Sashe 55
Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shima Daddy ya kwashe duk yadda ya tsinto Saratun a dokar daji a kan hanyarsa ta zuwa Kano daga Kaduna domin halartar (Seminar) ya kawowa Saratu, rokon shi da tayi su rufe sirrin a ce ‘yar ta ce har illa Masha-Allahu.
Yadda suka gayawa ‘ya’yan shi cewa haihuwa tayi haka uwar su saida suka yi alkawarin cewa duk rintsi ba zata fada ba. Brigedier yai shiru na ‘yan dakikai kana ya cigaba.
“Bayan wannan ban san komai ba. Na yi zaton Saratu karama na Riyadh, ashe wai tana gidan tana aiki a sassan masu aiki. Allah ya gani ban taba sani ba har zuwa dawowar Saratu gidana, da yake mun sami sabani na lokaci mai tsawo hakannan ni ba mazauni bane kwata-kwata.
Na dawo daga tafiya muna hirar fahimtar juna da iyalina kamar yadda muka saba, a lokacin Saratu ce min tayi Intisar tazo hutu ne daga makarantar da muka kaita a can Riyadh, inda har kika ce kin ganta Haj. Hadiza. Aminu ya shigo, yadda ya nuna kwata-kwata bai taba sanin Intisar ‘yar gidan bace.
Ita ta rika fadar wasu maganganu da dukkanmu bamu gane ba amma…sai ya dubi Intisar da murmushi, ta kau da kai ta sunne fuskarta da karfi jikin Antinta. Shi ko gogan sai ya kara lumshe ido yana dubarta da dukkan so da duk wata kauna da da namiji ke iya mallakawa diya mace, ba abinda ya dameshi da iyayen su dake zazzaune, suruki zuwa matar shi ta aure.
Daddy ya cigaba da cewa “amma ke Intisar na ji kin ce ne wai ashe Al’ameen ne nawa na Miami? Amma har kuke shirin aure? Sauran duk ban ji ba don haka daina jin kunya. Kai kuma Al’ameen kace Saratu ta maka karya, daga nan kuma duk kuka susuce kuka susuta mu. To kuma bayan kun ji ana cewa duka babu alakar Jini akwai aure shine ko kunya babu kuka karkade riguna kuka taso daga gadon asibiti, wato mu zo muyi muku auren ko?
Sannan kai Aminu karyar me Saratu ta yi maka?�
Gaba daya falon aka sa dariya, Hunainah har da hawayenta jage-jage inka dauke Faisal da ‘yar Argungu. Shi kansa Dr. Argungu yayi murmushi kuma hakika labarin ya tsuma shi. Baya shakkar wadannan mutane masu cikar mutunci nada nufin cutar ko cin zarafin ‘yarshi illah al’amarin Intisar da Aminu Allah ne ya tsarashi.
Aminu ya dubi Haj. Hadiza da girmamawar da bata kwatantuwa yace
“Maman su Hidayah karyar da yarinyar nan ta shirya min har ta wuce hankali. Wai Babanta ne ya siyarwa Haj. Ita tayi mata ayyuka, nace yana ina? Wai yana fita ranar da ya kawota mota ta bigeshi ya mutu, uwar ta kuma bata san inda take ba wai dama foreigner ce, wai talauci ne ya ishesu suka sayar da ita.
A hakan kuma sai gata tana min karatun kimiyya mai inganci, tun daga nan na sinsino karya take, na dai bita ne kawai da yadda take so don a zauna lafiya.
Akwai sanda haka kawai na yi tunanin ko gudowa ta yi daga garin su akan maza? Don ko sallama nayi mata bata amsawa amma in mai aikin Hajiya ce (Dela) sai ta amsa�. Nan ma aka sake yin dariya. Ya ce
“Na taba ganin hoton Hidayah da Hunainah a hannun ta, ina gani nace wadannan kannen ta ne, domin kamar ta isa. Amma a rashin sanin dukkanmu, tace da ni makaranta kurum ta hadasu amma ko Mamar su kamar an tsaga kara suke�. A nan kuma murmushi aka yi.
Al’ameen ya yi shiru na dan lokaci cikin wani tunani, a lokacin sautin muryar shi ya karye gabadaya. Ya dubi Anti Saratu yayi murmushi ya sadda kanshi kasa cikin jin nauyi ya ce,
“Na taso da kiyayyar Intisar diyar Anti Amarya, a dalilin son da Daddy ke mata, ban ga wanda akaiwa hakan ba cikin su baki daya bayan ni, amma wannan son ya zarce nawa.
A da, Daddy na sona fiye da kowa a gidan, amma tunda aka ce an haifi Intisar a kuruciyata sai nayi tsammanin Daddy ya daina sona.
Babu wani nau’in azaba da ya zo min a rai da ban gana mata ba, amma Intisar so na take bata kuma guje ni ba, kullum sai ta yi ta leke na. Idan na juyo muka hada ido sai ta zura da gudu dakin Mamarta.
Nayi ball da ita domin ta karye, ko ta targade ta daina wannan tafiyan nata kaman ta mage tun tana mitsitsiyar ta amma ba don ta makance ba. A kuruciyata, ban taba tsanar kaina irin ranar ba. Na bar gida a dalilin bakin-cikin abinda nayiwa Intisar haka agabadayan tsayin rayuwata 15 years a Miami, Intisar nake tunawa da halin da na barta ciki.
Yana daga abinda ya dugunzumo zuciyata ga son dawowa, don kawai in ga Intisar in nemi gafarar ta. Abin haushin, Hajiyata ta boye min gaskiyar inda take, don kar inje ko don kar ince tayi ba dai-dai ba? Haka su Najib ban san dalilinsu na boye min ba, kodayake ban tambayesu ba, suma kuma basu ce min ba.
Hajiya ce tayi sanadin da naje kitchen (Madafi) kamar yadda tayi sanadin da na nakasta ta. Zuwan da yayi sanadiyyar kasancewana dumu-dumu a kaunar yarinyar da ban sani ba, kawai na sa mata suna halimah, ashe intisar ce kanwar Faisal diyar Anti Amarya, kuma ‘yar wasu? Kai abin da mamaki�. Kowa sai murmushi.
Dr. Argungu ya dan zamo daga cikin kujerarsa yayi gyaran murya duk hankali ya koma kansa aka nutsu ana sauraron sa yace.
“To a madadin kawun Al’ameen ina nemawa dana Al’ameen alfarmar auren Intisar a hannun ka Daddyn Intisar koko a hanun su Bashir Sambo ne?� Hajjo ta yi karaf tace
“Ina! A hannun Daddy Makarfi ne, har yanzu wannan sunan “Saratu Bello Makarfi� babu mai kankareshi. Mu kam Ameenu shine namu, don haka mun bayan alfarmar Dr. Argungu.�
Daddy ya sunkuyar da kai tabbas nauyin Argungu yake ji, amma a zahiri yafi kowa farin-ciki. Ya dade da wannan burin a rayuwar sa don dai ba yadda zai yi ne. Kamin ya sani abin furtawa Ihsan ta fasa kara mai firgitarwa ta soma yiwa Babanta kuka tana masifar baya kaunar ta ita dama Ann ce kadai mahaifiyarta. Kuka take wurjanjan tana neman fita daga falon amma Anti Saratu da Hajjo suka riketa tamau.
Intissar ta mike sauran kannenta suka mara mata baya kamar wasu ‘body-guards� dinta, harta kai bakin kofar fita falon ta juyo Idanunta sun kada tamkar an watsa masu dakakken barkono, wani tukuki yazo ya tokareta a kahon zuci, kallon da tabi kowa dashi tamkar ba ita ba, ba kowa take tunani ba a wannan lokacin face kuruciyarta da al’ameen dan Haj. Nafi.
How much do you like this story?
5/10/22, 21:33 - Ummi Tandama😇: ____________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book three
*@Takori*
Page6ï¸âƒ£
Ta zargi kanta ta tsani kanta duk a lokaci daya ta kuma kalubalanci zuciyarta da so da kaunar Al’ameen. Idanunta gab suke dasu tsiyayo da kwallar da ta kasa kwarara balle taji sanyi-sanyin azabtuwar da kirjinta keyi¸duk da haka tayi murmushi ta girgiza kai ta koma ta russunawa Dr. Abubakar Argungu ta ce,
“Don Allah Baban Anti Ihsan kada ka kara fadin wannan maganan. Alkawarine na riga na yi tuntuni ba abinda zai kara hadani da Jinin Haj. Nafi ko a Lahira balle aure? Da nasan ma Al’ameen dan ta ne wallahi ko gaisuwa…� sai ta rushe musu da matsanancin kuka.
Duk falon yayi tsit sai da tayi mai isarta tukunna ta nayi tana share hawaye da majina da gefen mayafinta.
Tamkar anyi masa allurar karfi, Al’ameen wanda ke sauraronta cikin rashin fahimtar me take cewa, ya isa gareta tamkar wanda aka fizgo daga kujerar da yake zaune, ya figi hannayenta duka biyu ya mikar da ita daga durkuson da tayi kamar na mai neman gafara sukayi facing (fuskanci) juna tamkar zakarun dake shirin dambacewa, yace cikin karyayyar murya
“Kika ce mene Intisar? Say it again!�
Ta dube shi cikin ido, babu tsoro ba fargaba balle kallon nan nata cikin kunya dake gigita shi, babu komi cikin kwayar idon dake birgeshi face kallon tsana da tsabar kiyayya tsagwaro, da karfi ta ce,
“Nace ko zan mutu ba aure, bazan aureka ba! Ka je ka tambayi mamarka ya mukai da ita? Tunda dan ta shine ‘da� to taje ta nemo masa ‘ya� ba bayi irin mu ba (slaves). Aure nace ba zanyi ba, Al’ameen ko ana dole�.?� Kamin ta kare ya falla mata kyakkyawan marin da ya gigitata, in batayi kuskure ba ta ce har ta ga wuta. Aunty Saratu ta saki Ihsan ta ce,
“Ah ah! Al’ameen, bayan lahanta mata idanun kuma again za’a kurumtata? Wallahi bazai yiwu ba. Ta ce batayi din ko tilas ne? Ga matarka nan ta dawo dakinta ita kuma a bar mana ita haka ta sarara. Wanda uwarku tayi mata bai isa ba sai ka kara mata? Al’ameen akan idona? Ke Saratu shige mu tafi� Ta juya ga Ihsan ta ce,
“Ihsan kiyi hakuri ki zauna a dakin ki, indai a kan Intisar ne kin ji tace bata yi, in ce ko shikenan?� Gaba daya suka fice.
Daddy ya ce, “Ku dai mata duk shekarun ku tumaki ne.� Dr. Argungu ya ce “Hakane, yanzu kuma da kansu zakaji sun dawo maka da maganar, kaga Ihsan don Allah. Daga cewa an fasa aure ta shige daki ko kunyar idanun mutane, koda yake duk Amerikar ce ta kwashe masu albarka� Dukkansu suka sa dariya.
Wannan ta wuce.
*****
Ihsan kwana tayi kuka Al’ameen kuma kwanan takaicin da bazai fadu ba. Kin dai san Aminun Halimar, Halimar ta ce bata auren? Ya rasa ma takamaimai takaicin me yake? Sai da yayi tsam da ransa ya fahimci takaicin abin da ya aikata ne.
Yaya za’ayi ya bugi ‘yar mutane a idon mutanen da basu da ya ita a duniya a lokacin da suke cike da doki da farin cikin ganinta suna lailayarta tamkar kwai? Kuma bayan tana da gaskiya. Abinda Hajiya tayi mata in yayi tunani kome tace dasu daidainta ne, ba kuma abinda ba zata ce dasu ba, don ma dai tana da dimbin hakuri, to amma for God’s sake su ina ruwansu kuma meye nasu a ciki? Ina laifin wani ya taba shafar wani?
Yadda suka gayawa ‘ya’yan shi cewa haihuwa tayi haka uwar su saida suka yi alkawarin cewa duk rintsi ba zata fada ba. Brigedier yai shiru na ‘yan dakikai kana ya cigaba.
“Bayan wannan ban san komai ba. Na yi zaton Saratu karama na Riyadh, ashe wai tana gidan tana aiki a sassan masu aiki. Allah ya gani ban taba sani ba har zuwa dawowar Saratu gidana, da yake mun sami sabani na lokaci mai tsawo hakannan ni ba mazauni bane kwata-kwata.
Na dawo daga tafiya muna hirar fahimtar juna da iyalina kamar yadda muka saba, a lokacin Saratu ce min tayi Intisar tazo hutu ne daga makarantar da muka kaita a can Riyadh, inda har kika ce kin ganta Haj. Hadiza. Aminu ya shigo, yadda ya nuna kwata-kwata bai taba sanin Intisar ‘yar gidan bace.
Ita ta rika fadar wasu maganganu da dukkanmu bamu gane ba amma…sai ya dubi Intisar da murmushi, ta kau da kai ta sunne fuskarta da karfi jikin Antinta. Shi ko gogan sai ya kara lumshe ido yana dubarta da dukkan so da duk wata kauna da da namiji ke iya mallakawa diya mace, ba abinda ya dameshi da iyayen su dake zazzaune, suruki zuwa matar shi ta aure.
Daddy ya cigaba da cewa “amma ke Intisar na ji kin ce ne wai ashe Al’ameen ne nawa na Miami? Amma har kuke shirin aure? Sauran duk ban ji ba don haka daina jin kunya. Kai kuma Al’ameen kace Saratu ta maka karya, daga nan kuma duk kuka susuce kuka susuta mu. To kuma bayan kun ji ana cewa duka babu alakar Jini akwai aure shine ko kunya babu kuka karkade riguna kuka taso daga gadon asibiti, wato mu zo muyi muku auren ko?
Sannan kai Aminu karyar me Saratu ta yi maka?�
Gaba daya falon aka sa dariya, Hunainah har da hawayenta jage-jage inka dauke Faisal da ‘yar Argungu. Shi kansa Dr. Argungu yayi murmushi kuma hakika labarin ya tsuma shi. Baya shakkar wadannan mutane masu cikar mutunci nada nufin cutar ko cin zarafin ‘yarshi illah al’amarin Intisar da Aminu Allah ne ya tsarashi.
Aminu ya dubi Haj. Hadiza da girmamawar da bata kwatantuwa yace
“Maman su Hidayah karyar da yarinyar nan ta shirya min har ta wuce hankali. Wai Babanta ne ya siyarwa Haj. Ita tayi mata ayyuka, nace yana ina? Wai yana fita ranar da ya kawota mota ta bigeshi ya mutu, uwar ta kuma bata san inda take ba wai dama foreigner ce, wai talauci ne ya ishesu suka sayar da ita.
A hakan kuma sai gata tana min karatun kimiyya mai inganci, tun daga nan na sinsino karya take, na dai bita ne kawai da yadda take so don a zauna lafiya.
Akwai sanda haka kawai na yi tunanin ko gudowa ta yi daga garin su akan maza? Don ko sallama nayi mata bata amsawa amma in mai aikin Hajiya ce (Dela) sai ta amsa�. Nan ma aka sake yin dariya. Ya ce
“Na taba ganin hoton Hidayah da Hunainah a hannun ta, ina gani nace wadannan kannen ta ne, domin kamar ta isa. Amma a rashin sanin dukkanmu, tace da ni makaranta kurum ta hadasu amma ko Mamar su kamar an tsaga kara suke�. A nan kuma murmushi aka yi.
Al’ameen ya yi shiru na dan lokaci cikin wani tunani, a lokacin sautin muryar shi ya karye gabadaya. Ya dubi Anti Saratu yayi murmushi ya sadda kanshi kasa cikin jin nauyi ya ce,
“Na taso da kiyayyar Intisar diyar Anti Amarya, a dalilin son da Daddy ke mata, ban ga wanda akaiwa hakan ba cikin su baki daya bayan ni, amma wannan son ya zarce nawa.
A da, Daddy na sona fiye da kowa a gidan, amma tunda aka ce an haifi Intisar a kuruciyata sai nayi tsammanin Daddy ya daina sona.
Babu wani nau’in azaba da ya zo min a rai da ban gana mata ba, amma Intisar so na take bata kuma guje ni ba, kullum sai ta yi ta leke na. Idan na juyo muka hada ido sai ta zura da gudu dakin Mamarta.
Nayi ball da ita domin ta karye, ko ta targade ta daina wannan tafiyan nata kaman ta mage tun tana mitsitsiyar ta amma ba don ta makance ba. A kuruciyata, ban taba tsanar kaina irin ranar ba. Na bar gida a dalilin bakin-cikin abinda nayiwa Intisar haka agabadayan tsayin rayuwata 15 years a Miami, Intisar nake tunawa da halin da na barta ciki.
Yana daga abinda ya dugunzumo zuciyata ga son dawowa, don kawai in ga Intisar in nemi gafarar ta. Abin haushin, Hajiyata ta boye min gaskiyar inda take, don kar inje ko don kar ince tayi ba dai-dai ba? Haka su Najib ban san dalilinsu na boye min ba, kodayake ban tambayesu ba, suma kuma basu ce min ba.
Hajiya ce tayi sanadin da naje kitchen (Madafi) kamar yadda tayi sanadin da na nakasta ta. Zuwan da yayi sanadiyyar kasancewana dumu-dumu a kaunar yarinyar da ban sani ba, kawai na sa mata suna halimah, ashe intisar ce kanwar Faisal diyar Anti Amarya, kuma ‘yar wasu? Kai abin da mamaki�. Kowa sai murmushi.
Dr. Argungu ya dan zamo daga cikin kujerarsa yayi gyaran murya duk hankali ya koma kansa aka nutsu ana sauraron sa yace.
“To a madadin kawun Al’ameen ina nemawa dana Al’ameen alfarmar auren Intisar a hannun ka Daddyn Intisar koko a hanun su Bashir Sambo ne?� Hajjo ta yi karaf tace
“Ina! A hannun Daddy Makarfi ne, har yanzu wannan sunan “Saratu Bello Makarfi� babu mai kankareshi. Mu kam Ameenu shine namu, don haka mun bayan alfarmar Dr. Argungu.�
Daddy ya sunkuyar da kai tabbas nauyin Argungu yake ji, amma a zahiri yafi kowa farin-ciki. Ya dade da wannan burin a rayuwar sa don dai ba yadda zai yi ne. Kamin ya sani abin furtawa Ihsan ta fasa kara mai firgitarwa ta soma yiwa Babanta kuka tana masifar baya kaunar ta ita dama Ann ce kadai mahaifiyarta. Kuka take wurjanjan tana neman fita daga falon amma Anti Saratu da Hajjo suka riketa tamau.
Intissar ta mike sauran kannenta suka mara mata baya kamar wasu ‘body-guards� dinta, harta kai bakin kofar fita falon ta juyo Idanunta sun kada tamkar an watsa masu dakakken barkono, wani tukuki yazo ya tokareta a kahon zuci, kallon da tabi kowa dashi tamkar ba ita ba, ba kowa take tunani ba a wannan lokacin face kuruciyarta da al’ameen dan Haj. Nafi.
How much do you like this story?
5/10/22, 21:33 - Ummi Tandama😇: ____________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book three
*@Takori*
Page6ï¸âƒ£
Ta zargi kanta ta tsani kanta duk a lokaci daya ta kuma kalubalanci zuciyarta da so da kaunar Al’ameen. Idanunta gab suke dasu tsiyayo da kwallar da ta kasa kwarara balle taji sanyi-sanyin azabtuwar da kirjinta keyi¸duk da haka tayi murmushi ta girgiza kai ta koma ta russunawa Dr. Abubakar Argungu ta ce,
“Don Allah Baban Anti Ihsan kada ka kara fadin wannan maganan. Alkawarine na riga na yi tuntuni ba abinda zai kara hadani da Jinin Haj. Nafi ko a Lahira balle aure? Da nasan ma Al’ameen dan ta ne wallahi ko gaisuwa…� sai ta rushe musu da matsanancin kuka.
Duk falon yayi tsit sai da tayi mai isarta tukunna ta nayi tana share hawaye da majina da gefen mayafinta.
Tamkar anyi masa allurar karfi, Al’ameen wanda ke sauraronta cikin rashin fahimtar me take cewa, ya isa gareta tamkar wanda aka fizgo daga kujerar da yake zaune, ya figi hannayenta duka biyu ya mikar da ita daga durkuson da tayi kamar na mai neman gafara sukayi facing (fuskanci) juna tamkar zakarun dake shirin dambacewa, yace cikin karyayyar murya
“Kika ce mene Intisar? Say it again!�
Ta dube shi cikin ido, babu tsoro ba fargaba balle kallon nan nata cikin kunya dake gigita shi, babu komi cikin kwayar idon dake birgeshi face kallon tsana da tsabar kiyayya tsagwaro, da karfi ta ce,
“Nace ko zan mutu ba aure, bazan aureka ba! Ka je ka tambayi mamarka ya mukai da ita? Tunda dan ta shine ‘da� to taje ta nemo masa ‘ya� ba bayi irin mu ba (slaves). Aure nace ba zanyi ba, Al’ameen ko ana dole�.?� Kamin ta kare ya falla mata kyakkyawan marin da ya gigitata, in batayi kuskure ba ta ce har ta ga wuta. Aunty Saratu ta saki Ihsan ta ce,
“Ah ah! Al’ameen, bayan lahanta mata idanun kuma again za’a kurumtata? Wallahi bazai yiwu ba. Ta ce batayi din ko tilas ne? Ga matarka nan ta dawo dakinta ita kuma a bar mana ita haka ta sarara. Wanda uwarku tayi mata bai isa ba sai ka kara mata? Al’ameen akan idona? Ke Saratu shige mu tafi� Ta juya ga Ihsan ta ce,
“Ihsan kiyi hakuri ki zauna a dakin ki, indai a kan Intisar ne kin ji tace bata yi, in ce ko shikenan?� Gaba daya suka fice.
Daddy ya ce, “Ku dai mata duk shekarun ku tumaki ne.� Dr. Argungu ya ce “Hakane, yanzu kuma da kansu zakaji sun dawo maka da maganar, kaga Ihsan don Allah. Daga cewa an fasa aure ta shige daki ko kunyar idanun mutane, koda yake duk Amerikar ce ta kwashe masu albarka� Dukkansu suka sa dariya.
Wannan ta wuce.
*****
Ihsan kwana tayi kuka Al’ameen kuma kwanan takaicin da bazai fadu ba. Kin dai san Aminun Halimar, Halimar ta ce bata auren? Ya rasa ma takamaimai takaicin me yake? Sai da yayi tsam da ransa ya fahimci takaicin abin da ya aikata ne.
Yaya za’ayi ya bugi ‘yar mutane a idon mutanen da basu da ya ita a duniya a lokacin da suke cike da doki da farin cikin ganinta suna lailayarta tamkar kwai? Kuma bayan tana da gaskiya. Abinda Hajiya tayi mata in yayi tunani kome tace dasu daidainta ne, ba kuma abinda ba zata ce dasu ba, don ma dai tana da dimbin hakuri, to amma for God’s sake su ina ruwansu kuma meye nasu a ciki? Ina laifin wani ya taba shafar wani?