Sashe 81
Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Aunty Intisar sunan ki daga yau, kin yi mun abinda har abada bazan manta ba, me kike so in miki nima in faranta miki don Allah?� Ta ce,
“To aje ni in gaya miki, kada kirjin ki ya bude?� Ta dire ta tana dariya ta ce,
“Wallahi baki da nauyi, shafal kamar na dauki bokitin ruwa.� Ta bita da kallon mamaki ta ce,
“Hunainah, dama kina da karfi haka?� Ta juya mata baya cikin jin kunyar abinda ta yi, ita kanta bata san inda karfin nan ya fito ba, karfin soyayya kenan?
Ta dafa kafadarta ta ce, “Me ya faru ne sister, you look so happy than ever, whats the matter? (Da alama kina cikin, farin ciki fiye da koyaushe, me ya faru?) Ta juyo ta koma cikin nutsuwarta ta ce,
“Ke share kawai, nayi passing papers dina in ji Saajid Marwan (abokin karatun ta).� Ta san halin Intisar sarai, yanzu idan ta ji zancen nan sai kowa a gidan ya ji, tsiya kuwa da zasu yi mata ita da Hidaya, sai ta kasa kurbar ruwa a gidan don ta sha ce musu ba wanda ya isa ta bata muhimmin lokacin ta a kansa, sabida duk mazan mayaudara ne balle Hidaya da tayi saurin yarda da Najib bata ko tunanin karatun ta, gata nan har yau ta kasa komawa karatun, Najib sama- Najib-kasa bata da wani aiki sai nasa ga tsohon ciki tun bata cimma komi a rayuwa ba (a tunanin ta fa).
Intisar ta yi murmushi don ta sunsuno yar uwarta ta amma sai itama ta bagarar ta ce,
“Shine kuma sai ka ce yau kika fara cin jarrabawa, idiot� Ta sa hannu ta lakace mata hanci ta cigaba da kwabin da ta ke cikin mider, ta ce,
“Je ki daki ki cigaba da hirar ki da Saajid Marwan din naki, ko dai da shi zaa yi ne?�
Ta kyalkyale da dariya tace amman kin yanke ni, wannan abu dan kutuf ya kuttun tofa miyau? Ta ce,
“Yi a hankali dai ke mace ce, kada ki haifo irin sa ko wanda ya fi shi muni.�
Ta dubi yawan aikin da Intisar ta yi cikin dan lokaci tana can tana soyayya, ta jinjina kai ta ce,
“Amma ni a ganina Hajiyar su Najib ba karamin taimakon rayuwar ki tayi ba, tayi miki horo na ya mace, abinda kike yi ni ko rabin rabin sa bazan iya ba, ke ko cake wannan wallahi ganin wahalar in zauna in kwaba na ke.�
Ta yi murmushi ta ce,
“Nima na sha tunanin haka, in banda dukan da take mun da kebur, da shocking din da take jona mini kamar wata barauniya, da zagin da take mun na fitar hankali da ni da Anti Saratu, da gorin da take mun a kan son yayanta, wallahi da na gode mata.�
Hunainah ta fiddo ido ta ce, “Shocking fa kika ce? Ta girgiza kai cikin tuno tsohon bakin ciki ta ce,
“Shi fa, ke dai kawai a share, ban taba gayawa kowa ba ko Antina sai Alamin, na barwa raina, na barwa Allah ya saka min abinda matar nan ta wanzar da rayuwanta a yi mun, na barta da fitowar rana da faduwarta, na bar ta da duniya da abinda ke cikinta, na bar ta da Allah!�
Hawaye suka ciko idon ta, Hunainah ta ce, “Menene kebur? Ta ce,
“Wani siririn karfe ne da ake daure itace da shi, yafi bulala zafi, ya fi kututturen ice shiga jikin dan adam, kada Allah yasa a doke ki da shi Hunainah. Ta janye rigar ta sama ta nuna mata gadon bayan ta ta ce,
“Duba nan ki ga, wannan tabon har abada ba zai goge daga kafafuna da gadon baya na ba, kamar yadda har abada bazan yafe mata ba.�
Hunainah ta dubi zanen da ke gadon bayan ta wani a kan wani, sai dai yabi lafiyar jikin ta ya fara bacewa, ta share kwallar idon ta tace ido na idon matar nan Unh! Intisar ta yi murmushi ta ce,
“Kada ma ki fara wannan tunanin, don a yanzu ta zame maki dole, kakar dan ki da Hidayah zata Haifa, ni kuwa ta gama mun komi tunda ta haifa mun Alameen ta shayar da shi, ta so shi, ta kauna ce shi fiye da komai a rayuwar ta, ta haifa mun Faisal daya zamo ginshiki kuma tushen duk wani mataki da na taka a rayuwa.
Ya so ni, ya kaunace ni yayi duk iya kokarin sa wurin gina mun rayuwa mai inganci. Ina tabbatar miki duk wani hakilon Faisal na rayuwa domina ne, ni yake nemawa, bai damu da kansa ba tunda yana daga tsatson Hajiya, bana jin ko jikokin jikokin su zasu taba wahala a rayuwa.
Tana da arzikin da hankalin ki ba zai taba baki ba don haka ni yakema tanadin rayuwa amma ba shi ba. To don ta ki ni bata yi laifi ba, don ita zuciya an halicce ta da kishi a kan abinda ta ke so, ta na son yayan ta, su kuma suna so na, dole ta yi kishi dani.�
Hunainah ta yi ajiyar zuciya ta ce,
“Allah ya saka miki.�
Ta ce, “Wannan kawai itace magana Hunainah, A bar wa Allah ya fi a ja Yasin. Yanzu me ta isa ta yi mun a duniya sai dai in mata in kwana lafiya, to amma ba zan yin ba, ko gobe na gan ta durkusawa zan yi har kasa in gaishe ta, don na san Alameen ko a ina ya ga Mamata ba zai yi mata kallon banza ba, zai tsuguna da guiwoyin sa ya gaisheta cike da girmamawa. Ya gaya mun cewa kiyayyar da take min bata da dalili Allah ne ya daura mata, ba don kuma wani aibu na ta ke ki na ba, illa kawai ta samu kanta a mai ki na. Sai in fidda ta cikin masoyana in rungumi masu so na.
Bai yiwuwa mu samu soyyaya daga kowa don ko Annabin rahma Allah bai bar shi ba makiya ba. Kenan ya dace na yi mata uzuri. Uwa- uba tana auren mutuminda bani da kamar sa a duniya, tana auren Daddy Makarfi, da dadi ba dadi ta yi hakuri ta zauna da shi cikin kowanne hali. Ni kuma duk mai kaunar sa abin girmamawa ne a gareni.
Don haka a ranar da kika yiwa Babar Alameen rashn kunya, a ranar zan lakada miki dukan da baa taba yi miki ba!�
Ta rungumeta tana dariya ta ce, “Allah ya sauwake ki doke ni dukan haushi sai dai ki yi mini dukan kauna.�
Ta ce, “To ko ke fa?�
Cikin dan lokaci sun kammala aikin su mai ban shaawa, abinci kala-kala har kala bakwai Intisar ta shiryawa bakin ta da bata san ko su wanene ba, abin sha kala hudu, (snacks) kuwa baa maganar su kala-daban daban mai ban shaawa. Gabadaya abincin ta babu irin namu daga na Masar sai na Korea. Sai da kasusuwan bayanta suka amsa kas! Kana ta shiga wanka.
Ta dade tana gyaran fatar jikinta da mayuka masu gyara fata da sanya taushin fata, irin su aveeno E45 da norwegian formula kamin ta shirya cikin wani tattausan lesi (cotton) baki mai kananan duwarwatsu, ta killace gashin kanta cikin hair bound ta mulke siraran labbanta da lip-balm mai sanyin kamshi, ta kuma feshe jikin ta da turaren cKIn2U. Iyakacin kwaliyar ta kenan a kullum cool don ko kwalli bata damu da ta sanya ba sai Anti Saratu ta matsa mata.
Hunainah na gefen gado can a makure tana amsa waya cikin yar karamar murya don bata son Intisar din ta ji, da ganin yadda take kashe murya kasan da masoyin da a ke matukar so ake magana. Intisar ta yi biris da ita kaman bata san me take ba amma a ranta tayi dariya tayi har ta gaji.
Ta na zaune a gaban mudubin bata mike ba tana fesa turare wani dan yaro da bai fi shekaru biyu ba ya yane labulen dakin ya shigo yana zare kyawawan idanun shi alamun bakunta, yatsun shi biyu duka a baki yana tsotso, sanye yake cikin caftan na purple shadda rini me tsadar, kafar sa daure cikin farin kambas.
Da farko dai zuciyar ta ce tayi wani irin mummunan bugu kafin hawaye su biyo baya su bata mata kwalliyar fuskar ta, kirjin ta yana harbawa da sauri da sauri ta karasa ga yaron, ta zube ragwaf a gaban sa ta kama hannuwan shi da ke cikin bakin sa ta rungume shi sosai a kirjin ta, hawayen ta na zuba a gadon bayan sa.
Ganin babba tana kuka shima sai yasa kuka, ta yi saurin share idon ta tana dariya ta cira shi zuwa gefen gado ta zaunar da shi a kan cinyoyinta ta jawo jakar Hunainah da bata rabo da choculate ta dauko kit-kat ta bare ta bashi, ta ce,
Alameen Alameen Bello, suna na Aunty Intisar, ka na so na? Ya gyada mata ka kawai cikin halin ko in kula, ta ce wa ya kawo ka? Yace Uncle dina da Baba na.
To ai uncle din nashi da Babannin nashi suna da yawa, don haka bazata ce wanne ne ba wanne ne ba. Ta ce ka ga shi wancan Alameen din yana sona, yana yi mun murmushi, kaima kayi mun murmushi don Allah?
Gaba daya ya bude bakin yana yi mata dariya da kyawawan hakoran shi, beauty point din da cleave suka lotsa a tare, tayi saurin juyawa tana share hawaye.
Hunainah ta kashe wayarta ta dauki yaron a cinyar ta, itama kwalla ta cika idonta tace Allah da girma yake, Intisar ashe akwai irin wannan kama ta da da uban sa? Intisar ba baki, tace Alameen ka ga ka sa Aunty Intisar kuka, ka bata hakuri ya kai dan hannunshi ya shafo hawayen ta, ya sauka daga cinyar Hunainah da gudunsa yayi waje, a hausar shi wai Baban shi zai je ya nunawa Antin tana kuka.
Hidayah ce ta shigo Najib na biye da ita kaman jela, kafin ka ganta sai ka fara ganin tulelen cikin ta sabida girman sa, kafafunta sun kunbura haka ita kanta ta zama katuwa basu san sanda suka fashe da dariya ba. Ta juya cikin shagwaba, hannunta a ido tana kai karar su ga Najib. Ya ce,
“To aje ni in gaya miki, kada kirjin ki ya bude?� Ta dire ta tana dariya ta ce,
“Wallahi baki da nauyi, shafal kamar na dauki bokitin ruwa.� Ta bita da kallon mamaki ta ce,
“Hunainah, dama kina da karfi haka?� Ta juya mata baya cikin jin kunyar abinda ta yi, ita kanta bata san inda karfin nan ya fito ba, karfin soyayya kenan?
Ta dafa kafadarta ta ce, “Me ya faru ne sister, you look so happy than ever, whats the matter? (Da alama kina cikin, farin ciki fiye da koyaushe, me ya faru?) Ta juyo ta koma cikin nutsuwarta ta ce,
“Ke share kawai, nayi passing papers dina in ji Saajid Marwan (abokin karatun ta).� Ta san halin Intisar sarai, yanzu idan ta ji zancen nan sai kowa a gidan ya ji, tsiya kuwa da zasu yi mata ita da Hidaya, sai ta kasa kurbar ruwa a gidan don ta sha ce musu ba wanda ya isa ta bata muhimmin lokacin ta a kansa, sabida duk mazan mayaudara ne balle Hidaya da tayi saurin yarda da Najib bata ko tunanin karatun ta, gata nan har yau ta kasa komawa karatun, Najib sama- Najib-kasa bata da wani aiki sai nasa ga tsohon ciki tun bata cimma komi a rayuwa ba (a tunanin ta fa).
Intisar ta yi murmushi don ta sunsuno yar uwarta ta amma sai itama ta bagarar ta ce,
“Shine kuma sai ka ce yau kika fara cin jarrabawa, idiot� Ta sa hannu ta lakace mata hanci ta cigaba da kwabin da ta ke cikin mider, ta ce,
“Je ki daki ki cigaba da hirar ki da Saajid Marwan din naki, ko dai da shi zaa yi ne?�
Ta kyalkyale da dariya tace amman kin yanke ni, wannan abu dan kutuf ya kuttun tofa miyau? Ta ce,
“Yi a hankali dai ke mace ce, kada ki haifo irin sa ko wanda ya fi shi muni.�
Ta dubi yawan aikin da Intisar ta yi cikin dan lokaci tana can tana soyayya, ta jinjina kai ta ce,
“Amma ni a ganina Hajiyar su Najib ba karamin taimakon rayuwar ki tayi ba, tayi miki horo na ya mace, abinda kike yi ni ko rabin rabin sa bazan iya ba, ke ko cake wannan wallahi ganin wahalar in zauna in kwaba na ke.�
Ta yi murmushi ta ce,
“Nima na sha tunanin haka, in banda dukan da take mun da kebur, da shocking din da take jona mini kamar wata barauniya, da zagin da take mun na fitar hankali da ni da Anti Saratu, da gorin da take mun a kan son yayanta, wallahi da na gode mata.�
Hunainah ta fiddo ido ta ce, “Shocking fa kika ce? Ta girgiza kai cikin tuno tsohon bakin ciki ta ce,
“Shi fa, ke dai kawai a share, ban taba gayawa kowa ba ko Antina sai Alamin, na barwa raina, na barwa Allah ya saka min abinda matar nan ta wanzar da rayuwanta a yi mun, na barta da fitowar rana da faduwarta, na bar ta da duniya da abinda ke cikinta, na bar ta da Allah!�
Hawaye suka ciko idon ta, Hunainah ta ce, “Menene kebur? Ta ce,
“Wani siririn karfe ne da ake daure itace da shi, yafi bulala zafi, ya fi kututturen ice shiga jikin dan adam, kada Allah yasa a doke ki da shi Hunainah. Ta janye rigar ta sama ta nuna mata gadon bayan ta ta ce,
“Duba nan ki ga, wannan tabon har abada ba zai goge daga kafafuna da gadon baya na ba, kamar yadda har abada bazan yafe mata ba.�
Hunainah ta dubi zanen da ke gadon bayan ta wani a kan wani, sai dai yabi lafiyar jikin ta ya fara bacewa, ta share kwallar idon ta tace ido na idon matar nan Unh! Intisar ta yi murmushi ta ce,
“Kada ma ki fara wannan tunanin, don a yanzu ta zame maki dole, kakar dan ki da Hidayah zata Haifa, ni kuwa ta gama mun komi tunda ta haifa mun Alameen ta shayar da shi, ta so shi, ta kauna ce shi fiye da komai a rayuwar ta, ta haifa mun Faisal daya zamo ginshiki kuma tushen duk wani mataki da na taka a rayuwa.
Ya so ni, ya kaunace ni yayi duk iya kokarin sa wurin gina mun rayuwa mai inganci. Ina tabbatar miki duk wani hakilon Faisal na rayuwa domina ne, ni yake nemawa, bai damu da kansa ba tunda yana daga tsatson Hajiya, bana jin ko jikokin jikokin su zasu taba wahala a rayuwa.
Tana da arzikin da hankalin ki ba zai taba baki ba don haka ni yakema tanadin rayuwa amma ba shi ba. To don ta ki ni bata yi laifi ba, don ita zuciya an halicce ta da kishi a kan abinda ta ke so, ta na son yayan ta, su kuma suna so na, dole ta yi kishi dani.�
Hunainah ta yi ajiyar zuciya ta ce,
“Allah ya saka miki.�
Ta ce, “Wannan kawai itace magana Hunainah, A bar wa Allah ya fi a ja Yasin. Yanzu me ta isa ta yi mun a duniya sai dai in mata in kwana lafiya, to amma ba zan yin ba, ko gobe na gan ta durkusawa zan yi har kasa in gaishe ta, don na san Alameen ko a ina ya ga Mamata ba zai yi mata kallon banza ba, zai tsuguna da guiwoyin sa ya gaisheta cike da girmamawa. Ya gaya mun cewa kiyayyar da take min bata da dalili Allah ne ya daura mata, ba don kuma wani aibu na ta ke ki na ba, illa kawai ta samu kanta a mai ki na. Sai in fidda ta cikin masoyana in rungumi masu so na.
Bai yiwuwa mu samu soyyaya daga kowa don ko Annabin rahma Allah bai bar shi ba makiya ba. Kenan ya dace na yi mata uzuri. Uwa- uba tana auren mutuminda bani da kamar sa a duniya, tana auren Daddy Makarfi, da dadi ba dadi ta yi hakuri ta zauna da shi cikin kowanne hali. Ni kuma duk mai kaunar sa abin girmamawa ne a gareni.
Don haka a ranar da kika yiwa Babar Alameen rashn kunya, a ranar zan lakada miki dukan da baa taba yi miki ba!�
Ta rungumeta tana dariya ta ce, “Allah ya sauwake ki doke ni dukan haushi sai dai ki yi mini dukan kauna.�
Ta ce, “To ko ke fa?�
Cikin dan lokaci sun kammala aikin su mai ban shaawa, abinci kala-kala har kala bakwai Intisar ta shiryawa bakin ta da bata san ko su wanene ba, abin sha kala hudu, (snacks) kuwa baa maganar su kala-daban daban mai ban shaawa. Gabadaya abincin ta babu irin namu daga na Masar sai na Korea. Sai da kasusuwan bayanta suka amsa kas! Kana ta shiga wanka.
Ta dade tana gyaran fatar jikinta da mayuka masu gyara fata da sanya taushin fata, irin su aveeno E45 da norwegian formula kamin ta shirya cikin wani tattausan lesi (cotton) baki mai kananan duwarwatsu, ta killace gashin kanta cikin hair bound ta mulke siraran labbanta da lip-balm mai sanyin kamshi, ta kuma feshe jikin ta da turaren cKIn2U. Iyakacin kwaliyar ta kenan a kullum cool don ko kwalli bata damu da ta sanya ba sai Anti Saratu ta matsa mata.
Hunainah na gefen gado can a makure tana amsa waya cikin yar karamar murya don bata son Intisar din ta ji, da ganin yadda take kashe murya kasan da masoyin da a ke matukar so ake magana. Intisar ta yi biris da ita kaman bata san me take ba amma a ranta tayi dariya tayi har ta gaji.
Ta na zaune a gaban mudubin bata mike ba tana fesa turare wani dan yaro da bai fi shekaru biyu ba ya yane labulen dakin ya shigo yana zare kyawawan idanun shi alamun bakunta, yatsun shi biyu duka a baki yana tsotso, sanye yake cikin caftan na purple shadda rini me tsadar, kafar sa daure cikin farin kambas.
Da farko dai zuciyar ta ce tayi wani irin mummunan bugu kafin hawaye su biyo baya su bata mata kwalliyar fuskar ta, kirjin ta yana harbawa da sauri da sauri ta karasa ga yaron, ta zube ragwaf a gaban sa ta kama hannuwan shi da ke cikin bakin sa ta rungume shi sosai a kirjin ta, hawayen ta na zuba a gadon bayan sa.
Ganin babba tana kuka shima sai yasa kuka, ta yi saurin share idon ta tana dariya ta cira shi zuwa gefen gado ta zaunar da shi a kan cinyoyinta ta jawo jakar Hunainah da bata rabo da choculate ta dauko kit-kat ta bare ta bashi, ta ce,
Alameen Alameen Bello, suna na Aunty Intisar, ka na so na? Ya gyada mata ka kawai cikin halin ko in kula, ta ce wa ya kawo ka? Yace Uncle dina da Baba na.
To ai uncle din nashi da Babannin nashi suna da yawa, don haka bazata ce wanne ne ba wanne ne ba. Ta ce ka ga shi wancan Alameen din yana sona, yana yi mun murmushi, kaima kayi mun murmushi don Allah?
Gaba daya ya bude bakin yana yi mata dariya da kyawawan hakoran shi, beauty point din da cleave suka lotsa a tare, tayi saurin juyawa tana share hawaye.
Hunainah ta kashe wayarta ta dauki yaron a cinyar ta, itama kwalla ta cika idonta tace Allah da girma yake, Intisar ashe akwai irin wannan kama ta da da uban sa? Intisar ba baki, tace Alameen ka ga ka sa Aunty Intisar kuka, ka bata hakuri ya kai dan hannunshi ya shafo hawayen ta, ya sauka daga cinyar Hunainah da gudunsa yayi waje, a hausar shi wai Baban shi zai je ya nunawa Antin tana kuka.
Hidayah ce ta shigo Najib na biye da ita kaman jela, kafin ka ganta sai ka fara ganin tulelen cikin ta sabida girman sa, kafafunta sun kunbura haka ita kanta ta zama katuwa basu san sanda suka fashe da dariya ba. Ta juya cikin shagwaba, hannunta a ido tana kai karar su ga Najib. Ya ce,