiri ji take kamar ta makureta ta huce.

Ihsan tayi murmushi ta mike, a ranta ko cewa take lallai wannan yarinyace, danya (fresh), kalaminta kadai zaka ji ka tabbatar kurucci dangin hauka na dawainiya da ita, har akwai wata ‘ya mace mai cikakken hankali ta kuma san abinda takeyi da zata budi baki tace wai bata son Al’ameen Bello?

Ta mike ta na rataya jakarta ta nufi kofa ta ce,

“Ki dai kara baiwa zuciyar ki shawara Intisar, Al’ameen mai matukar son ki ne tsakani da Allah. Ba fata nake miki ba, amma ba zaki samu miji da ke son ki tamkar yadda ya ke son ki ba.�

Intisar ta bita da hararar haushi, kar ta samu din, wannan dan iskan mijin nata? Yau kam kunya da tozarci tagama jin shi a rayuwar ta. Da wane ido zata dubi Faisal?

Wane kalami gareta na wanke kanta daga sunan mayaudariya, maciyiya amana, butulu kuma mai manta alkhairi a idon Faisal? Sai ta kara jin tsanar Al’ameen ninkin baninkin na da, dubi yadda yake wa matarshi don wai kurum tana sonshi. Itama idan ya aureta wata rana ya sami wadda ya fiso fiye da ita ba mamaki ya turota lallasar yarinyar da yake son, tab! In ita ce ai za’a yi kata’i. Bata san wannan duk yana cikin wayewar Ihsan da duniya ne ba, ko ba komi zata sayo ma kanta daraja da soyayya a zuciyar mijinta, gaskiyar Hajjo ne Ihsan da Aminu sun fita wayo, ba kuma tsaranta bane a budewar kai da Ilmi.

How much do you like this story?
5/14/22, 09:25 - Ummi Tandama😇: _____________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book three

*@Takori*

Page9ï¸âƒ£

A lokacin ne hankalin ta ya kai ga Hidayah da Hunainah wadanda ke hada komatsansu cikin ‘trollies� din su basa ko dubarta. Hankalinta ya tashi, ta ji babu dadi ta ce,

“Ku kuma ina za ku?�

In jakunkunan su sun amsa, to suma sun tsinka mata. Ta ja jiki ta sakko daga gadon fuskarta jike da hawaye taje ga Hidayah da Hunainah, ta kama kowacce da hannu daya ta rungume a jikinta ta cigaba da kuka mai tsuma rai su kansu basu san sanda hawaye ya cika idon su ba. Tace cikin kuka

“Don Allah ‘yan kanne na ba sai jibi zaku tafi ba?� Hidayah ta tureta tana share hawayen ta da bayan hannu.

“Ai zaman mu baya da amfani, tunda ke ba kya jin shawarar kowa kuma ba’ajin damuwarki. Yaya zaki sa Ya Aminu kuka akan idon matar sa?

Mu bazamu iya jurar ganin wannan wulakancin ba, so hauka ne? Kuma idan yanzu ba kya sonsa ba zaki aure shi ba ai ba haka ake abun da wulakanci ba.�

Ta ce, “Hidayah, Kome zan gaya miki a yanzu bazaki gane ba�. Baki san Babar Al’ameen ba ne�.� Ta katseta,

“Ba bu abinda na tambayeki, ban kuma ce ki gaya mun ba, ban santa ba ba kuma na so in santa, to amma ta yaya zaki hukunta shi da laifin uwar sa wanda ba nashi ba ai har ga Allah kin dau hakkin shi…� Ta ce,

“Hidayah, ba wannan ne kadai ba�.� sai kuma ta kara sa kuka, to tace mata me?

Bata da abinda zata ce da ita ta fahimta game da Faisal Bello Makarfi, daga Anti sai Daddy ne zasu fahimce ta akan hukuncinta amma su Hidayah baki ne basu san komi ba.

Dai-dai lokacin da Anti ta shigo tana rike da Zarah, tun kan ta zauna Zarah ke mikawa mutuniyar ta Hunainah hannu tana zillo daga jikin Antin, ta amsheta yayinda Antin ta samu gefen gado ta zauna ta dibesu dukkansu tace “duk mi ya janyo wannan?�

Hunainah ta ce,

“Tafiya zamu yi Anti� ta ce, “Ina?�

Su duka suka hada baki suka ce “Can inda aka sauki su Maman mu.� Ta ce,

“Akan me?� Duk suka yi shiru ta ce,

“Nasan sai jibi zaku tafi Korea, mun yi da Hajiya sai zasu tafi zasu biyo ku tafi, to a kan me yanzu zaku ce zaku tafi, ku bar ‘yar uwarku cikin irin wannan halin da ta jefa kanta don bana ce wani ya jefa ta ba.�

Hunainah ta ce, “To Aunty yaya zamuji dadin zama alhalin tana kuntatawa kanta? A ce mutum bashi da aiki sai kuka kamar wanda ya rasa iyaye da dangi, mu bamu da amfani a gareta kenan. Muna iya kokarin mu don kawo ma Saratu canjin rayuwa amma bata gani. Damuwar ta bamu isa mu ji ba, bamu san hakikanin kuma me ke damun ta ba. Ni ban ga meye abin bakin ciki duk a cikin maganar nan ba, tace ta fasa auren Yaya Al’ameen waye yace dole ta aure shi?

Sai kuma tasa mutane gaba tayi ta kuka in ta canja shawarane ba sai taje ta sameshi ta bashi hakuri ba?�

Ta share hawayenta da yatsunta biyu ta ja ‘tissue� ta fyace hanci ba tare da ta lura da hararar da Intisar din ta wurgo mata ba, dai-dai lokacin da Najib ya yi sallama ya shigo.

Da ganin yanayin da suke ciki duk ya bi ya rikice, ya zube a gabanta bai ma kula da Anti dake zaune ba ya ce,

“Hidayah, tafiya, why?� Sai ta sake barkewa da kuka.

Ya fiddo ‘handkerchief� a aljihun don share mata hawayen da ke zuba ya na tambayar su me ya faru? Aunty ta ce,

“Najib ya zan yi in san damuwan Saratu ne don Allah?�

Ya kai dubanshi ga Intisar, cikin kwanaki kalilan rak wai har tafi can baya sanda take cin bakar wuya lalacewa, yayi murmushi ya ce,

“Aunty, wait a minute� (jira ni minti daya).�

Ya juya ya fita da sassarfarshi, ya fi rabin awa kamin ya dawo Faisal na biye da shi. Idanun shi jazur da gani shi din ma yana cikin tsananin tashin hankali kwatankwacin koma fiye da na Intisar din, don dai shi namiji ne, sannan akwai juriya.

Kallon kyama kawai yake bin kowa da shi da tsanar duk wani al’amari dake cikin duniyar. Najib ya ce,

“Zauna� ya ce,

“Bana bukata.�

Ya tsaya kikam a bakin kofa ya harde hannuwanshi bisa kirji, idanunshi akan Inteesar tamkar mijin da ya kama matarshi da kwarto.

Najib ya zauna jikin Hidayarshi, cikin kwanciyar hankali ya dibi Anti cikin basira ya ce,

“Dibe su Anti.�

A mamakance Anti ta dubi Faisal, kana ta maida dubanta ga Intisar ya ce,

“Anti me kika fuskanta?� Ta ce,

“Dukkanin su, suna cikin yanayi daya.� Ya kuma cewa,

“Anti ba ki tuno can baya?� Cikin rashin fahimta ta ce,

“Ban gane ba�.

Ya bugi Jakar Hidayah da kafarsa ya ce,

“To cut the long story short! Na fahimci daga Faisal har Intisar suna son junansu ne tunda dadewa, duk wani da ya san kuruciyarsu zai gane hakan sai dai in baya da lura.

Na dade da sanin Intisar kishin Faisal take har zazzabi sai da nayi na kwana bakwai don mamaki. Intisar na cikin damuwar yaya zata bar Faisal akan Al’ameen? Ko da taso Al’ameen ta so shi ne a rashin Faisal, ta so shi ne domin ya mallaki wasu ‘qualities� da ‘appearances� na Faisal kaman murya, taku, da sauran su, yayin da Faisal ke jin haushin jinkirin shi na kin fara furtawa cewa…�

A fusace Faisal ya katse shi,

“Dakata don Allah Malam abin naka ya koma sharri, for God’s sake, yaushe na taba ce ma ina son Intessar, irin son da kake nufi? Yaushe ka zama predictor? Zuciyar wa ka shi ga a tsakanin mu har ka gano hakan?�

Najib ya dubeshi a lalace ya ce,

“To canzawa juna da kuka yi na mene ne?�

Kamin ya rufe bakinsa kawai sai suka ji Faisal ya ce,

“Hidayah zaki iya aurena?�

Hidayah ta dago a razane, ta girgiza kai da karfi tace “A’ah, wallahi ba ruwana, ni ina da wanda nake so kada a kara sani a ciki.�

Yadda ta fada da sauri da gigita saida ta ba Najib matsiyaciyar dariya, ya kuma ji nadamar abinda ya jangwalo ga abin na shirin juyewa kansa, shi ko Faisal wani dogon tsaki tsuuu� yaja ya juya ya fita har yana tuntube da dokin kofa.

Hunainah ta sunkuyar da kai cikin alhinin wannan cukurkudadden al’amari. Anti ta dubi Najib ta mike tsaye ta ce,

“Ni dai ina ganin Saratu ki sassautama ranki hakannan, Allah ya zaba abinda yafi alheri gaba daya.� In banda Najib ba wanda ya ce, “Amin.�

Ta fita ta ja masu kofa yayin da Najib ya cigaba dayi mata nasiha mai sanyaya rai. Ya ce,

“In da nine ke, Saratu ba kuma wani abu da zai sake sa ni bakin-ciki. Kamar yau ne nake gaya maki cikin wasikata sanda akai mana katanga dake cewa; ni na tabbata wani babban al’amari ne zai faru dake anan gaba, kuma hakika ke din wata ce a cikinmu.

Ga shi a yau kin zamo mabudi kuma sityari mai juya zuciyoyin ‘ya’yan Hajiya, sai inda ki ka garasu. Duba ki ga nima shakikiyarki bata barni ba. Kun zamo mana barin jiki, bango abin jinginar mu mu ji sanyi sai yadda kuka yi da mu. Don a yau Hidayah tace bata so na, ina jin haukacewa zanyi.

To haka daga Ya Aminu har Ya Faisal na tabbata babu mai tsira daga takobin kaunarki, duk da nasan Al’ameen bai san Faisal na sonki ba da duk matsalar ta warware.
Chapter 64 · 0% Book details