Sashe 58
Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
So nake bandakin nan ya fiki fari, ya kuma fi Faisal di na kamshi� Faisal ne ya sa miki suna Intisar, kuma da na ne, mallakina ne, don haka daga yau na kwace�. Ke Jikar Jummai ce, Jummai uwar Saratu�. Daga yau kika sake koda kallar min ‘ya’ya, sai na sa wuka na tsokale wadanna makafin idanun munafurcin, kina jina? Ta tuna amsar da ta baiwa Hajiyar a lokacin. A yau ma sai ta samu kanta da nanata su, sai dai sabanin sunayen da ta kira a wancen lokacin a yau cewa tayi…ba Faisal ba, ba Aminu ba� duk wani jininki ma idan na sake daga ido na dubeshi ba da kiyayya ba, ki ce ni shegiya ce na amince!
Ta kudurce a ranta daga yau dukkansu ko gaisuwar dayansu bata so. Aure kuma in har sai da ‘ya’yan Haj. Nafi ne, to ita Saratu ta yafe!
Ba irin bugun da su Hunainah da Anti ba suyi ba amma Intisar bata bude ba. Wuni tayi cin kuka da nadama mara amfani. Ta rasa meyasa rayuwar ta ke da matsaloli iri-iri tun tana jaririyarta. Dagabaya kuma tayi tunanin akan me zata bari soyayyar ‘ya’yan Hajiya ya wargaza mata rayuwa? Komi fa mutum ke daurama kansa don Allah baya daurawa rai sai abinda zata iya.
Ta yankewa kanta ‘solution� na karshe tayi murmushi ita kadai. Ta san cikin Iyayenta kakaf, babu mai matsa mata akan wannan kudurin nata. Sai ko Mamarsu Hunainah ita ko bata jin ta don ta tabbata Daddynta zai bata goyon baya dari bisa dari.
Ba ita ta fito ba sai karfe hudu na yamma, shi din ma azababbiyar yunwa ta fiddota. Su Hunainah na magana da Anti Hajjo a waya ta ce,
“Gata nan ma ta fito� ta mika mata wayan ta ce,
‘Hello Aunty� Hajjo ta ce,
“Ba wani Yello Aunty, nikan baki dauke ni Antin ba, da ko menene ke damunki da kin kira ni kin gaya mini, Saratu shin me yayi zafi ne haka? Na ji an ce tun safe kin rufe kanki a daki kina kuka.
Na dauka kasancewar mu kusa da ke, da tabbacin da kike da shi na iyayen kwarai ya isa ya sanyaya maki zuciya? Wannan kuntata duk na menene?�
Tayi shiru, Idanuwan ta sunyi rau-rau kaman ta saki kuka. In da Anti Hajjo ta san yadda take jin zuciyar nan tata, da bata zargeta da kuntatawa kanta ba.
Ita ba sauyin Iyaye ya dameta ba, damuwarta daban ne, daga ita sai Ubangijin ta suka santa. Hajjo ta ce,
“Koda bakya kaunar mu Saratu, mu ne dai iyayenki, kuma ba’a sake iyaye sai iyayen daki. Wannan rashin sakin jikin da kike damu ban sani ba ko don ki na ganin bamu isa mu zamo iyayen ki ne ba?� (Aunty Saratu ce ta koya mata, ba’a jin damuwan ta sai da dabara) Ta sa kuka da karfi tace “Aunty Hajjo me ya kawo wannan maganar?
Na rantse da Allah ba haka bane, ni abinda ke damuna daban ne.�
Hajjo ta ce, “Don kin ce kin fasa auren Al’ameen? Ke, yarinyar ki da ke kar ki bari ciwon hawan jini ya kamaki akan soyayya. Shi Al’ameen din yace dake ya damu? Yana can tare da matarshi Allah kadai yasan farin-cikin da suke ciki sai ke ki bi ki kuntatawa ranki?�
Ta share hawayen da ke zuba mata da bayan hannu, dai-dai sanda dan halak din ya yiwa falon tsinke, matarsa na biye da shi tamkar ta shige jikinshi don tsatsiba, ya zarce kai tsaye har inda take, ya ja tebur inda take ya daura kafa daya, dayar kuwa na kasa tamkar mai son jin kwakkwafin abinda ke sata kuka a waya.
Ihsan ta bisu da kallo kana tabi bayan su Hunainah da sukayi cikin dakin Anti. Intisar ta bude baki domin ta bawa Antinta amsar da tai niyya amma kwarjinin Al’ameen ya katse komi. So ta ke tace har wata tsiyace Al’ameen din da zata kuntatawa kanta akansa? Ita ba shine damuwanta ba.
Hajjo ta ji tayi shiru ta cigaba da cewa, “Ni dai shawarata a gareki Intisar, ki fidda damuwar komi a ranki, ki koma makaranta. A shirye muke damu nuna maki kauna ta kowanne fanni. Na san kina son Al’ameen, so bana wasa ba. Tunda har kika kusa salwantar da rayuwar ki akan tunanin bazaku iya auren juna ba.
Amma abinda na ke so ki gane shine, ki yi tunani, ke yarinya ce karama har yanzu cikin shekarun (teenage), wannan gigin son duk na dan lokaci ne, da anyi auren an haihu shikenan ya zama tarihi sai zaman hakuri da juna.
Abinda nake so da ke shine ki tsaya ki gina rayuwarki a bisa tubala na kwarai, in ba hakaba ba mamaki bada jimawa ba soyayya ta ruguzata. Al’ameen ya fiki wayo, daga shi har matarshi ba tsaranki bane a budewar kai da ilmi.
Don haka ki tsaya ki nemawa kanki madogara mai kyau tukunna, wanda shine wannan ilimin mai matukar wuya. Idan kika sameshi samun Aminu ba zai maki wuya ba haka in kika barshi ke da banza a cikin su daya kuke, don sai kin raina kan ki a cikinsu.
Ni in son raina ne ma Allah bana son ki auri mai mata irin Ihsan, ki dubi yadda take hauka akan mijinta fa, ke ‘yar nan, mind yourself (ki shiga taitayinki)�. Ahaf! Ai kamar Antin ta shiga ranta taga abinda take shiri komawa makaranta, tayi murmushi tare da saurin rufe ido, maganganun Antin take aunawa abisa sikeli daya bayan daya, wanda dama duk tayi tunaninsu, babu wanda bata ga gaskiya a ciki ba, ta ce a raunane.
“Na gode Aunty.�
Ta rufe wayar, sai yanzu ya fuskanci da wa take magana, bata ko dubeshi ba ta murda kofar da zata hadaka da dakin ta daga falon Anti, yayi hamzarin murda keys ya zare ya tura aljihun bayan wandon ‘basachi� dake jikinsa ya ce.
“Me Anti Hajjo ke gaya maki a waya, kike godewa kina kuma kara yi mun asaran hawayen da nake ganin daraja da kimar su fiye da na kowa?�
Wasu ubansu harara da ta watso mai ya bashi mamaki don bai taba ganin tayi ba, ga idanun sunyi jawur sai ta kara kyau a idon shi, ko da yake so ne hana ganin aibi, ya ce, “Inteesar� da muryar nan da ke karya lagonta, ta kassara kuzarin ta, amma a yau ko gezau, har yanzu hararar shi ta ke ba kakkautawa.
Ya soma taki har inda take tsaye tamkar sassakakken gunki, ta soma ja da baya kamar wadda taga abin tsoro da kyama, ta san ba karamin aikin shi ba ne ya kamata da kokawa kawai don ya sata yin magana, cikin tsiwa da yatsina ta bude dan bakinta tana mai nunashi da dan manuninta ta ce,
“Wallahi Al’ameen ka sake ka tabani yau zan fasa ma kaine, in bar inyamurar matarka da jiyyar da baka taba yi ba.� Bai fasa dosarta ba ya ce,
“Jinya kuma wacce ce ba’ayi ba? Sai dai kar a kuma, idan jinya ta ciwon son halimah ce, to ayi ta yi kar a tashi. Kar ki kara kira mun mata inyamura, yadda kike musulma diyar musulmi, haka itama take.� dai-dai lokacin da ta dangana da bangon karshe na falon, shi kuma bai fasa bin ta ba, ta ce,
“Wallahi zan kirawo Anti, tayi ma kashedin shiga harkana, ka nemo Halimar ka can amma ni Intisar ce, ka manta ka taba sanina a rayuwarka, ina gaya maka, ina kara gaya maka� ya toshe mata baki. Ya ja hannunta na dama da karfi har bisa seater dake tsakiyar falon, ta karfin tsiya ya zaunarta ya ce,
“Ke in ma Daddy zaki kirawo babu laifi. Amma sai na gama maganar da zan yi. Kin san me ya kawo ni?
Zuwa nayi in gaya maki ranar da duk wannan maganannen bakin ya kara kuskuren cewa bazai aureni ba don uwata, wallahi sai na kakkarya ki.�
Cikin tsiwar da bai san ta iya ba ta ce,
‘Ka karya ni? To ka ji ka sani ko da can da ka makantani, don ban da wayo ne, amma yanzu wallahi sai dai ayi ‘yar bibbiyu� saura kadan da dariya ta kwace masa, to amma shi kansa yasan bai kyauta ba, jiya ya mareta yau ya gaya mata kakkausar magana, shi da ke neman wanke dattin da Hajiya ta yayyaba masu daga idanunta.
Ya dire gwiwoyinsa bisa carpet abinda bai taba yiwa wata ‘ya mace a rayuwarsa ba, a yayinda ita kuma take zaune cikin kujera ta cika fam, kiris take jira ta fashe.
Ya langabe kai gefe guda gwanin ban tausayi, yayi kamar ya share mata hawayen da suka soma surtu, sai kuma yafasa. Ya ce,
“Inteesarr!�
Yadda ya kira sunan cikin murya mai karkarwa da kauri (husky) kadai ya birkita Saratun, bata jin ko dan yatsanta zata iya motsawa. Ya ce,
“I ‘am sorry, terribly sorry! Wallahi ni, wasa nake maki, in karya ki in ce na karya wa kenan?
Jiya kuma zuciya ce ta debe ni, kin san bata da kashi, abinda kika fadi cikin mutane ya bata mun kwarai. Ni kaina ban san ya akai ba, Pls, 4 give me…� Ya karasa a raunane, kana ya matso ‘yar kwallah, ya maida ta bisa kujerar ya ce,
“Wallahi Intisar nasan Hajiya ta bata miki, to amma ni meye laifina? Ni ban ji tsoron abinda hakan zai janyo man ba daga gareta na furta ina sonki? Sannan kuma bakya tausaya mun halinda zan shiga in na rasa ki kwata-kwata, ki tuna baya?�
Ta sadda kai kawai, bata son jin wannan abun da take ji game da Aminu, bata son wadannan ‘feelings� din da take ji game da shi masu tada tsigogin jikinta a duk lokacin da suke tare, to amma Al’ameen din kamar wani mayen karfe ne, wuyarta yayi mata magana da wannan muryan nashi mai jan mutum uwa lantarki duk wani ‘weakness� din ta ya gama samunshi.
Ta tabbata nisa da shi shine abu mafi a’ala a gareta in har tana son cimma kudurirrikanta akan Haj. Nafi, wadanda daga ita sai zuciyarta sai mahaliccinta suka san na mene, amma ba don bata son shi ba.
Ta kudurce a ranta daga yau dukkansu ko gaisuwar dayansu bata so. Aure kuma in har sai da ‘ya’yan Haj. Nafi ne, to ita Saratu ta yafe!
Ba irin bugun da su Hunainah da Anti ba suyi ba amma Intisar bata bude ba. Wuni tayi cin kuka da nadama mara amfani. Ta rasa meyasa rayuwar ta ke da matsaloli iri-iri tun tana jaririyarta. Dagabaya kuma tayi tunanin akan me zata bari soyayyar ‘ya’yan Hajiya ya wargaza mata rayuwa? Komi fa mutum ke daurama kansa don Allah baya daurawa rai sai abinda zata iya.
Ta yankewa kanta ‘solution� na karshe tayi murmushi ita kadai. Ta san cikin Iyayenta kakaf, babu mai matsa mata akan wannan kudurin nata. Sai ko Mamarsu Hunainah ita ko bata jin ta don ta tabbata Daddynta zai bata goyon baya dari bisa dari.
Ba ita ta fito ba sai karfe hudu na yamma, shi din ma azababbiyar yunwa ta fiddota. Su Hunainah na magana da Anti Hajjo a waya ta ce,
“Gata nan ma ta fito� ta mika mata wayan ta ce,
‘Hello Aunty� Hajjo ta ce,
“Ba wani Yello Aunty, nikan baki dauke ni Antin ba, da ko menene ke damunki da kin kira ni kin gaya mini, Saratu shin me yayi zafi ne haka? Na ji an ce tun safe kin rufe kanki a daki kina kuka.
Na dauka kasancewar mu kusa da ke, da tabbacin da kike da shi na iyayen kwarai ya isa ya sanyaya maki zuciya? Wannan kuntata duk na menene?�
Tayi shiru, Idanuwan ta sunyi rau-rau kaman ta saki kuka. In da Anti Hajjo ta san yadda take jin zuciyar nan tata, da bata zargeta da kuntatawa kanta ba.
Ita ba sauyin Iyaye ya dameta ba, damuwarta daban ne, daga ita sai Ubangijin ta suka santa. Hajjo ta ce,
“Koda bakya kaunar mu Saratu, mu ne dai iyayenki, kuma ba’a sake iyaye sai iyayen daki. Wannan rashin sakin jikin da kike damu ban sani ba ko don ki na ganin bamu isa mu zamo iyayen ki ne ba?� (Aunty Saratu ce ta koya mata, ba’a jin damuwan ta sai da dabara) Ta sa kuka da karfi tace “Aunty Hajjo me ya kawo wannan maganar?
Na rantse da Allah ba haka bane, ni abinda ke damuna daban ne.�
Hajjo ta ce, “Don kin ce kin fasa auren Al’ameen? Ke, yarinyar ki da ke kar ki bari ciwon hawan jini ya kamaki akan soyayya. Shi Al’ameen din yace dake ya damu? Yana can tare da matarshi Allah kadai yasan farin-cikin da suke ciki sai ke ki bi ki kuntatawa ranki?�
Ta share hawayen da ke zuba mata da bayan hannu, dai-dai sanda dan halak din ya yiwa falon tsinke, matarsa na biye da shi tamkar ta shige jikinshi don tsatsiba, ya zarce kai tsaye har inda take, ya ja tebur inda take ya daura kafa daya, dayar kuwa na kasa tamkar mai son jin kwakkwafin abinda ke sata kuka a waya.
Ihsan ta bisu da kallo kana tabi bayan su Hunainah da sukayi cikin dakin Anti. Intisar ta bude baki domin ta bawa Antinta amsar da tai niyya amma kwarjinin Al’ameen ya katse komi. So ta ke tace har wata tsiyace Al’ameen din da zata kuntatawa kanta akansa? Ita ba shine damuwanta ba.
Hajjo ta ji tayi shiru ta cigaba da cewa, “Ni dai shawarata a gareki Intisar, ki fidda damuwar komi a ranki, ki koma makaranta. A shirye muke damu nuna maki kauna ta kowanne fanni. Na san kina son Al’ameen, so bana wasa ba. Tunda har kika kusa salwantar da rayuwar ki akan tunanin bazaku iya auren juna ba.
Amma abinda na ke so ki gane shine, ki yi tunani, ke yarinya ce karama har yanzu cikin shekarun (teenage), wannan gigin son duk na dan lokaci ne, da anyi auren an haihu shikenan ya zama tarihi sai zaman hakuri da juna.
Abinda nake so da ke shine ki tsaya ki gina rayuwarki a bisa tubala na kwarai, in ba hakaba ba mamaki bada jimawa ba soyayya ta ruguzata. Al’ameen ya fiki wayo, daga shi har matarshi ba tsaranki bane a budewar kai da ilmi.
Don haka ki tsaya ki nemawa kanki madogara mai kyau tukunna, wanda shine wannan ilimin mai matukar wuya. Idan kika sameshi samun Aminu ba zai maki wuya ba haka in kika barshi ke da banza a cikin su daya kuke, don sai kin raina kan ki a cikinsu.
Ni in son raina ne ma Allah bana son ki auri mai mata irin Ihsan, ki dubi yadda take hauka akan mijinta fa, ke ‘yar nan, mind yourself (ki shiga taitayinki)�. Ahaf! Ai kamar Antin ta shiga ranta taga abinda take shiri komawa makaranta, tayi murmushi tare da saurin rufe ido, maganganun Antin take aunawa abisa sikeli daya bayan daya, wanda dama duk tayi tunaninsu, babu wanda bata ga gaskiya a ciki ba, ta ce a raunane.
“Na gode Aunty.�
Ta rufe wayar, sai yanzu ya fuskanci da wa take magana, bata ko dubeshi ba ta murda kofar da zata hadaka da dakin ta daga falon Anti, yayi hamzarin murda keys ya zare ya tura aljihun bayan wandon ‘basachi� dake jikinsa ya ce.
“Me Anti Hajjo ke gaya maki a waya, kike godewa kina kuma kara yi mun asaran hawayen da nake ganin daraja da kimar su fiye da na kowa?�
Wasu ubansu harara da ta watso mai ya bashi mamaki don bai taba ganin tayi ba, ga idanun sunyi jawur sai ta kara kyau a idon shi, ko da yake so ne hana ganin aibi, ya ce, “Inteesar� da muryar nan da ke karya lagonta, ta kassara kuzarin ta, amma a yau ko gezau, har yanzu hararar shi ta ke ba kakkautawa.
Ya soma taki har inda take tsaye tamkar sassakakken gunki, ta soma ja da baya kamar wadda taga abin tsoro da kyama, ta san ba karamin aikin shi ba ne ya kamata da kokawa kawai don ya sata yin magana, cikin tsiwa da yatsina ta bude dan bakinta tana mai nunashi da dan manuninta ta ce,
“Wallahi Al’ameen ka sake ka tabani yau zan fasa ma kaine, in bar inyamurar matarka da jiyyar da baka taba yi ba.� Bai fasa dosarta ba ya ce,
“Jinya kuma wacce ce ba’ayi ba? Sai dai kar a kuma, idan jinya ta ciwon son halimah ce, to ayi ta yi kar a tashi. Kar ki kara kira mun mata inyamura, yadda kike musulma diyar musulmi, haka itama take.� dai-dai lokacin da ta dangana da bangon karshe na falon, shi kuma bai fasa bin ta ba, ta ce,
“Wallahi zan kirawo Anti, tayi ma kashedin shiga harkana, ka nemo Halimar ka can amma ni Intisar ce, ka manta ka taba sanina a rayuwarka, ina gaya maka, ina kara gaya maka� ya toshe mata baki. Ya ja hannunta na dama da karfi har bisa seater dake tsakiyar falon, ta karfin tsiya ya zaunarta ya ce,
“Ke in ma Daddy zaki kirawo babu laifi. Amma sai na gama maganar da zan yi. Kin san me ya kawo ni?
Zuwa nayi in gaya maki ranar da duk wannan maganannen bakin ya kara kuskuren cewa bazai aureni ba don uwata, wallahi sai na kakkarya ki.�
Cikin tsiwar da bai san ta iya ba ta ce,
‘Ka karya ni? To ka ji ka sani ko da can da ka makantani, don ban da wayo ne, amma yanzu wallahi sai dai ayi ‘yar bibbiyu� saura kadan da dariya ta kwace masa, to amma shi kansa yasan bai kyauta ba, jiya ya mareta yau ya gaya mata kakkausar magana, shi da ke neman wanke dattin da Hajiya ta yayyaba masu daga idanunta.
Ya dire gwiwoyinsa bisa carpet abinda bai taba yiwa wata ‘ya mace a rayuwarsa ba, a yayinda ita kuma take zaune cikin kujera ta cika fam, kiris take jira ta fashe.
Ya langabe kai gefe guda gwanin ban tausayi, yayi kamar ya share mata hawayen da suka soma surtu, sai kuma yafasa. Ya ce,
“Inteesarr!�
Yadda ya kira sunan cikin murya mai karkarwa da kauri (husky) kadai ya birkita Saratun, bata jin ko dan yatsanta zata iya motsawa. Ya ce,
“I ‘am sorry, terribly sorry! Wallahi ni, wasa nake maki, in karya ki in ce na karya wa kenan?
Jiya kuma zuciya ce ta debe ni, kin san bata da kashi, abinda kika fadi cikin mutane ya bata mun kwarai. Ni kaina ban san ya akai ba, Pls, 4 give me…� Ya karasa a raunane, kana ya matso ‘yar kwallah, ya maida ta bisa kujerar ya ce,
“Wallahi Intisar nasan Hajiya ta bata miki, to amma ni meye laifina? Ni ban ji tsoron abinda hakan zai janyo man ba daga gareta na furta ina sonki? Sannan kuma bakya tausaya mun halinda zan shiga in na rasa ki kwata-kwata, ki tuna baya?�
Ta sadda kai kawai, bata son jin wannan abun da take ji game da Aminu, bata son wadannan ‘feelings� din da take ji game da shi masu tada tsigogin jikinta a duk lokacin da suke tare, to amma Al’ameen din kamar wani mayen karfe ne, wuyarta yayi mata magana da wannan muryan nashi mai jan mutum uwa lantarki duk wani ‘weakness� din ta ya gama samunshi.
Ta tabbata nisa da shi shine abu mafi a’ala a gareta in har tana son cimma kudurirrikanta akan Haj. Nafi, wadanda daga ita sai zuciyarta sai mahaliccinta suka san na mene, amma ba don bata son shi ba.