Sashe 65
Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duka wannan matter bai yi kamari yadda kika daukeshi ba, don Allah, ki maida walwalarki ki, ki bude sabon shafin rayuwar farin-ciki da ‘yanci tamkar kowa, ina kara gaya miki ba fa mai yi miki dole kan abinda ba kya so.�
Tasa gefen dankwalinta ta share idon ta tas, eh, gaskiya Najib ya fada, yanzune ya dace ta budewa kanta sabuwar rayuwa mai ‘yanci, tamkar sauran ‘ya’yan gata, ciki kuwa har da neman ‘yancin kanta na rama abinda uwar su ta shekara yi mata!
Wasa farin girki! Tun kowa na tsammanin Intisar wasa take maganar rashin amincewar ta kan aurenta da Al’ameen har suka tabbatar da gaske take. Duk wasu hanyoyin sadarwa tsakanin su ta toshe su, bata daukar wayar shi hakannan in zai wuni cikin gidan bazata bari ya ganta ba, ko dai ta kulle kanta a (toilet) ko ta shige cikin (store) har ya gaji ya tafi haka Anti tace ba ruwan ta, ta tsame hannun ta a al’amarin duk abinda Intisar din ta zabawa rayuwar ta tayi dai-dai.
Al’ameen duk ya sukurkuce ya rasa inda zai tsoma ransa, bashi gaban Daddy bashi gaban Anti, wurin Hajiya Hadiza kadai yake samun sanyi to ita din ma mijin ta daga baya ya gargadeta ta fita harkar su, tunda tare ta gan su, bata da wata (power) in dai akan Intisar ne.
Su Hidayah kam bakin-cikin da suke ji kan Yayar su da hukuncin ta har kuka suke tausayin Al’amen kadai ya ishe su, duk ya rame ga wata kasimba ta babu gaira babu dalili ta cika kyakkyawar fuskar sa, duk son gayu da kwalisa irin na Al’ameen Bello, a yanzu babu ya kau. Babu komi gaban sa kamar Intisar din da ke neman kufce masa karfi da yaji yana ji yana gani.
Babban abinda yafi damun sa shine wani kululu ko katutu dake tokare shi a kahon zucci, in ya tuna wai yau Halimar sa ce ke gudun sa sabida Hajiyar sa? Yayi dakacen kasancewar sa Al’ameen dan Hajiya Nafi, ba tun yau ba, a yau ma yana karawa.
Ya kuma tabbata wannan tabon data yaba masu har abada bazai gogu a zuciyar yarinyar ba. Yayi ban hakurin, yayi ban bakin yayi lallashin duk a banza. Yo ina ya ganta ma?
Ta haramta masa ganin kyakkyawar fuskarta da ke sa shi nutsuwa balle dan murmushin ta dake gigita shi, duk sun zama tarihi, na wani zamani can daya shude, zamanin da yake ganin ba zamanin da ya samu gata a cikin sa kamar sa, wato zamanin rayuwar ta a Kitchin.
Ya kan zauna yayi tunani, iya kokarin sa ya rasa mafita cikin al’aamarin sa, karewa ma, bai san me take nufi da shi ba; tana son sa ko ta daina son sa?
Kai bashi kadai ba babu wanda ya san nufin da ke kunshe cikin zuciyarta a gidan. Cikin wannan halin Faisal ya samu Daddy ya gaya masa ‘transfer� da ya dade yana nema zuwa NNPC na Lagos ya fito. Daddy ya nemi dalilin ‘transfer� din yace hakanan yake son yanayin garin Legas, ya kuma dade da burin aiki a nan to sai ga yadda al’amarin ya kasance, wato samun aikin da yayi da wurwuri anan Abj.
Daddy yace ya je Allah ya sanya albarka amma yayi kokarin zuwa ya ga lafiyar gida duk karshen sati ko bayan sati bibbiyu. Ba kuma tare da ya kara bi ta kan kowa ba ya yai tafiyar sa, inda ya rungumi aikin sa cike da karfin zuciya.
Yau kam Al’ameen ya kudurce bai barin gidan sai yaga Intisar ko da hakan na nufin ya kwana a gidan ne. Yana ta zarya falon Anti zuwa sassan Daddy har dare bata ba alamarta. Shi kam duk ya fi daura laifin komi akan Anti don a tsammanin sa da sanin Antin Intisar ke yi masa duk abinda ta ke yi.
Bai sani ba, Antin ta fishi takaicin abinda Intisar ta yanke a kansa, don dai bata son matsanta mata ne. Ta tabbata ita yarinya ce, amma mai sahihin tunani da hangen nesa, tabbas tana da kwakkwarar hujjar ta ta yin hakan. Ita kadai tasan azabar da ta kwankwada a hannun Hajiya, sai dai tana matukar tausayin Al’ameen har hawaye take masa kamar su Hidayah amma a bayan idon sa.
Karfe daya da rabi na sulusin dare ta fito daga maboyar ta, wato cikin store, ta san dai duk nacin sa zuwa yanzun ya hakura ya tafi amma me? Ta zauna gefen gadon ta kenan ya murdo kofar ya shigo.
Ba karamar razana ta yi ba amma sai ta cije, ta yi kamar bata gan shi ba. Ta cigaba da kokarin gyara wajen da zata kwanta. Hakikah zuciyar ta ta girgiza da ganin muguwar ramar da yayi fiye da sanda ya kwanta ciwo, ga sumar da ta cika kyakkyawar fuskar sa kamar ba Al’ameen din da ta sani ba, mai tsananin kwarjini, gayu da kwalisa, ilhama da cikar zati. Fuskar shi ba annuri sam kamar yadda zuciyar sa ke wani irin zazzafan bugu da sauri da sauri.
Ya dubeta da lumsassasun idanun sa cikin fidda rai da al’amarinta, ya karisa har gaban mudubin ta ya ja (stool) ya zauna yana fuskantar ta, cikin raunanniyar muryar da bata taba ji daga gare shi ba yace
“Inteesar!�
Ta dago ta dube shi, amma ta kasa magana, sabida zuciyarta dake neman bayar da ita. Ji ta ke kamar ta ruga ta rungume shi tayi kukanta mai isar ta, ta gaya mishi tayi kewarsa ita ma fiye da yadda harshe zai iya furtawa, fiye da yadda kwakwalwa zata iya fassarawa kuma fiye da yadda tunani zai iya kintatawa.
Ta ji ta a marainiya, duk kuwa da tarin iyayen da suka zagayeta a yanzun. Ta fi jin ta a mai cikakken gata, a sanda suke tare a (kitchen) fiye da yanzun da take da Daddy da mamar ta. Ta azabtu da rashin ganinsa fiye da yadda shi yake tunani.
Ya dubeta ya gani, ta fi shi ramewa da lalacewa, ta fi shi ciwon zuciya illa ita mai iya ‘controlling� zuciyanta ne ba kamar shi da zuciya ke juyawa ba.
Ta fishi jin ciwon abinda take masa da hukuncin da ta yanke masu, kuma ta fishi azabtuwa daga hukuncin. Ta fi shi tunanin yaya rayuwarta zata karasa batare da shi ba? Ya fiye mata duk wannan gayyar dangin da suka zagayeta! To amma wannan alkawari ne, alkawari ne tsakanin ta da zuciyar ta da Ubangijin da ya halicceta ta yaya bazai gane ba ya taimaka mata wajen cikar alkawarinta da burin da ta dade tana ciwa zuciyarta�.
Sheshekar kukan Al’ameen ya katseta da digar zafafan hawayenshi bisa tafin kafarta, dubawar nan da zatayi sai taga Al’ameen ne durkushe a gabanta, yama rasa kalmar da zai yi amfani da ita wajen rarrashinta da nuna mata muhimmancinta a gareshi.
Me zai gaya mata ta yarda bazai iya jinyar zuciyar nan ba� me zai gaya mata ta san ya manta komi, ya manta kowa, ya manta ko shi wanene saboda rashin soyayyar ta?
To itama kukan take mai tsima zuciya an rasa wanda zai rarrashi wani a tsakanin su.
Ta ga dai inta biye masa zasu kwana ne a hakan, wanda ita bata fatan hakan. Ita kadai ta san yakin da take yi da zuciyarta a duk sanda take tare da Al’ameen, balle a irin wannan halin da zuciyoyinsu ke gab da narkewa saboda azababben son da fada ma bata baki ne.
Ta sauka daga gadon itama tayi tsugunne bisa carpet a gabansa tamkar yadda yayi, don tana ganin it’s a disgrace agareshi ya durkusa mata, cikin muryar kuka da nadama tace
“Ni, ni� dama cewa nayi sai in har Hajiya ta rokeni gafarar abinda tayi mun, ta kuma furta amincewa da ni a matsayin matar ka, sannan ne zan yarda.�
Ya dago a hankali ya dubeta, yayi tsai da ransa yana nazarin zancenta. Tamkar kuma wanda aka yiwa allurar kuzari kuma sai ya mike tsaye, ya zauna a gefenta yace
“Har ga Allah Saratu wanan shine uzrin ki?� Ta gyada kai tana hadiyar zuciya. Yayi murmushi, ya ce,
“Intisar, idan na kawo Hajiya na gaban ki da Daddy da Aunty, ta nemi gafararki, ta kuma ce ta amince muyi aure, shikenan?�
Ta kara gyada kai da sauri. Ya sake yin murmushi ya mike, jikinsa ba inda baya rawa ya ce,
“Keep your promise.�
Ya soma ja da baya-da-baya har ya tadda kofar fita idon shi na kanta, yana mata murmushin da har abada ba zai gushe daga zuciyarta ba, cikin karfin hali itama ta mayar masa, sai kuma duk suka kyalkyale da dariya ga hawaye sosai a fuskar kowannen su. Ya daga hannunshi ya sumbata kana ya huro mata iskar. Da haka ya bar dakin gudu-gudu sauri-sauri, zuwa inda ya adana motarsa. Akan idon Daddy dake kallonshi ta taga ya ja motar ya bar gidan.
Daddy da Aunty Saratu suka yi ajiyar zuciya a tare. Duk kawaici irin nasa a yau ya yanke shawarar dosar Intisar a washegari don jin inda ta sa gaba, abin ya isa.
Washegari ta je gaida Daddyn da safe kamar yadda ta saba a ‘main� falonshi, yana rigingine cikin kujera da ‘yar karamar rediyon shi inda yake sauraren ‘Voice of America� shigowar ta yasa ya kashe rediyon kwata-kwata ya bata hankalinshi yana murmushi tun kamin ta zauna ya ce,
“Saratu, gobe fa in Allah ya kaimu tare da su Hunainah zaku tashi, daga Korea zasu rakaki makaranta don duk wasu shirye-shiryen komawar taki ban san sanda Al’ameen yayi ba. Dama abinda yasa aka daga tasu tafiyar kenan nima ban sani ba sai jiya yake gaya mun. Sai dai kuma naga alamar bakya son sakin jiki da Haj. Hadiza, Why?�
Ta yi shiru, yayi zaton bata ji ba sai ya sake maimaita tambayarshi. Ta dan kada kafadu alamun zancen bai dameta ba ta ce, “ba komi� ya ce,
“Ba komi, na nufin komi. Duk inda kika ji ance ba komi, to anan koman take�.
Tasa gefen dankwalinta ta share idon ta tas, eh, gaskiya Najib ya fada, yanzune ya dace ta budewa kanta sabuwar rayuwa mai ‘yanci, tamkar sauran ‘ya’yan gata, ciki kuwa har da neman ‘yancin kanta na rama abinda uwar su ta shekara yi mata!
Wasa farin girki! Tun kowa na tsammanin Intisar wasa take maganar rashin amincewar ta kan aurenta da Al’ameen har suka tabbatar da gaske take. Duk wasu hanyoyin sadarwa tsakanin su ta toshe su, bata daukar wayar shi hakannan in zai wuni cikin gidan bazata bari ya ganta ba, ko dai ta kulle kanta a (toilet) ko ta shige cikin (store) har ya gaji ya tafi haka Anti tace ba ruwan ta, ta tsame hannun ta a al’amarin duk abinda Intisar din ta zabawa rayuwar ta tayi dai-dai.
Al’ameen duk ya sukurkuce ya rasa inda zai tsoma ransa, bashi gaban Daddy bashi gaban Anti, wurin Hajiya Hadiza kadai yake samun sanyi to ita din ma mijin ta daga baya ya gargadeta ta fita harkar su, tunda tare ta gan su, bata da wata (power) in dai akan Intisar ne.
Su Hidayah kam bakin-cikin da suke ji kan Yayar su da hukuncin ta har kuka suke tausayin Al’amen kadai ya ishe su, duk ya rame ga wata kasimba ta babu gaira babu dalili ta cika kyakkyawar fuskar sa, duk son gayu da kwalisa irin na Al’ameen Bello, a yanzu babu ya kau. Babu komi gaban sa kamar Intisar din da ke neman kufce masa karfi da yaji yana ji yana gani.
Babban abinda yafi damun sa shine wani kululu ko katutu dake tokare shi a kahon zucci, in ya tuna wai yau Halimar sa ce ke gudun sa sabida Hajiyar sa? Yayi dakacen kasancewar sa Al’ameen dan Hajiya Nafi, ba tun yau ba, a yau ma yana karawa.
Ya kuma tabbata wannan tabon data yaba masu har abada bazai gogu a zuciyar yarinyar ba. Yayi ban hakurin, yayi ban bakin yayi lallashin duk a banza. Yo ina ya ganta ma?
Ta haramta masa ganin kyakkyawar fuskarta da ke sa shi nutsuwa balle dan murmushin ta dake gigita shi, duk sun zama tarihi, na wani zamani can daya shude, zamanin da yake ganin ba zamanin da ya samu gata a cikin sa kamar sa, wato zamanin rayuwar ta a Kitchin.
Ya kan zauna yayi tunani, iya kokarin sa ya rasa mafita cikin al’aamarin sa, karewa ma, bai san me take nufi da shi ba; tana son sa ko ta daina son sa?
Kai bashi kadai ba babu wanda ya san nufin da ke kunshe cikin zuciyarta a gidan. Cikin wannan halin Faisal ya samu Daddy ya gaya masa ‘transfer� da ya dade yana nema zuwa NNPC na Lagos ya fito. Daddy ya nemi dalilin ‘transfer� din yace hakanan yake son yanayin garin Legas, ya kuma dade da burin aiki a nan to sai ga yadda al’amarin ya kasance, wato samun aikin da yayi da wurwuri anan Abj.
Daddy yace ya je Allah ya sanya albarka amma yayi kokarin zuwa ya ga lafiyar gida duk karshen sati ko bayan sati bibbiyu. Ba kuma tare da ya kara bi ta kan kowa ba ya yai tafiyar sa, inda ya rungumi aikin sa cike da karfin zuciya.
Yau kam Al’ameen ya kudurce bai barin gidan sai yaga Intisar ko da hakan na nufin ya kwana a gidan ne. Yana ta zarya falon Anti zuwa sassan Daddy har dare bata ba alamarta. Shi kam duk ya fi daura laifin komi akan Anti don a tsammanin sa da sanin Antin Intisar ke yi masa duk abinda ta ke yi.
Bai sani ba, Antin ta fishi takaicin abinda Intisar ta yanke a kansa, don dai bata son matsanta mata ne. Ta tabbata ita yarinya ce, amma mai sahihin tunani da hangen nesa, tabbas tana da kwakkwarar hujjar ta ta yin hakan. Ita kadai tasan azabar da ta kwankwada a hannun Hajiya, sai dai tana matukar tausayin Al’ameen har hawaye take masa kamar su Hidayah amma a bayan idon sa.
Karfe daya da rabi na sulusin dare ta fito daga maboyar ta, wato cikin store, ta san dai duk nacin sa zuwa yanzun ya hakura ya tafi amma me? Ta zauna gefen gadon ta kenan ya murdo kofar ya shigo.
Ba karamar razana ta yi ba amma sai ta cije, ta yi kamar bata gan shi ba. Ta cigaba da kokarin gyara wajen da zata kwanta. Hakikah zuciyar ta ta girgiza da ganin muguwar ramar da yayi fiye da sanda ya kwanta ciwo, ga sumar da ta cika kyakkyawar fuskar sa kamar ba Al’ameen din da ta sani ba, mai tsananin kwarjini, gayu da kwalisa, ilhama da cikar zati. Fuskar shi ba annuri sam kamar yadda zuciyar sa ke wani irin zazzafan bugu da sauri da sauri.
Ya dubeta da lumsassasun idanun sa cikin fidda rai da al’amarinta, ya karisa har gaban mudubin ta ya ja (stool) ya zauna yana fuskantar ta, cikin raunanniyar muryar da bata taba ji daga gare shi ba yace
“Inteesar!�
Ta dago ta dube shi, amma ta kasa magana, sabida zuciyarta dake neman bayar da ita. Ji ta ke kamar ta ruga ta rungume shi tayi kukanta mai isar ta, ta gaya mishi tayi kewarsa ita ma fiye da yadda harshe zai iya furtawa, fiye da yadda kwakwalwa zata iya fassarawa kuma fiye da yadda tunani zai iya kintatawa.
Ta ji ta a marainiya, duk kuwa da tarin iyayen da suka zagayeta a yanzun. Ta fi jin ta a mai cikakken gata, a sanda suke tare a (kitchen) fiye da yanzun da take da Daddy da mamar ta. Ta azabtu da rashin ganinsa fiye da yadda shi yake tunani.
Ya dubeta ya gani, ta fi shi ramewa da lalacewa, ta fi shi ciwon zuciya illa ita mai iya ‘controlling� zuciyanta ne ba kamar shi da zuciya ke juyawa ba.
Ta fishi jin ciwon abinda take masa da hukuncin da ta yanke masu, kuma ta fishi azabtuwa daga hukuncin. Ta fi shi tunanin yaya rayuwarta zata karasa batare da shi ba? Ya fiye mata duk wannan gayyar dangin da suka zagayeta! To amma wannan alkawari ne, alkawari ne tsakanin ta da zuciyar ta da Ubangijin da ya halicceta ta yaya bazai gane ba ya taimaka mata wajen cikar alkawarinta da burin da ta dade tana ciwa zuciyarta�.
Sheshekar kukan Al’ameen ya katseta da digar zafafan hawayenshi bisa tafin kafarta, dubawar nan da zatayi sai taga Al’ameen ne durkushe a gabanta, yama rasa kalmar da zai yi amfani da ita wajen rarrashinta da nuna mata muhimmancinta a gareshi.
Me zai gaya mata ta yarda bazai iya jinyar zuciyar nan ba� me zai gaya mata ta san ya manta komi, ya manta kowa, ya manta ko shi wanene saboda rashin soyayyar ta?
To itama kukan take mai tsima zuciya an rasa wanda zai rarrashi wani a tsakanin su.
Ta ga dai inta biye masa zasu kwana ne a hakan, wanda ita bata fatan hakan. Ita kadai ta san yakin da take yi da zuciyarta a duk sanda take tare da Al’ameen, balle a irin wannan halin da zuciyoyinsu ke gab da narkewa saboda azababben son da fada ma bata baki ne.
Ta sauka daga gadon itama tayi tsugunne bisa carpet a gabansa tamkar yadda yayi, don tana ganin it’s a disgrace agareshi ya durkusa mata, cikin muryar kuka da nadama tace
“Ni, ni� dama cewa nayi sai in har Hajiya ta rokeni gafarar abinda tayi mun, ta kuma furta amincewa da ni a matsayin matar ka, sannan ne zan yarda.�
Ya dago a hankali ya dubeta, yayi tsai da ransa yana nazarin zancenta. Tamkar kuma wanda aka yiwa allurar kuzari kuma sai ya mike tsaye, ya zauna a gefenta yace
“Har ga Allah Saratu wanan shine uzrin ki?� Ta gyada kai tana hadiyar zuciya. Yayi murmushi, ya ce,
“Intisar, idan na kawo Hajiya na gaban ki da Daddy da Aunty, ta nemi gafararki, ta kuma ce ta amince muyi aure, shikenan?�
Ta kara gyada kai da sauri. Ya sake yin murmushi ya mike, jikinsa ba inda baya rawa ya ce,
“Keep your promise.�
Ya soma ja da baya-da-baya har ya tadda kofar fita idon shi na kanta, yana mata murmushin da har abada ba zai gushe daga zuciyarta ba, cikin karfin hali itama ta mayar masa, sai kuma duk suka kyalkyale da dariya ga hawaye sosai a fuskar kowannen su. Ya daga hannunshi ya sumbata kana ya huro mata iskar. Da haka ya bar dakin gudu-gudu sauri-sauri, zuwa inda ya adana motarsa. Akan idon Daddy dake kallonshi ta taga ya ja motar ya bar gidan.
Daddy da Aunty Saratu suka yi ajiyar zuciya a tare. Duk kawaici irin nasa a yau ya yanke shawarar dosar Intisar a washegari don jin inda ta sa gaba, abin ya isa.
Washegari ta je gaida Daddyn da safe kamar yadda ta saba a ‘main� falonshi, yana rigingine cikin kujera da ‘yar karamar rediyon shi inda yake sauraren ‘Voice of America� shigowar ta yasa ya kashe rediyon kwata-kwata ya bata hankalinshi yana murmushi tun kamin ta zauna ya ce,
“Saratu, gobe fa in Allah ya kaimu tare da su Hunainah zaku tashi, daga Korea zasu rakaki makaranta don duk wasu shirye-shiryen komawar taki ban san sanda Al’ameen yayi ba. Dama abinda yasa aka daga tasu tafiyar kenan nima ban sani ba sai jiya yake gaya mun. Sai dai kuma naga alamar bakya son sakin jiki da Haj. Hadiza, Why?�
Ta yi shiru, yayi zaton bata ji ba sai ya sake maimaita tambayarshi. Ta dan kada kafadu alamun zancen bai dameta ba ta ce, “ba komi� ya ce,
“Ba komi, na nufin komi. Duk inda kika ji ance ba komi, to anan koman take�.