Sashe 86
Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta ce in na sake ka ai ban gama cin ribar rayuwata ba, ni fa mayya ce, ko ba haka a ke ce muku ba? Don haka in kaga na sake ka Ya Faisal to nima bana numfashi. Kisa kuma tunda na rigaya na fara akan me zan bari? Bayan barin ba zai shafen wannan dattin na baya ba? Ya yi murmushin da bai shirya ba, ya ce haka ne? To ki je ki kama kurwar wasu man, dole sai tamu?
Ta share hawayen da suke zubo mata tace ai baka sani ba, takun ce tafi ta kowa gardi. Kuma abinda baka sani ba shine mu mayu in muka fara cin daya a gida, bama hakura sai mun cinye sauran duk. Don haka kai ne babba a yanzu, ta kanka zan fara kenan? Sannan in gangaro Nasir, in iso Daddy karami, in gangaro in dawo Faruk sannan Yasir. Sai in koma kan Idris da Furkan. Shima Najib din ba don na koshi ba, sai don yar uwata da ke samu tana lasa sannu a hankali kamin shima ta kayar da shi gaba daya.
Mutun daya kawai zan bari shine Khaleel shima a bisa dalilai biyu;
Na farko kurwar sa ta mun kankanta, makale mun za tayi a makogaro. Na biyu kuma ina da burin saka masa abokantakar kurucciya; shi abokina ne, dan uwa na ne, abokin shawara na ne. Cikin halin kunci, dadi, farin ciki da ukuba da na kasance a raynwa, bai taba juyan baya ba, bai taba goranta mun ba. Bai taba daina so na ba kuma bai taba nunan ni bare ce a gare shi ba.
Ta cika mishi kafar ta mike da gudu ta yi sama da hawayenta da basu bar ambaliya ba. Amma sabida zurfin ciki irin nata sai ta rakabe tayi kukanta mai isar ta ta share idonta, kana ta lallaba ta je ta kwanta a gadon ta.
Idan tace barci ya ziyarci idanunta a yau ita kanta ta san karya ta ke. Wani irin masifar son Faisal da bata taba ji ba ke yagalgala zuciyar ta. Ta kudundune a cikin bargonta tamkar curin alkaki. Gaba daya jikinta kyarma yake kamar ana kada mata gangi, haka a take wani irin sanyi mai huda bargo ya shiga keta tattausar fatar ta zuwa cikin jikin ta, kamin dan lokaci wani zazzafan zazzabi ya rufe ta.
Don haka koda tayi sallar Asubahi bata iya ta cigaba da lazimin da take yi ba har zuwa wayewar gari ba; lallabawa tayi ta koma cikin bargonta da take jin da shi da babu duk daya ne a gareta, domin bai taimaka ba ko kankani wajen rabata da wannan azababben sanyin da take ji.
Wajen karfe bakwai na safe Hidayah ta shiga jan kafarta wai ta tashi suyi mata rakiya bakin mota zasu tafi. Cikin kankanuwar murya ta ce ki yi hakuri, akwai barci mai yawa a kaina Allah ya kai ku lafiya. Muma nan da next week na ke jin zamu taho Abujan, safe journey. Hidayah tayi murnushi kawai ta juya tana sauka daga matattakalar bene, tana ta korafin zurfin ciki irin na yar uwarta, ga dai damuwa fal a bakinta amma ba zata taba bude baki ta fadi ba.
***
A Lagos
A birnin Ikko, cikin maaikatar matatar mai ta kasa (NNPC) Engr. Faisal Bello Makarfi ne jingine jikin tagar ofishin sa yana kallon alumma cikin motocin da ke yawo bisa titi, freely, babu abinda ya dame su. Har yau ya rasa sukunin zuciyarsa ya kuma kasa yankewa kan sa hukunci.
Babu abinda yake tunani kamar kalamun Intisar gareshi a daren jiya, da irin kukan da ta dinga yi a gabansa. Ya ji zuciyarsa a karo na farko tana mai kalubalantar sa musanman in ya tuna abubuwanda Hajiya, Aunty Saratu da Najib suka ce da shi. Ya dace ya yiwa Intisar uzuri cikin alamarin ta, me zata iya yi akai? Me ta yi na hakika wanda ya zamanto cin amana, ko yaudara?
Na farko dai ta so Alameen a sanda bata da kowa, ya nuna kulawa da damuwa da rayuwar ta a zuwan dukkanin su basu san junansu ba. Baya da haka ma wace diya mace ce zata yi arba da Alameen Bello, har ya furta yana son ta tace bata son shi? “Babu! Wannan karya ne!�
Shi kan sa ya sani wannan a cikin jinin Alameen ne, yana daga cikin baiwarwakin da Allah yayi masa watau farin jinin mata, tun yana sakandire babu irin damben da yammata basa yi a kan shi, balle a lokacin da yake cikakken mutum? Hakannan ya san Intisar tana da wani hali na girmama duk mai kaunar ta, da kaunar duk mai kaunar ta.
Ta so Alameen a cikakkun shakarunta na teenage a lokacin da ta san menene so na hakika kuma mece ce kauna?
Tana kaunar sa matsayinsa na Yayan ta mai sonta, mai kulawa da ita da alamarin ta, a matsayin sa na Yayan da suke uba daya. Sabanin Alameen da ya zo mata a matsayin wani bako da bata sani ba.
Mutuwa dai guda daya ce, sai dai hanyoyin ta yawa garesu. To hanyar mutuwar Alameen ta kasance hakan, akan turbar cika burin zuciyar shi na so da kaunar Intisar amma ba Intisar ce ta kashe shi ba. To ta kashe shi a kan me? Bayan shine kadai wanda zuciyarta ke so da kauna? Wani kishi kuma ya zo ya tokareshi a kahon zucci. Dai-dai lokacin da Tajuddeen ya bankado kofar shi ya shigo.
Ya juyo da sauri ya dube shi yayinda shi kuma ya watsa mai katunan da ke hannun shi a fuska, ya ce meye haka na ke shirin gani? Faisal are you in your full-sense? (Kana cikin cikakken hankalin ka)
Ya russuna ya dau daya cikin katinan daya watso mishi, katin gayyatar auren su ne Ronke ta bugo take rabawa cikin maaikatar inda itama nan take aiki. Yayi murmushi cikin bagararwa yace to meye abin mamaki? Ba ni na ce ina sonta ba?
Ya bishi da kallon ya ga mahaukaci ya ce ko ka san Ronke ita ta kashe mijinta da hannun ta, don kawai ta samu damar auren ka?
Yayi dariyar shi mai ban shaawa data kara kular da Tajon ya ce to ai ka ji shi bata son sa, shi yasa ta kashe shi, ni ko akan me zata kashe ni? Ni da ta ke so shekaru dai-dai har takwas? Tajuddeen ya mike yasa hannun shi cikin aljihu yana girgiza kai yace
alright, Allah ya baka saa Faisal ya fita bayan ya bugo masa kofar ji kake garam.
Yayi tsaki a ransa yace kaga mun mutum da daukar dala ba gammo.
A karshen satin ya iso gida cike da zullumi, ya kara ramewa, ya kara lalacewa alamun rashin cikakkar nutsuwa ya game koina a tare da shi. Babban zullumin sa yau ne rana ta karshe da Daddyn ya deba mishi don jin amsa ta karshe daga gareshi tun bayan fatattakar zancen Ronke da ya yi.
Ya tabbatar mai daga ranar in bai zo mai da wata kwakkwarar madafa ba auren shi da Ihsan karshen satin ya tabbata, zai daura, duk da ita Ihsan din bata nan ya jirata ta dawo.
Idan har akwai abinda yafi daga masa hankali a rayuwa to wannan maganar da Daddy ke ikrari ne. Yana zaune falon Aunty Saratu wadda ke ta fama da fitinar Alameen karami dake ta fatali da komi na falon wai shi a kai shi gidan Baba Najib, ko kallon inda yake bata yi ba, balle ta bashi lemu ko madarar da ta saba bashi idan yana cikin bacin rai don ita yanzu Faisal ya daina bata tausayi haushi kawai yake bata.
Wai Intisar din ta, ita ce ake lallamin Faisal ya aura yana bijirewa kamar an ce da shi rasa masoyi ta yi? Tayi kwafa ta ce sai ka isa falon ya fito, tun dazu dama ya ke tambayar isowar ka.
Ya mike tamkar wanda kwai ya fashewa a ciki, ya nufi sassan Daddyn zuciyar shi na harbawa.
Gwarzon Uba, namiji sauran mazan jiya, na zaune cikin lallausar carpet din karamin falon hutawar shi yana sauraron labarum duniya daga muryar Amurka (Voice of America), a gefen shi Hajiya Nafi ce tana ninke wasu kayan Daddyn da aka wanke. Faisal yayi sallama cikin muryar shi mai cike da ladabi da rashin kuzari, gaba daya suka amsa mai sallamar tare da kai duban su gare shi.
Cikin su babu wanda zuciyar shi bata motsa ba da ganin karin ramar da yaron ke tayi a kullum, ya kasa hutar da zuciyar shi, ya tsayar da ita wuri daya ta samu abinda ta ke so. Cikin yayan su baki daya basu taba ganin jarumi kuma mai fin karfin zuciya irin Faisal ba.
Ga mamakin sa, abinda bai zata ba Daddyn murmushi ya sakar mishi mai kwantar da hankali ya ce bakin Ikko ne, sai yanzu aka iso? Ya dan ji dadi shima ya yi murmushin, kansa a sadde ya ce eh wallahi, an samu delay ne na isowar jirgi mai zuwa Abuja, da nace zan bari sai gobe to kuma sai naji duk hankalina yayo nan din suka cigaba da hirar su kan aikin shi da karin girma da ya samu, wanda Daddyn ya gani a (television) daren jiya cikin labarun NTA na kasa.
Ko kadan bai sako zancen da Faisal din kewa dari-dari ba. Sai da Faisal din yace kwanannan Nigeria zata yi exporting crude oil (fitar da man fetur) zuwa Belgium kuma shine wanda alamarin ke hannun sa, don haka cikin sati na sama yake sa ran tafiya Belgium din zai yi a kalla sati biyu domin yin wasu bincike.
Daddy ya maida fuskar shi ta koma ta manyantaka kamar yadda yake yi a duk lokacinda zai masu magana mai muhimmanci ya ce Faisal cikin babbar muryar da ta kada yayan hanjin sa
ina maganar mu ta kwana?
Ya kara sunkuyar da kai ya rasa bakin magana sai zufa da ke ketowa takoina a sassan jikin shi. Hajiya ta yi tsaki ta ce kaima da laifinka Baban su Khalil. Har yaushe zakayi ta biye mishi yana yi ma yawo da hankali sai kace shi din karamin yaro ne?
Ta share hawayen da suke zubo mata tace ai baka sani ba, takun ce tafi ta kowa gardi. Kuma abinda baka sani ba shine mu mayu in muka fara cin daya a gida, bama hakura sai mun cinye sauran duk. Don haka kai ne babba a yanzu, ta kanka zan fara kenan? Sannan in gangaro Nasir, in iso Daddy karami, in gangaro in dawo Faruk sannan Yasir. Sai in koma kan Idris da Furkan. Shima Najib din ba don na koshi ba, sai don yar uwata da ke samu tana lasa sannu a hankali kamin shima ta kayar da shi gaba daya.
Mutun daya kawai zan bari shine Khaleel shima a bisa dalilai biyu;
Na farko kurwar sa ta mun kankanta, makale mun za tayi a makogaro. Na biyu kuma ina da burin saka masa abokantakar kurucciya; shi abokina ne, dan uwa na ne, abokin shawara na ne. Cikin halin kunci, dadi, farin ciki da ukuba da na kasance a raynwa, bai taba juyan baya ba, bai taba goranta mun ba. Bai taba daina so na ba kuma bai taba nunan ni bare ce a gare shi ba.
Ta cika mishi kafar ta mike da gudu ta yi sama da hawayenta da basu bar ambaliya ba. Amma sabida zurfin ciki irin nata sai ta rakabe tayi kukanta mai isar ta ta share idonta, kana ta lallaba ta je ta kwanta a gadon ta.
Idan tace barci ya ziyarci idanunta a yau ita kanta ta san karya ta ke. Wani irin masifar son Faisal da bata taba ji ba ke yagalgala zuciyar ta. Ta kudundune a cikin bargonta tamkar curin alkaki. Gaba daya jikinta kyarma yake kamar ana kada mata gangi, haka a take wani irin sanyi mai huda bargo ya shiga keta tattausar fatar ta zuwa cikin jikin ta, kamin dan lokaci wani zazzafan zazzabi ya rufe ta.
Don haka koda tayi sallar Asubahi bata iya ta cigaba da lazimin da take yi ba har zuwa wayewar gari ba; lallabawa tayi ta koma cikin bargonta da take jin da shi da babu duk daya ne a gareta, domin bai taimaka ba ko kankani wajen rabata da wannan azababben sanyin da take ji.
Wajen karfe bakwai na safe Hidayah ta shiga jan kafarta wai ta tashi suyi mata rakiya bakin mota zasu tafi. Cikin kankanuwar murya ta ce ki yi hakuri, akwai barci mai yawa a kaina Allah ya kai ku lafiya. Muma nan da next week na ke jin zamu taho Abujan, safe journey. Hidayah tayi murnushi kawai ta juya tana sauka daga matattakalar bene, tana ta korafin zurfin ciki irin na yar uwarta, ga dai damuwa fal a bakinta amma ba zata taba bude baki ta fadi ba.
***
A Lagos
A birnin Ikko, cikin maaikatar matatar mai ta kasa (NNPC) Engr. Faisal Bello Makarfi ne jingine jikin tagar ofishin sa yana kallon alumma cikin motocin da ke yawo bisa titi, freely, babu abinda ya dame su. Har yau ya rasa sukunin zuciyarsa ya kuma kasa yankewa kan sa hukunci.
Babu abinda yake tunani kamar kalamun Intisar gareshi a daren jiya, da irin kukan da ta dinga yi a gabansa. Ya ji zuciyarsa a karo na farko tana mai kalubalantar sa musanman in ya tuna abubuwanda Hajiya, Aunty Saratu da Najib suka ce da shi. Ya dace ya yiwa Intisar uzuri cikin alamarin ta, me zata iya yi akai? Me ta yi na hakika wanda ya zamanto cin amana, ko yaudara?
Na farko dai ta so Alameen a sanda bata da kowa, ya nuna kulawa da damuwa da rayuwar ta a zuwan dukkanin su basu san junansu ba. Baya da haka ma wace diya mace ce zata yi arba da Alameen Bello, har ya furta yana son ta tace bata son shi? “Babu! Wannan karya ne!�
Shi kan sa ya sani wannan a cikin jinin Alameen ne, yana daga cikin baiwarwakin da Allah yayi masa watau farin jinin mata, tun yana sakandire babu irin damben da yammata basa yi a kan shi, balle a lokacin da yake cikakken mutum? Hakannan ya san Intisar tana da wani hali na girmama duk mai kaunar ta, da kaunar duk mai kaunar ta.
Ta so Alameen a cikakkun shakarunta na teenage a lokacin da ta san menene so na hakika kuma mece ce kauna?
Tana kaunar sa matsayinsa na Yayan ta mai sonta, mai kulawa da ita da alamarin ta, a matsayin sa na Yayan da suke uba daya. Sabanin Alameen da ya zo mata a matsayin wani bako da bata sani ba.
Mutuwa dai guda daya ce, sai dai hanyoyin ta yawa garesu. To hanyar mutuwar Alameen ta kasance hakan, akan turbar cika burin zuciyar shi na so da kaunar Intisar amma ba Intisar ce ta kashe shi ba. To ta kashe shi a kan me? Bayan shine kadai wanda zuciyarta ke so da kauna? Wani kishi kuma ya zo ya tokareshi a kahon zucci. Dai-dai lokacin da Tajuddeen ya bankado kofar shi ya shigo.
Ya juyo da sauri ya dube shi yayinda shi kuma ya watsa mai katunan da ke hannun shi a fuska, ya ce meye haka na ke shirin gani? Faisal are you in your full-sense? (Kana cikin cikakken hankalin ka)
Ya russuna ya dau daya cikin katinan daya watso mishi, katin gayyatar auren su ne Ronke ta bugo take rabawa cikin maaikatar inda itama nan take aiki. Yayi murmushi cikin bagararwa yace to meye abin mamaki? Ba ni na ce ina sonta ba?
Ya bishi da kallon ya ga mahaukaci ya ce ko ka san Ronke ita ta kashe mijinta da hannun ta, don kawai ta samu damar auren ka?
Yayi dariyar shi mai ban shaawa data kara kular da Tajon ya ce to ai ka ji shi bata son sa, shi yasa ta kashe shi, ni ko akan me zata kashe ni? Ni da ta ke so shekaru dai-dai har takwas? Tajuddeen ya mike yasa hannun shi cikin aljihu yana girgiza kai yace
alright, Allah ya baka saa Faisal ya fita bayan ya bugo masa kofar ji kake garam.
Yayi tsaki a ransa yace kaga mun mutum da daukar dala ba gammo.
A karshen satin ya iso gida cike da zullumi, ya kara ramewa, ya kara lalacewa alamun rashin cikakkar nutsuwa ya game koina a tare da shi. Babban zullumin sa yau ne rana ta karshe da Daddyn ya deba mishi don jin amsa ta karshe daga gareshi tun bayan fatattakar zancen Ronke da ya yi.
Ya tabbatar mai daga ranar in bai zo mai da wata kwakkwarar madafa ba auren shi da Ihsan karshen satin ya tabbata, zai daura, duk da ita Ihsan din bata nan ya jirata ta dawo.
Idan har akwai abinda yafi daga masa hankali a rayuwa to wannan maganar da Daddy ke ikrari ne. Yana zaune falon Aunty Saratu wadda ke ta fama da fitinar Alameen karami dake ta fatali da komi na falon wai shi a kai shi gidan Baba Najib, ko kallon inda yake bata yi ba, balle ta bashi lemu ko madarar da ta saba bashi idan yana cikin bacin rai don ita yanzu Faisal ya daina bata tausayi haushi kawai yake bata.
Wai Intisar din ta, ita ce ake lallamin Faisal ya aura yana bijirewa kamar an ce da shi rasa masoyi ta yi? Tayi kwafa ta ce sai ka isa falon ya fito, tun dazu dama ya ke tambayar isowar ka.
Ya mike tamkar wanda kwai ya fashewa a ciki, ya nufi sassan Daddyn zuciyar shi na harbawa.
Gwarzon Uba, namiji sauran mazan jiya, na zaune cikin lallausar carpet din karamin falon hutawar shi yana sauraron labarum duniya daga muryar Amurka (Voice of America), a gefen shi Hajiya Nafi ce tana ninke wasu kayan Daddyn da aka wanke. Faisal yayi sallama cikin muryar shi mai cike da ladabi da rashin kuzari, gaba daya suka amsa mai sallamar tare da kai duban su gare shi.
Cikin su babu wanda zuciyar shi bata motsa ba da ganin karin ramar da yaron ke tayi a kullum, ya kasa hutar da zuciyar shi, ya tsayar da ita wuri daya ta samu abinda ta ke so. Cikin yayan su baki daya basu taba ganin jarumi kuma mai fin karfin zuciya irin Faisal ba.
Ga mamakin sa, abinda bai zata ba Daddyn murmushi ya sakar mishi mai kwantar da hankali ya ce bakin Ikko ne, sai yanzu aka iso? Ya dan ji dadi shima ya yi murmushin, kansa a sadde ya ce eh wallahi, an samu delay ne na isowar jirgi mai zuwa Abuja, da nace zan bari sai gobe to kuma sai naji duk hankalina yayo nan din suka cigaba da hirar su kan aikin shi da karin girma da ya samu, wanda Daddyn ya gani a (television) daren jiya cikin labarun NTA na kasa.
Ko kadan bai sako zancen da Faisal din kewa dari-dari ba. Sai da Faisal din yace kwanannan Nigeria zata yi exporting crude oil (fitar da man fetur) zuwa Belgium kuma shine wanda alamarin ke hannun sa, don haka cikin sati na sama yake sa ran tafiya Belgium din zai yi a kalla sati biyu domin yin wasu bincike.
Daddy ya maida fuskar shi ta koma ta manyantaka kamar yadda yake yi a duk lokacinda zai masu magana mai muhimmanci ya ce Faisal cikin babbar muryar da ta kada yayan hanjin sa
ina maganar mu ta kwana?
Ya kara sunkuyar da kai ya rasa bakin magana sai zufa da ke ketowa takoina a sassan jikin shi. Hajiya ta yi tsaki ta ce kaima da laifinka Baban su Khalil. Har yaushe zakayi ta biye mishi yana yi ma yawo da hankali sai kace shi din karamin yaro ne?