Sashe 23
Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Komai yake yi yana yi ne don farin cikin Hajiya, don Hajiyar shi ta ji dadi, domin ta ce da shi ba irin wulakanci da tozarcin da Daddy bai mata ba a kan Intisar lokacin yana makarantar kwana shi yasa shi ma ya tsane ta, don komai yake so ita ma Hajiyar naso, komai yake so ta na yi masa, ko damuwa ya shiga Hajiya ba ta kuma samun kwanciyar hankali ba kuma za ta huta ba sai ta ga ta gusar masa da wannan damuwar.
Abu daya ne har zuwa yanzun ta ki mara masa baya wato ra’ayin shi na son tafiya karatu Miami (Miami gari ne na ‘yan hutu cikin U.S.A) don tana ganin duk cikin ‘ya’yanta ya fi sonta, ya fi su kaunar ta, ya fi kaunar abin da take so. Idan ya tafi wa zai taya ta kiyayyar su Saratu?
Tsaye yake jikin Volvos 6 din Hajiyar shi, yana ta faman murza ‘yar karamar kwamfutar aljihu pocket computer, sanye yake cikin Kaftani na wata jikakkiyar shadda-rini ‘yar Mali. Sai ga Intisar da Khalil tana rungume da ribdediyar teddin ta, daga inda yake tsaye yana iya jiyo muryar Khalil na cewa, “Baby ki je ki kwantar da ita a karkashin mota zan je in dauko mata filon ta.�
Ya juya ya koma cikin gida yayin da ita kuma ta nufi karkashin motar da Al’ameen ke tsaye ba tare da ta lura da shi ba, domin ya ba su baya ne. Sojojin da ke gadi a harabar gidan ba wanda ya ba su hankalin shi kasancewar sun riga sun saba wasansu a wurin kullum ta Allah.
Ta sunkuya za ta shimfide teddin kenan, sai ya sa kafa iya karfin shi ya yi (bull) da ita, ta hantsila ta wulwula har sau uku, kafin idanunta da goshinta su hadu da wani karfen pipe ta gigice ta dimauce ta saki wata irin razananniyar kara da amsa kuwwar ta ya ratsa illahirin gidan, gaba daya ma’aikatan gidan har shi Aminun suka yi kanta a guje.
Jikinsa ya yi sanyi da ganin jini na gudu daga idanun yarinyar hade da wani irin ruwa. Ya saki Computer da ke hanun shi ya dauke ta a gigice yana.
‘Emma bude mini mota, wayyo Allah na shiga uku! Na yi kisan kai!�
Abin da yake ta nanatawa kenan, har suka isa asibiti. Mummunan labarin ya riski Aunty Saratu ne tana cin abinci, ta saki cokalin ta ce, ‘Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un�.� Don Khalil da ke bayar da labarin cewa ya yi idanun Baby sun tsiyaye.
Shi kan shi Daddy jikin shi babu inda baya rawa, da kyar ya kulle Aunty Saratu yabi bayan su saboda yadda ta fita daga hayyacinta cewa kawai take, ‘Yanzu baby shi kenan idon ki ya tsiyaye?�
Likitocin ido kwararru uku ne a kan Intisar suna kokarin ceton ‘eye-bulls� dinta (kwayar idonta). Sai bayan awanni uku babban likitan ya nemi ganin Daddyn a ofis din shi, ya fara da kwantar masa da hankali, don ganin yadda duk ya fidda rai ya kuma ba shi shawarar a kai baby asibitin kwararrun ido na Kaduna, in an yi sa’a a ceci lafiyar idonta, amma he’s sorry to say, ko da Saratu ta warke ba za ta ci gaba da gani da naked-eyes dinta ba.
Inda duk hankalin Daddy yake in ya yi dubu to ya tashi, bai tausayin Baby kamar Aunty Saratu, da ta ci duk wani buri da fatan ta a kan Inteesar! Amman a yau a ce ta makance! Duk kwazon ta, duk himmar ta da ke sawa ana yi mata hangen zama wani abu a gaba. Bai san san da wasu zafafan hawaye suka shiga yi masa lugulgude a fuska ba tamkar ba Brigadier na soja ba.
Yasa habar babbar rigar a ya share kafin ya sa hannu a tura su Kadunan.
A jirgin (bell-view) da suke ciki, Aminu Bello, tafukansa yasa ya rufe kyakkyawar fuskarsa. Ya sha jin Malamin su na Islamiyya na cewa, ‘Ku roki Allah ya kare ku daga nadama mara amfani.�
Bai taba sanin mene ne nadama mara amfani ba sai yau. Tausayin mahaifin su kadai ya ishe shi na wahalar da ya jawo masa. Ya san Daddyn na son shi, amma a yau yana shakkar, idan son da Daddy ke wa Inteesar diyar Aunty Amarya bai dame wanda Daddyn ke masa ba.
A asibitin Kadunar ma sun ce ne idan Daddyn na da hali to ya gaggauta fitar da diyar sa asibitin kwararrun ido da ke Jiddah, nan suka bar Intisar karkashin matsananciyar kulawar likitoci su suka tafi neman visa. Masu abu da abin su nan da nan suka samu. Karfe tara na dare an shigar da Baby tiyatar ido.
Mu karasa a littafi na biyu.
Taku
Takori
How much do you like this story?
5/7/22, 13:10 - Ummi Tandama😇: ____________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book two
*@Takori*
Page1ï¸âƒ£
Ameenu kishingide cikin lallausar kujerar asibitin Saudi-German, nadama goma da ashirin ji yake kamar ya farkewa Daddyn shi komai, in ya so ya nemi gafarar shi, ko ya samu saukin wannan dumbin hakki da ya dauka na rayukan al’umma da dama, na kuma yarinyar da ba ta ji ba ba ta gani ba, ba ta kuma tsare masa komai a rayuwa ba.
Lokaci daya ya ji ya tsani kan sa kai da duk ‘ya’ya masu irin halin shi na taya iyayensu mata kishi. Amma tsoron hukuncin da Daddyn zai dauka a kan shi ya hana shi, gani yake kamar ma ya san shi ne sanadiyyar shigar diyar shi cikin wannan azaba shiru kawai ya yi masa, watakila ma kuma idan ya fada masa shi din ne ya tsane shi, hakan kuma ya yi sanadiyyar jawo masa bacin ran Hajiyar shi.
Ya yi tunani iyaka tunani, ya rasa mafita cikin al’amarinsa, tunda kuwa ya zama fitina kenan ga iyayen shi? Daga karshe ya yanke abinda yake ganin shi ne mafi dacewa a gareshi shi ne ya bar su kwata-kwata ya fita daga tsakanin su, ya yi nisa da rayuwar su, ya bar masu kasar baki daya ya je ya ginawa kansa sabuwar rayuwa mai amfani. Me ye amfanin ‘ya’ya irin sa masu sanya iyayensu cikin halin ha’u’la’i? Babu.
Kada ma ya je Hajiya ta angiza shi ga kisan kai, don ma abin ya zo da sauki? Da ta mutu fa me zai ce da Ubangijinsa? A kan wani kishin su na mata wanda shi bai shafe shi ba.
Tunaninikan da yake ta yi kenan har aka fiddo Intisar daga dakin tiyatar da karfe biyu da rabi na sulusin dare agogon su na can. Ya tsaya a kan ta yana ta muzurai ganin yadda aka nannade dukkan idanunta da bandeji, jikinsa ya saki gaba daya.
Washe gari likita Doctor Khair ya tabbatar wa Daddy Saratu za ta gani da taimakon medical glasses kanana da za su yi mata. Bayan sati biyu da yin aikin aka cire bandejin da addu’o’i na musamman a bakunansu don Daddy har Dawafi na musamman ya yi a kan lafiyar Intisar kadai.
To Alhamdulillahi Saratu na gani daga kusa-kusa, sai dai ba ta iya gane abin da ke nesa da ita tangaran abinda a turance suke kira short eye-sight.
A ranar Dr. Khair ya manna mata farin siririn medical glasses tamkar gidan biro don siranta garai-garai da shi kamar na ado, wallahi kada ki so ki ga yadda ya karawa yarinyar nan wani irin kyau da kwarjini, da aka sa mata sai ta kama dariya.
Daddy ya kashe kudi ba kadan ba, amma wannan ba shi ne damuwarsa ba shi dai burinsa kada a ce Saratu ta rasa ganin ta kwata-kwata. Don haka da ya tabbatar tana gani tar da gilashin in an cire ne take gani dusu-dusu sai ya gode Allah.
A ranar da suka cika sati na biyar suka dawo. Anti Saratu duk ta rame ta yi duhu saboda zullumi. A guje Intisar ta rungume Mamarta suka shiga juyi a tsakar gidan har suka bai wa kowa da ke wajen tausayi.
Tana gaya mata labarin Daddy ya saya mata gilas mai kyau, za ta ke ba ta aro tana danawa, yaya Aminu yana ba ta abinci a baki baya tsula mata carbi a unguwar da suka je. Yayin da Ameenun ya yi tsaye harde da hannunsa bisa kirji yana kallon su cike da jin nauyi ko kadan bai bari sun hada idanu da Antin ba, tunda suka dawo. Antin ta dube si ta watsar ta ce, ‘Al’ameen kenan. Kai ma sannu da kokari.�
Yanayin yadda ta fadi maganar cikin gatse, dole ta sa shi ya yi murmushin dole har cleft din ya lotsa, ya kuma sha jinin jikin sa, ji yake kamar ya ce da kasar ta tsage ya shige, ji yake kamar Anti Saratu ta san shi ne sanadiyyar nakasar diyar ta.
Haka kurum Daddy ya aika takardun retire (murabus daga soja) Abuja. Ko kadan Al’ameen bai so ba, domin yana tunanin Daddyn ya yi hakan ne domin ya yi joining su Benga Delsu da ke son yin juyin mulki cikin ‘yan shekaru kalilan. Bakin ciki biyu kenan ya hadu ya tarar masa. Ga nadamar abin da ya aikata, wadda ta sa har ya tsani kansa da kasar haihuwar shi baki daya, ga kuma bakin cikin Daddyn su zai zubar da mutuncin su a idon duniya.
Ran shi a masifar bace ya sake bijiro da bukatar shi na tuntuni, wato na son tafiya karatu Miami, ba tare da ya tambayi Daddyn dalilin shi na yin ritaya ba. Daddyn ya ce ya je duk abin da suka shawarta da mahaifiyarsa shi ba shi da ta cewa. Da kyar Al’ameen ya shawo kan Hajiyar ta amince da tafiyar shi sai dai ba ta amince mai zuwa America ba, duk wani Musulmi na kwarai yana neman tsari daga sharrin wannan kasa, amma ba wai ya yi marmarin kai kansa ba, ba mamamki ya mance kasar haihuwar shi Nigeria ce, birni irin Miami?
Birni ne na hutu zallah, yana daya daga cikin biranen da kasar Amurka ke takama da su, saboda kasancewar shi wani bangare na kara bunkasar tattalin arzikinta (tourist attraction) sabida yadda al’ummar duniya suka zabeshi a matsayin wajen hutun su (Miami resort) ga kuma kashe Musulmi da kasar Amurka ke yi a lokacin.
Abu daya ne har zuwa yanzun ta ki mara masa baya wato ra’ayin shi na son tafiya karatu Miami (Miami gari ne na ‘yan hutu cikin U.S.A) don tana ganin duk cikin ‘ya’yanta ya fi sonta, ya fi su kaunar ta, ya fi kaunar abin da take so. Idan ya tafi wa zai taya ta kiyayyar su Saratu?
Tsaye yake jikin Volvos 6 din Hajiyar shi, yana ta faman murza ‘yar karamar kwamfutar aljihu pocket computer, sanye yake cikin Kaftani na wata jikakkiyar shadda-rini ‘yar Mali. Sai ga Intisar da Khalil tana rungume da ribdediyar teddin ta, daga inda yake tsaye yana iya jiyo muryar Khalil na cewa, “Baby ki je ki kwantar da ita a karkashin mota zan je in dauko mata filon ta.�
Ya juya ya koma cikin gida yayin da ita kuma ta nufi karkashin motar da Al’ameen ke tsaye ba tare da ta lura da shi ba, domin ya ba su baya ne. Sojojin da ke gadi a harabar gidan ba wanda ya ba su hankalin shi kasancewar sun riga sun saba wasansu a wurin kullum ta Allah.
Ta sunkuya za ta shimfide teddin kenan, sai ya sa kafa iya karfin shi ya yi (bull) da ita, ta hantsila ta wulwula har sau uku, kafin idanunta da goshinta su hadu da wani karfen pipe ta gigice ta dimauce ta saki wata irin razananniyar kara da amsa kuwwar ta ya ratsa illahirin gidan, gaba daya ma’aikatan gidan har shi Aminun suka yi kanta a guje.
Jikinsa ya yi sanyi da ganin jini na gudu daga idanun yarinyar hade da wani irin ruwa. Ya saki Computer da ke hanun shi ya dauke ta a gigice yana.
‘Emma bude mini mota, wayyo Allah na shiga uku! Na yi kisan kai!�
Abin da yake ta nanatawa kenan, har suka isa asibiti. Mummunan labarin ya riski Aunty Saratu ne tana cin abinci, ta saki cokalin ta ce, ‘Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un�.� Don Khalil da ke bayar da labarin cewa ya yi idanun Baby sun tsiyaye.
Shi kan shi Daddy jikin shi babu inda baya rawa, da kyar ya kulle Aunty Saratu yabi bayan su saboda yadda ta fita daga hayyacinta cewa kawai take, ‘Yanzu baby shi kenan idon ki ya tsiyaye?�
Likitocin ido kwararru uku ne a kan Intisar suna kokarin ceton ‘eye-bulls� dinta (kwayar idonta). Sai bayan awanni uku babban likitan ya nemi ganin Daddyn a ofis din shi, ya fara da kwantar masa da hankali, don ganin yadda duk ya fidda rai ya kuma ba shi shawarar a kai baby asibitin kwararrun ido na Kaduna, in an yi sa’a a ceci lafiyar idonta, amma he’s sorry to say, ko da Saratu ta warke ba za ta ci gaba da gani da naked-eyes dinta ba.
Inda duk hankalin Daddy yake in ya yi dubu to ya tashi, bai tausayin Baby kamar Aunty Saratu, da ta ci duk wani buri da fatan ta a kan Inteesar! Amman a yau a ce ta makance! Duk kwazon ta, duk himmar ta da ke sawa ana yi mata hangen zama wani abu a gaba. Bai san san da wasu zafafan hawaye suka shiga yi masa lugulgude a fuska ba tamkar ba Brigadier na soja ba.
Yasa habar babbar rigar a ya share kafin ya sa hannu a tura su Kadunan.
A jirgin (bell-view) da suke ciki, Aminu Bello, tafukansa yasa ya rufe kyakkyawar fuskarsa. Ya sha jin Malamin su na Islamiyya na cewa, ‘Ku roki Allah ya kare ku daga nadama mara amfani.�
Bai taba sanin mene ne nadama mara amfani ba sai yau. Tausayin mahaifin su kadai ya ishe shi na wahalar da ya jawo masa. Ya san Daddyn na son shi, amma a yau yana shakkar, idan son da Daddy ke wa Inteesar diyar Aunty Amarya bai dame wanda Daddyn ke masa ba.
A asibitin Kadunar ma sun ce ne idan Daddyn na da hali to ya gaggauta fitar da diyar sa asibitin kwararrun ido da ke Jiddah, nan suka bar Intisar karkashin matsananciyar kulawar likitoci su suka tafi neman visa. Masu abu da abin su nan da nan suka samu. Karfe tara na dare an shigar da Baby tiyatar ido.
Mu karasa a littafi na biyu.
Taku
Takori
How much do you like this story?
5/7/22, 13:10 - Ummi Tandama😇: ____________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book two
*@Takori*
Page1ï¸âƒ£
Ameenu kishingide cikin lallausar kujerar asibitin Saudi-German, nadama goma da ashirin ji yake kamar ya farkewa Daddyn shi komai, in ya so ya nemi gafarar shi, ko ya samu saukin wannan dumbin hakki da ya dauka na rayukan al’umma da dama, na kuma yarinyar da ba ta ji ba ba ta gani ba, ba ta kuma tsare masa komai a rayuwa ba.
Lokaci daya ya ji ya tsani kan sa kai da duk ‘ya’ya masu irin halin shi na taya iyayensu mata kishi. Amma tsoron hukuncin da Daddyn zai dauka a kan shi ya hana shi, gani yake kamar ma ya san shi ne sanadiyyar shigar diyar shi cikin wannan azaba shiru kawai ya yi masa, watakila ma kuma idan ya fada masa shi din ne ya tsane shi, hakan kuma ya yi sanadiyyar jawo masa bacin ran Hajiyar shi.
Ya yi tunani iyaka tunani, ya rasa mafita cikin al’amarinsa, tunda kuwa ya zama fitina kenan ga iyayen shi? Daga karshe ya yanke abinda yake ganin shi ne mafi dacewa a gareshi shi ne ya bar su kwata-kwata ya fita daga tsakanin su, ya yi nisa da rayuwar su, ya bar masu kasar baki daya ya je ya ginawa kansa sabuwar rayuwa mai amfani. Me ye amfanin ‘ya’ya irin sa masu sanya iyayensu cikin halin ha’u’la’i? Babu.
Kada ma ya je Hajiya ta angiza shi ga kisan kai, don ma abin ya zo da sauki? Da ta mutu fa me zai ce da Ubangijinsa? A kan wani kishin su na mata wanda shi bai shafe shi ba.
Tunaninikan da yake ta yi kenan har aka fiddo Intisar daga dakin tiyatar da karfe biyu da rabi na sulusin dare agogon su na can. Ya tsaya a kan ta yana ta muzurai ganin yadda aka nannade dukkan idanunta da bandeji, jikinsa ya saki gaba daya.
Washe gari likita Doctor Khair ya tabbatar wa Daddy Saratu za ta gani da taimakon medical glasses kanana da za su yi mata. Bayan sati biyu da yin aikin aka cire bandejin da addu’o’i na musamman a bakunansu don Daddy har Dawafi na musamman ya yi a kan lafiyar Intisar kadai.
To Alhamdulillahi Saratu na gani daga kusa-kusa, sai dai ba ta iya gane abin da ke nesa da ita tangaran abinda a turance suke kira short eye-sight.
A ranar Dr. Khair ya manna mata farin siririn medical glasses tamkar gidan biro don siranta garai-garai da shi kamar na ado, wallahi kada ki so ki ga yadda ya karawa yarinyar nan wani irin kyau da kwarjini, da aka sa mata sai ta kama dariya.
Daddy ya kashe kudi ba kadan ba, amma wannan ba shi ne damuwarsa ba shi dai burinsa kada a ce Saratu ta rasa ganin ta kwata-kwata. Don haka da ya tabbatar tana gani tar da gilashin in an cire ne take gani dusu-dusu sai ya gode Allah.
A ranar da suka cika sati na biyar suka dawo. Anti Saratu duk ta rame ta yi duhu saboda zullumi. A guje Intisar ta rungume Mamarta suka shiga juyi a tsakar gidan har suka bai wa kowa da ke wajen tausayi.
Tana gaya mata labarin Daddy ya saya mata gilas mai kyau, za ta ke ba ta aro tana danawa, yaya Aminu yana ba ta abinci a baki baya tsula mata carbi a unguwar da suka je. Yayin da Ameenun ya yi tsaye harde da hannunsa bisa kirji yana kallon su cike da jin nauyi ko kadan bai bari sun hada idanu da Antin ba, tunda suka dawo. Antin ta dube si ta watsar ta ce, ‘Al’ameen kenan. Kai ma sannu da kokari.�
Yanayin yadda ta fadi maganar cikin gatse, dole ta sa shi ya yi murmushin dole har cleft din ya lotsa, ya kuma sha jinin jikin sa, ji yake kamar ya ce da kasar ta tsage ya shige, ji yake kamar Anti Saratu ta san shi ne sanadiyyar nakasar diyar ta.
Haka kurum Daddy ya aika takardun retire (murabus daga soja) Abuja. Ko kadan Al’ameen bai so ba, domin yana tunanin Daddyn ya yi hakan ne domin ya yi joining su Benga Delsu da ke son yin juyin mulki cikin ‘yan shekaru kalilan. Bakin ciki biyu kenan ya hadu ya tarar masa. Ga nadamar abin da ya aikata, wadda ta sa har ya tsani kansa da kasar haihuwar shi baki daya, ga kuma bakin cikin Daddyn su zai zubar da mutuncin su a idon duniya.
Ran shi a masifar bace ya sake bijiro da bukatar shi na tuntuni, wato na son tafiya karatu Miami, ba tare da ya tambayi Daddyn dalilin shi na yin ritaya ba. Daddyn ya ce ya je duk abin da suka shawarta da mahaifiyarsa shi ba shi da ta cewa. Da kyar Al’ameen ya shawo kan Hajiyar ta amince da tafiyar shi sai dai ba ta amince mai zuwa America ba, duk wani Musulmi na kwarai yana neman tsari daga sharrin wannan kasa, amma ba wai ya yi marmarin kai kansa ba, ba mamamki ya mance kasar haihuwar shi Nigeria ce, birni irin Miami?
Birni ne na hutu zallah, yana daya daga cikin biranen da kasar Amurka ke takama da su, saboda kasancewar shi wani bangare na kara bunkasar tattalin arzikinta (tourist attraction) sabida yadda al’ummar duniya suka zabeshi a matsayin wajen hutun su (Miami resort) ga kuma kashe Musulmi da kasar Amurka ke yi a lokacin.