← Book details Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 71 OF 90

Sashe 71

Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Na yafe maka duniya da lahira. Ina rokon Allah yayi maka rahmah da gafara!. Wasu hawayen suka zubo, irin wadanda basa saukaka kunci da radadin mutuwar da a zuciyar mahaifansa! Balle da irin Alameen Bello! Ba iyayen sa kadai ba, duk ma wanda wata muamala ta taba hada shi da shi koda sau daya ne, dole ya girgiza da gushewar sa a doron kasa.

A lokacin ne ye tuna wannan ba lokacin kuka bane, lokaci ne na karfafa zuciya, lokaci ne na nunawa Alameen din sa gata na karshe a rayuwarsa, wanda ba komi bane illa Addua da nema masa rahmar Ubangiji.

Wani Imani ya zo masa. Ya yunkura ya mike ya doshi kofa ya manta babu ko kwakkwarar suttura a jikin sa. Aunty Saratu ta mike bata ko ganin abinda yake gabanta illa ta mika masa babbar riga da takalmi, suka fito harabar gidan a tare.

Har zuwa sanda Daddy da mukarrabansa suka shiga mota suka bar gidan, bata ko motsa daga inda take tsaye ba, hakannan hawaye ko digo daya bai fito daga idanuwan ta ba. Ta kasa gasgata alamarin, ta kasa gaskata abinda kunnuwan ta suka jiyo mata, ta kasa amincewa da wai Alameen ya rasu! Ta dauki alamarin a matsayin irin mugayen mafarke mafarken nan da dan adam ke yi ya farka cikin dan lokaci.

Allah kadai yasan tsawon awonnin da ta yi a tsaye a wajen tamkar sassakakken gunki ko gungumen itace. Har zuwa lokacin da motar da ke dauke da gawar Alameen tare da motocin da ke biye da ita suka cika harabar gidan. Ta daga ido taga wai yau Alameen ne ake fiddowa da sunan babu wata gaba dake motsi a jikinsa kuma babu numfashi. Abin mamaki, babu ko kwarzane a jikin sa, babu ko digon jinni a jikinsa tamkar mai barci kai baka ce accident yayi ba. Fuskarsa da a kullum ke cike da ilhama da cikar zati, tare da kwarjini na musamman a yau ma hakan ta ke, baya ga wani haske da annuri da ya kara tamkar a ce Alameen ya bude kyawawan idanuwan sa ya amsa.

Ta dai tabbatar wannan zahiri ne ba mafarki ba ne sai ta yanke jiki ta fadi, yayin da jinni ya soma bin kafafunta ba kakkautawa. Babu ko tantama dan yaron cikin da take dauke da shi ne ya bi dan uwan sa nan take.

How much do you like this story?
5/14/22, 09:27 - Ummi Tandama😇: ____________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book four

*@Takori*

Page3ï¸âƒ£

Kamin wani dan lokaci labarin mutuwar Alameen Bello yayi tambari a cikin Abuja da wajenta ta kafofin yada labarai, haka gidan redion BBC tuni sun watsa labarin zuwa Jackson Memorial dake (Florida), da Meritime dake birnin Miami, haka sashen Hausa, redion Nigeria Kaduna, suma labarinsu a dan tsukin kenan.

Kamin kace meye wannan gidan Bello Makarfi babu masaka tsinke balle dai-dai da isowar shugaban kasa da yan majalisar sa, gami da babban limamin masallacin Abuja wanda zai jagoranci sallar. Daya bayan daya samarin Brigedier ke isowa, wani ya samu sallar wani bai samu ba, (irin su Faisal da Najib da ke garuruwa masu nisa).

Cikin wannan halin ne direbanta ya karaso da ita gidan cikin motarta (Volvos6) ko inda zasu tusa kan motar babu a layin, don haka tace da shi ya ajiye ta a nan farkon layin. Ta fito duk jikinta nade cikin laffaya koriya shar, idanuwan ta shabe-shabe da hawayen da ta ke jin har abada bazata daina zubar da su ba, illa a yau ta ji wani sabon imani ya shige ta, tsoron Allah da takwah ya karu a zuciyarta.

Ta yi iya kokarinta don ganin hawayenta ko daya bai diga a kasa ba, kokari take wajen ganin ta maida su, Allah Sarki! Wai Aminun ta ya tafi, Aminun ta mai sonta, mai yi mata biyayyar da cikin yayanta kaf, babu mai yi mata kwatankwacin ta. Ya tafi, cike da bakin-cikinta na rashin kyautayi da tausayi a gareshi, ya tafi, cike da buri na karshe a rayuwarsa wanda bata taimaka masa ya cikashi ba, ya tafi, ba tare da samun wata daddadar kalma ko daya daga bakinta ba a lokacin da yake tsananin bukatar hakan. Ya tafi, yana mai rokonta wata alfarma wadda bai taba nema daga gareta ba.

Dama ya ce rashin amincewarki na nufin alamura da dama ckin rayuwa ta. Da ma yace in kin so, zan iya murmurewa kamar ban taba yi ba, haka in kin so zai iya zama ajalina! Wasu hawayen suka shararo mata.

A yau Aminun da take so fiye da kowa da komai a duniya, hada da rayuwarta kuwa, ya tafi, akan buri da soyayyar wadda ta ki jini, ta tsana ta ke kuma gaba da ita fiye da mutuwar ta. In haka ne ita dame tayi riba a kiyayyar da ta ke wa yarinyar?

Ta na raye a doron kasa, za kuma tacigaba da rayuwarta tamkar kowa har zuwa lokacinda ita ma nata ajalin zai zo. Ashe duniyar ba komi ba ce? Ashe duniyar ba madawwama ba ce? Duk wata daukaka, soyayya, dukiya, ilmi, gami da gata basa hana mu komawa ga mai kowa mai komi?

Ta ci burirrika da yawa a rayuwar ta a kan Alameen dinta, taci burin ganin jikokinta daga gareshi, ta ci burin ya mallake komi na Daddy Makarfi, ta ci burin ya biye mata su sake korar Saratu su gina kansu, su tsere ma saa, suyi wa kowa fintinkau.

Bata so ya hada rayuwa da tsintacciya mara asali, bata so ya hada rayuwa da wadda ba kowa bace baa kuma san ko yar waye ba, bata so Saratu ta more shi, ba ta so Saratu ta rabe shi. To a yau ya tafi ya bar mata duniyar bakidaya. Cike da kuncin da soyayyarta ta uwa, bata yi kokarin yaye mishi ba. Cike da kucin da soyyar da take ikirarin yi mishi bata taimaka ba ko kankani wurin fidda shi daga halin ukubar da zuciyarshi ke ciki ba.

Ta sa habar zaninta ta share hawaye da majina a tare, zuciyarta na suya da kuna, gangar jikinta na kaduwa. Ta russuna ta kai hannunta na dama ta yaye farin kyallen da yai mata shamaki da kyakkyawar fuskar sa. Fuskar shi fes, tamkar bai taba dandanar wani bakin ciki a rayuwarsa ba. Babu ko kwarzane a jikinsa. Karfin imanin da ya kara ratsata shi ya bata damar bude Alkurani mai tsarki ta shiga karanta masa tare da sauran yan uwansa da mahaifinsa.

A lokacin Ado direba ya sauke Ihsan a gidan, ta soma dara mutane tana shigowa cikin falon, sai ta tsaya sororo idanuwan ta a kan Aminun ta, nannade cikin farin kyallen da idonta ke ganinshi bakkirin. Wata juwa da ta shiga kwasarta ta soma ganin mutanen sun zama bibbiyu uku-uku, har zuwa lokacin ta kasa gasgata abinda ake ankarar da ita.

Hajiya ce ta mike ta kamo hannunta, ta mika mata wani bangare na Alkurani da a ke karantawa, a lokacin ne kowa ya lura da jinin daya yanke yake malala a kasa kamar da bakin kwarya, kana ta fada jikin makarar ta kankeme shi jikinta na wani irin kyarma ta ce yaya za kai min haka? Yaya zanyi da babyn ni kadai Alameen bayan kace tare za muke rainon sa? Yaya zanyi da rayuwar bayan na sha gaya maka in ka bar ni bazan kara rayuwa mai kyau ba? Bazan iya amfanawa kaina komi ba?

Kai da kace min Kaduna zaka ka dawo, muje nemon auren Intisar din ka, na riga na gama yi muku shirin tafiya honey moon Miami! A cikin gidanmu na da Alameen yaya zakayi mana haka? A yayinne idnnuwanta suke shiga lunshewa da kansu, kamin ta bingire a jikin shi kamar mai barki. Babu wanda bata baiwa tausayi a wajen ba.

Dr. Hajjo ce da Goggo Jummai suka kinkime ta suka sa a motan Hajjon suka yi asibiti da ita. Jinin da ke fita jikinta ya balain gigita Aunty Hajjo, rokon ta Allah, rokon ta kada Ihsan ciki gareta yake ficewa kaman Anti Saratu, don haka ta ke kwarara gudu kamar ta tashi sama bata damu da zagin da motocin da ke gabanta da bayanta ke aiko mata ba, yayinda Goggo Jummai ke rungume da ita a bayan motar zuwa National Hospital inda akayi admittin din Aunty Saratu.

Yafiya ta uwa da uba, albarka ta uwa da uba tare da adduar neman Rahamar Ubangiji daga bakin da baya da kaico, bakin uwa, Alameen ya same shi daga bakin mahaifansa. Yo me yafi wannan dadi? Hajiya bata tashi tsinkewa gabadaya da alamarin Sarki Allah ba, sai da aka zo fita da Alameen dinta zuwa gidan sa na gaskiya. A nan ne ta ce bata san wannan ba. Ta ruga ta rike shi tamau da karfin da kowa ya tabbatar ba nata bane.

Daga Najib, Yasir, Bello har Faisal, watsar dasu tayi bakidaya da sukayi kokarin rabata da makarar dake dauke da Alameen dinta. Ta shiga surutu wadanda kowa ya tabbata baa hankalinta take yin su ba.

“Kana fitowa na dauki waya in gaya maka cewa na amince, kazo ka daukeni muje gaban mahaifin ka in nema maka aurenta. Shine ban samu layin ba. Na zauna da niyyar gobe in taho da kaina, sai kawai na ji a radio wai kayi hatsari. Don Allah ka dawo, wallahi da albarka ta da kake nema kaje ka auri Intisar.

Na yarda, na kuma amince da abinda a da, naki amincewa da gan-gan cewa ita din yar baiwa ce, ba duk yayane irin ta ba, ba duk yaya ne Allah yayi wa nasibobin da yayi mata ba, ba duk yaya mata ne masu hakurin ta ba. Na yarda, na amince ta zamo uwar yayanka, na tabbata suma yayan zasu zamo nagari, kuma masu biyayya da yakanah tamkar ku. Ko asirin da nayi mata a baya, ba da son raina ne ba, illa Hajiya Suwaiba da ta tursasani wai in ba hakaba watarana akan ta Babanku zai rabu da ni. Yayana, zan daina jin diminku duk Saratu zata kwace ku da kinibibinta.
Chapter 71 · 0% Book details