Sashe 54
Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Al’ameen ka gafarce ni, na san mun yi kuskure ni da Saratu wajen boye maku ainahin kowacece Intisar, ba mu yi hakan domin mugunta ko wata manufa ta daban ba, illa domin tserar da ita daga kuncin da zata iya fadawa a girmanta inta fahimci ita ‘yar tsintuwa ce, sanin kanka ne ba abinda ya kai rashin asali ciwo. Aminu ka taimake ni ka mike ni kum in aura ma Saratu-Intisar!
Wallahi ba ‘yata bace, tsintar ta nayi a daji na kawowa Saratu. Hajiyar ka zata tabbatar maka da hakan. Al’ameen don Allah ka mike! Ka mike!! Ba abinda ya hadaka da Saratu da zai hanaku aure�
Kuka yaci karfinsa da ya ga Aminu ko gizau. Ya kifa kai jikin karfen gadon yana ta yi kamar ba tsohon soja ba. Tausayi da dadi ne ya rufe Haj. Haddizah, wasu siraran hawaye suka ziraro mata, hawayen farin-ciki da tausayi duk a lokaci daya.
Ta dibi yadda Allah Al-mussawwiru ke juya masu al’amuran cikin ruwan sanyi, ta kara amincewa lallai shi buwaya ne, gagara mithali. Sai ta matsa jikin gadon Al’ameen ta dubshi sosai. Tausayin shi da kaunar shi babu inda bai bi jini da tsokar jikin ta ba.
Wai fa wannan kaunar diyarta ne ya kayar dashi haka? Ta russuna ta barin hagu, kanta jikin gadon a kife tace.
“Kwarai Al’ameen Saratu, Intissar kuma Fatima ba kanwar ka bace kamar yadda kake tunani, ka tashi don Allah ka tausayawa Intisar da Babanka bisa halin da zai shiga in ya rasaka. Ni ce mahaifiyar Intisar. Mahaifin ta ya rasu ne tun tana Jaririya a dalilin bakin-cikin sace mana ita da a kayi aka kai daji, shine Babanka ya tsinta. Wannan shine gaskiyar al’amarin.
Idan ka mike Al’amin ko a gobe sai mu daura maku aure, in ce ko shikenan? Ba fa abinda ya hadaku da Intissar!� Ta fadi da dan karfi cikin gunjin kuka.
Maganganun har tsakar kwakwalwarsa amon su ke yawo, ya motsa kadan alamar sun dameshi, Alfered ya janyesu yace “ya isa hakanan�.
To Hadiza da Daddy sai aka koma kallon-kallo. Kallo daya yayi wa Haj. Hadiza yasan yaga mahaifiyar Saratu a yau, in banda nauyin shekaru ba zai yarda ba Saratu-Intisar din su ce wannan tsaye a gabansa ba.
Kwanaki goma abinda iyaye da ‘yan uwa ke ta gayawa Al’ameen da Intisar kenan. Har ita kanta Anti Saratu ta gigice rannan da Intisar tayi wani dogon suma kamar bata dawo ba ta shiga fada mata ba abinda zai hanasu aure don babu alakar jini a tsakaninsu. Malam Sani da Goggo Jummai ma ba’a barsu a baya ba wurin nunawa ‘yan gatannan kauna.
Haka Hidayah da Hunainah dake kwana rungume da ‘yar uwarsu a cinya, suna rokonta ta tashi ta auri Yaya Al’ameen, ta basu kulawar da yayye ke baiwa kanne, ta ji dumin Mamarsu itama. Su nuna mata kulawa da kaunar da bata samu ba na kanne mata.
Fatan Anti Saratu kawai samuwar lafiyar Intisar da likita ya ce, ‘Shock� ne kadai ya gigitata ya wargaza mata tunani. Amma a hankali tunaninta yana saisaita kuma tunda ga komi yazo da sauki, danginta sun bayyana a sanda ake tsananin bukatar su.
Ita da Hajiya Hadiza kwana suke bakin su bai yi shiru ba kullum dai zancen kenan. Cikin wannan halin Najib ya kira mahaifiyarsu a waya ya ce,
“Hajiya, kin ce zaki dawo har yanzu kaman an aiki bawa garinsu, amma yanzu ina jin ya dace ki dawo, tunda ga Aminun ki kwance a gadon asibiti ba yadda yake, bai kuma san wanda ke kansa ba?�
Ta ce cikin shesshekar kuka
“Idan ka gan ni a Nigeria to na zo ganin ku ne, amma ni da gidan ubanku har abada! Sai dai ya zaba ko ni ko Saratu da tsinanniyar ‘yar sa. Idan nazo zan baiwa Aminu lafiya ne? Allah ya bashi sauki.�
Najib ya so yayi mata bayani yaga ma bayanin baya da amfani, shin yaya zata ji idan ta ji cewa ‘yar da tafi tsana a duniya ce Dan da tafi so fiye da kowa ke so har ya kamu da ciwon zuciya? Ashe dalilinta na kin Intisar shine don tsinto ta aka yi, kuma tana tsammanin shegiya ce? Wane bayani zai mata ta fahimta a waya? Sai yace “Hajiya ki daina illata Intisar hakannan, don zaki sha mamaki. Don Allah ki gyara halin ki, ki dawo ki ji me ke faruwa cikin rayuwar ‘ya’yan ki?�
Faisal tunda ya fahimci abinda ke faruwa ya bar asibitin, bai kara waiwayar kowa ba, babu kuma wanda ya kara jin duriyar shi cikin asibitin. A lokacin da ake tsammanin shine mutumin da zai fi kusantar Saratun fiye da kowa.
Iyayen na mamakin irin wannan masifaffen so na Intisar da Aminu, gashi ba wani dogon lokaci suka dauka tare ba. So mai neman salwantar da rayuwa kamar a birnin Hindu ai abin mamaki ne.
To Al’ameen da ‘feeling hopes� din da Daddy da Hadiza ke ta bashi ya soma shaida mutane. Ga Addu’o’in da su Baffa ke tayi har Mallam Sidi ya zo Abuja ya kwana yi masu addu’o’in samun saukin Ubangiji. Ranar wata Juma’a ya mike zaune yace zai sha (tea), farin-cikin mikewar sa wurin Daddy da suaran ‘yan uwa kema kin san ba sai an fada ba, jiki na rawa Haj. Hadiza ta hada shayi mai kauri ta mika mishi. Kai ciwon Aminu harda na shagwaba don ya dade da samun sauki ko don Allurai da magungunan da ake dirka mishi kadai masu tsadar gaske, sai ya rufe ido yana jinsu kurum.
Ba abinda yake son ji irin ya ji Daddy na yi masa ‘yar murya yana rokon sa don Allah ya tashi shi kuma ya aura mai Saratu a gobe. Har president da sauran abokan aiki da abokan arzikan Daddy sun zo duba Al’ameen, haka Dr. Argungu da sauran abokan Daddy na (aikin soja).
Daga Miami, Florida, da duk inda Al’ameen yai aiki ko karatu abokanshi likitoci sun barko don nuna mishi kauna, duk kuma sun ji to bakin Rehab ne da ya kira wayar Aminu Najib ya dauka yace yana kwance a babban asibitin birnin tarayya ba lafiya, kai wannan Asibiti yaga taron jar fata da bai taba gani ba, haka ta bangaren Daddy kusoshin Nigeria sai barkowa suke daga ko’ina cikin kasar mu mai dimbin albarka.
Wani abin dariya sai suyi ta cewa M.A.B na ciwon kirji ne. Idan an fadi haka Haj. Hadiza tayi ta dariya.
A ranar Ihsan tazo a gigice, Babanta ne ya gaya mata Aminu na kwance Asibiti. Ko gayawa Ann bata tsaya yi ba ta zari mota ta taho. Tana sanye da atamfa Holland koriya dinkin Niger, kanta yane da dan mayafi.
Ta isa ga gadon Al’ameen bata ko kula da tarin iyayenshi balle ‘yan uwa ba ta janyoshi ta soma kuka a lokacin yana barci. Haj. Hadiza ta tambayi su Nasir ko wacece? Suka ce suke jin itace Ihsan matarshi, don suma basu taba ganinta ba.
Tayi ta bata baki tace Aminu yaji sauki sosai a hakan ma sai karfin jiki kawai.
A can Asibitin da Intisar take, su Hunainah na tare da ‘yar uwarsu suna jiyya har ta soma taka kafafunta, kar kiso ki ga farin ciki a wurinsu da Anti Saratu.
Maganar farko da Al’ameen yayi shine akan me Haj. Hadiza ta bari aka sace Intisar? Haj. Hadizah tace “kai da baka da lafiya ina kai ina tone-tone? Amma kasan dai babu uwar da zata dauki Da na halal ta kai Daji, duk wahala, duk talauci balle babu daya kanwar biyu�. Sai yayi murmushi.
Ranar Asabar aka sallami Intisar, ita, Anti Saratu, Hunainah da Hidayah suka zarce gida, shi Al’ameen Alfered ya rikeshi yace bai gama farfadowa daga ‘Luv-sick� din nashi ba, kullum tsiyar da yake tayi mai kenan sai yayi biris ya kyaleshi kamar bai san yanayi ba.
Washegari ya mike da safe ya zare masu ledar ruwan ‘drip� da suka makala mishi ya aje bisan gado. Ya dubi inda Ihsan ke ta sharar barci ita da Haj. Hadiza (‘yan jinyar shi kenan kowa na tare da Intisar) a ranshi yace “mun hadu a gaba�. Kafarshi ko takalmi babu ya fita wajen asibitin ya tari machine yace ya kaishi Addis Ababa Crescent.
Masu gadi zuwa ma’aikatan gidan kadan ya rage dariya ta kufce masu ganin Oga ko takalmi babu dare a bayan achaba, ya sauka kuma sai yasa kai zai shige, mai babur yace “Sir, kudina fa?� Gabadaya ya juyo ya shafa aljihunan wandonshi zuwa na gaban riga bai ji ko sisi ba, Major mai baiwa shukokin gidan ruwa bai san sanda ya tintsire da dariya ba, a nashi aljihun ya biya mai machine.
Al’ameen ya juya yace da mai babur ya jira shi, mintuna goma a tsakani ya dawo da mukullan mota (Peugeot 505 Station Wagon) ya dankawa Major yace ya fitar da ita a rumfar adana motoci ya bashi, ya katse dimbin godiya da fatar alkhairin da mutumin ke ta kwarara mishi da cewa, “kayi mun Addu’a, Allah ya bani Halimahh!
Malam Sani Daddy ya umarta da ya bude taron da Addu’a. Bayan an shafa ya dubi Haj. Hadiza yace in Ambasada yayi izni ta fadi labarinta da yadda ta rabu da ‘yarta Fatima har ya tsinta. Ambasada yace ta fada.
Tiryan-tiryan ta fadi tun aurenta da Sarkin Noman Shanono, yadda kishiyar ta Shatu tasa aka sace Saratu suka kai daji. Abinda ya faru da ita bayan wannan har zuwa sanda su Hidayah suka kawo ta gidansu na Riyadh, wahalar da suka sha kan nemanta da ciwon data kwanta kamar bata rayuba har zuwansu Bashir Lagos a lokacin Daddyn yana kulle, sun kuma baro Lagos zuwa Abuja shida iyalinsa fiye da shekaru biyu, su kuma basu san inda suka koma ba har zuwa sanda Hajjo ta sami labarin cewa shi Makarfi ya yi bikin cikar shekarun haihuwarshi sittin a jarida, ta matsawa Hassan ya bincika suka je Korea suka taho da su.
Zuwan su can gidan Daddy da shaida musu da akayi suna Asibiti. Shigowar ta dakin da Daddy ya shiga da kuma abubuwan da ta ji yana fade.
Wallahi ba ‘yata bace, tsintar ta nayi a daji na kawowa Saratu. Hajiyar ka zata tabbatar maka da hakan. Al’ameen don Allah ka mike! Ka mike!! Ba abinda ya hadaka da Saratu da zai hanaku aure�
Kuka yaci karfinsa da ya ga Aminu ko gizau. Ya kifa kai jikin karfen gadon yana ta yi kamar ba tsohon soja ba. Tausayi da dadi ne ya rufe Haj. Haddizah, wasu siraran hawaye suka ziraro mata, hawayen farin-ciki da tausayi duk a lokaci daya.
Ta dibi yadda Allah Al-mussawwiru ke juya masu al’amuran cikin ruwan sanyi, ta kara amincewa lallai shi buwaya ne, gagara mithali. Sai ta matsa jikin gadon Al’ameen ta dubshi sosai. Tausayin shi da kaunar shi babu inda bai bi jini da tsokar jikin ta ba.
Wai fa wannan kaunar diyarta ne ya kayar dashi haka? Ta russuna ta barin hagu, kanta jikin gadon a kife tace.
“Kwarai Al’ameen Saratu, Intissar kuma Fatima ba kanwar ka bace kamar yadda kake tunani, ka tashi don Allah ka tausayawa Intisar da Babanka bisa halin da zai shiga in ya rasaka. Ni ce mahaifiyar Intisar. Mahaifin ta ya rasu ne tun tana Jaririya a dalilin bakin-cikin sace mana ita da a kayi aka kai daji, shine Babanka ya tsinta. Wannan shine gaskiyar al’amarin.
Idan ka mike Al’amin ko a gobe sai mu daura maku aure, in ce ko shikenan? Ba fa abinda ya hadaku da Intissar!� Ta fadi da dan karfi cikin gunjin kuka.
Maganganun har tsakar kwakwalwarsa amon su ke yawo, ya motsa kadan alamar sun dameshi, Alfered ya janyesu yace “ya isa hakanan�.
To Hadiza da Daddy sai aka koma kallon-kallo. Kallo daya yayi wa Haj. Hadiza yasan yaga mahaifiyar Saratu a yau, in banda nauyin shekaru ba zai yarda ba Saratu-Intisar din su ce wannan tsaye a gabansa ba.
Kwanaki goma abinda iyaye da ‘yan uwa ke ta gayawa Al’ameen da Intisar kenan. Har ita kanta Anti Saratu ta gigice rannan da Intisar tayi wani dogon suma kamar bata dawo ba ta shiga fada mata ba abinda zai hanasu aure don babu alakar jini a tsakaninsu. Malam Sani da Goggo Jummai ma ba’a barsu a baya ba wurin nunawa ‘yan gatannan kauna.
Haka Hidayah da Hunainah dake kwana rungume da ‘yar uwarsu a cinya, suna rokonta ta tashi ta auri Yaya Al’ameen, ta basu kulawar da yayye ke baiwa kanne, ta ji dumin Mamarsu itama. Su nuna mata kulawa da kaunar da bata samu ba na kanne mata.
Fatan Anti Saratu kawai samuwar lafiyar Intisar da likita ya ce, ‘Shock� ne kadai ya gigitata ya wargaza mata tunani. Amma a hankali tunaninta yana saisaita kuma tunda ga komi yazo da sauki, danginta sun bayyana a sanda ake tsananin bukatar su.
Ita da Hajiya Hadiza kwana suke bakin su bai yi shiru ba kullum dai zancen kenan. Cikin wannan halin Najib ya kira mahaifiyarsu a waya ya ce,
“Hajiya, kin ce zaki dawo har yanzu kaman an aiki bawa garinsu, amma yanzu ina jin ya dace ki dawo, tunda ga Aminun ki kwance a gadon asibiti ba yadda yake, bai kuma san wanda ke kansa ba?�
Ta ce cikin shesshekar kuka
“Idan ka gan ni a Nigeria to na zo ganin ku ne, amma ni da gidan ubanku har abada! Sai dai ya zaba ko ni ko Saratu da tsinanniyar ‘yar sa. Idan nazo zan baiwa Aminu lafiya ne? Allah ya bashi sauki.�
Najib ya so yayi mata bayani yaga ma bayanin baya da amfani, shin yaya zata ji idan ta ji cewa ‘yar da tafi tsana a duniya ce Dan da tafi so fiye da kowa ke so har ya kamu da ciwon zuciya? Ashe dalilinta na kin Intisar shine don tsinto ta aka yi, kuma tana tsammanin shegiya ce? Wane bayani zai mata ta fahimta a waya? Sai yace “Hajiya ki daina illata Intisar hakannan, don zaki sha mamaki. Don Allah ki gyara halin ki, ki dawo ki ji me ke faruwa cikin rayuwar ‘ya’yan ki?�
Faisal tunda ya fahimci abinda ke faruwa ya bar asibitin, bai kara waiwayar kowa ba, babu kuma wanda ya kara jin duriyar shi cikin asibitin. A lokacin da ake tsammanin shine mutumin da zai fi kusantar Saratun fiye da kowa.
Iyayen na mamakin irin wannan masifaffen so na Intisar da Aminu, gashi ba wani dogon lokaci suka dauka tare ba. So mai neman salwantar da rayuwa kamar a birnin Hindu ai abin mamaki ne.
To Al’ameen da ‘feeling hopes� din da Daddy da Hadiza ke ta bashi ya soma shaida mutane. Ga Addu’o’in da su Baffa ke tayi har Mallam Sidi ya zo Abuja ya kwana yi masu addu’o’in samun saukin Ubangiji. Ranar wata Juma’a ya mike zaune yace zai sha (tea), farin-cikin mikewar sa wurin Daddy da suaran ‘yan uwa kema kin san ba sai an fada ba, jiki na rawa Haj. Hadiza ta hada shayi mai kauri ta mika mishi. Kai ciwon Aminu harda na shagwaba don ya dade da samun sauki ko don Allurai da magungunan da ake dirka mishi kadai masu tsadar gaske, sai ya rufe ido yana jinsu kurum.
Ba abinda yake son ji irin ya ji Daddy na yi masa ‘yar murya yana rokon sa don Allah ya tashi shi kuma ya aura mai Saratu a gobe. Har president da sauran abokan aiki da abokan arzikan Daddy sun zo duba Al’ameen, haka Dr. Argungu da sauran abokan Daddy na (aikin soja).
Daga Miami, Florida, da duk inda Al’ameen yai aiki ko karatu abokanshi likitoci sun barko don nuna mishi kauna, duk kuma sun ji to bakin Rehab ne da ya kira wayar Aminu Najib ya dauka yace yana kwance a babban asibitin birnin tarayya ba lafiya, kai wannan Asibiti yaga taron jar fata da bai taba gani ba, haka ta bangaren Daddy kusoshin Nigeria sai barkowa suke daga ko’ina cikin kasar mu mai dimbin albarka.
Wani abin dariya sai suyi ta cewa M.A.B na ciwon kirji ne. Idan an fadi haka Haj. Hadiza tayi ta dariya.
A ranar Ihsan tazo a gigice, Babanta ne ya gaya mata Aminu na kwance Asibiti. Ko gayawa Ann bata tsaya yi ba ta zari mota ta taho. Tana sanye da atamfa Holland koriya dinkin Niger, kanta yane da dan mayafi.
Ta isa ga gadon Al’ameen bata ko kula da tarin iyayenshi balle ‘yan uwa ba ta janyoshi ta soma kuka a lokacin yana barci. Haj. Hadiza ta tambayi su Nasir ko wacece? Suka ce suke jin itace Ihsan matarshi, don suma basu taba ganinta ba.
Tayi ta bata baki tace Aminu yaji sauki sosai a hakan ma sai karfin jiki kawai.
A can Asibitin da Intisar take, su Hunainah na tare da ‘yar uwarsu suna jiyya har ta soma taka kafafunta, kar kiso ki ga farin ciki a wurinsu da Anti Saratu.
Maganar farko da Al’ameen yayi shine akan me Haj. Hadiza ta bari aka sace Intisar? Haj. Hadizah tace “kai da baka da lafiya ina kai ina tone-tone? Amma kasan dai babu uwar da zata dauki Da na halal ta kai Daji, duk wahala, duk talauci balle babu daya kanwar biyu�. Sai yayi murmushi.
Ranar Asabar aka sallami Intisar, ita, Anti Saratu, Hunainah da Hidayah suka zarce gida, shi Al’ameen Alfered ya rikeshi yace bai gama farfadowa daga ‘Luv-sick� din nashi ba, kullum tsiyar da yake tayi mai kenan sai yayi biris ya kyaleshi kamar bai san yanayi ba.
Washegari ya mike da safe ya zare masu ledar ruwan ‘drip� da suka makala mishi ya aje bisan gado. Ya dubi inda Ihsan ke ta sharar barci ita da Haj. Hadiza (‘yan jinyar shi kenan kowa na tare da Intisar) a ranshi yace “mun hadu a gaba�. Kafarshi ko takalmi babu ya fita wajen asibitin ya tari machine yace ya kaishi Addis Ababa Crescent.
Masu gadi zuwa ma’aikatan gidan kadan ya rage dariya ta kufce masu ganin Oga ko takalmi babu dare a bayan achaba, ya sauka kuma sai yasa kai zai shige, mai babur yace “Sir, kudina fa?� Gabadaya ya juyo ya shafa aljihunan wandonshi zuwa na gaban riga bai ji ko sisi ba, Major mai baiwa shukokin gidan ruwa bai san sanda ya tintsire da dariya ba, a nashi aljihun ya biya mai machine.
Al’ameen ya juya yace da mai babur ya jira shi, mintuna goma a tsakani ya dawo da mukullan mota (Peugeot 505 Station Wagon) ya dankawa Major yace ya fitar da ita a rumfar adana motoci ya bashi, ya katse dimbin godiya da fatar alkhairin da mutumin ke ta kwarara mishi da cewa, “kayi mun Addu’a, Allah ya bani Halimahh!
Malam Sani Daddy ya umarta da ya bude taron da Addu’a. Bayan an shafa ya dubi Haj. Hadiza yace in Ambasada yayi izni ta fadi labarinta da yadda ta rabu da ‘yarta Fatima har ya tsinta. Ambasada yace ta fada.
Tiryan-tiryan ta fadi tun aurenta da Sarkin Noman Shanono, yadda kishiyar ta Shatu tasa aka sace Saratu suka kai daji. Abinda ya faru da ita bayan wannan har zuwa sanda su Hidayah suka kawo ta gidansu na Riyadh, wahalar da suka sha kan nemanta da ciwon data kwanta kamar bata rayuba har zuwansu Bashir Lagos a lokacin Daddyn yana kulle, sun kuma baro Lagos zuwa Abuja shida iyalinsa fiye da shekaru biyu, su kuma basu san inda suka koma ba har zuwa sanda Hajjo ta sami labarin cewa shi Makarfi ya yi bikin cikar shekarun haihuwarshi sittin a jarida, ta matsawa Hassan ya bincika suka je Korea suka taho da su.
Zuwan su can gidan Daddy da shaida musu da akayi suna Asibiti. Shigowar ta dakin da Daddy ya shiga da kuma abubuwan da ta ji yana fade.