Sashe 59
Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Karya ne ko fatar bakinta ta fada, to bacin rai ne. Shi kadai take so har cikin tsokar zuciyarta, har gangar jiki zuwa kwakwalwarta babu inda baya girgiza da kaunar Al’ameen da sha’awar komi nashi, ita kadai ta san me take ji da yakin da take yi da zuciyarvta a duk lokacin da yai kuskuren kai hannunshi gareta koda yatsar hannunta ne kuwa amma ta rantse, ta kuma ta rantse ko son sa zai kasheta, ko duk duniya zata taru a kanta, bazata aure shi ba!
A ganinta ta hakanne kadai zata rama abinda sukai mata shi da mahaifiyarsa wanda har abada bazata manta ba, ba zata yafe mata ba kuma ba zata daina tunawa ba.
Bata san wannan hukuncin da ta yanke yai tsauri ba, domin son da Al’ameen ke mata Allah kadai ya san iyakarsa; ba na wasa bane, ya wuce ayi ramuwar gayya akansa yayi masa tsauri bazai iya dauka ba. Da kyar in bata yi kuskure ba, da kyar in hukuncinta ba zai zamo nadama mara amfani a gareta ba.
Ya cira hannunta ya aza bisa kirjinshi, tana iya jin nannauyan bugun da zuciyarsa ke yi akai-akai, jikinta ya soma sanyi, ya ce,
“Ki ji Intisar, kiji irin bugun da zuciyar nan ke yi a domin ki, saboda ke ne take ciwon da har abada bazata daina ba, ba kya tausayi na Intisar ba kya sona yanzun? Allah na rantse, in muka cigaba da tafiya a haka wata rana�. Wata rana bugawa zatayi gabadaya ta fashe kowa ya huta, ki taimake ni ki agaje ni, ki daina la’akari da laifin da ba nawa ba kina hukunta ni dashi don Allah?�
Ita dai ta zamo ‘pale� ko motsi ta kasa balle tayi kokarin yin wani abu, ta rasa abinda ke mata dadi shi kuma bakinshi bai yi shiru ba da gaya mata irin halin da zai shiga in ya rasata. Har ya kai ga kwantar da kansa bisa kafadunta.
Cikin wannan halin Faisal ya turo kofar falon ya shigo, fes idon shi a kan su, ya juya da sauri yana cewa, “Excuse me plz. Ya Aminu ban sani ba!�.
Ta mike a gigice ta banka dakin Anti, ta kifa kai bisa gado ta soma rera kuka sabo fil. Ina rowan mai neman kuka an jefeshi da dunkulen kashi.
Gabadaya suka zubo mata ido Anti da Ihsan suka yo kanta Anti ta ce,
“To kin gani Ihsan mijinki kullum sai yasa min ‘ya kuka, don haka ki je ki ja kayan ki ku tafi.� Ta sake kuluwa ta shaka ance Al’amin mijin Ihsan, ta sake tsugewa da kuka.
Ihsan ta matsa jikin gadon ta dago kanta ta aza bisa cinyarta tana murmushi tace “Haba little sister na, kin hana mun miji sakat ko tausayinshi ba kya ji, jiya saura kadan ya sakeni, don Allah kiyi hakuri ki bamu hadin kai ko na samu kan Al’ameen nima…�
Ta soma fidda kwalla itama, wani tukuki na cinta a rai, wai yau itace da kanta ke rokon wata ‘yar ficikar yarinya ta so mijin ta, Aminunta data gama shan bakar wahala a kansa, ta sadaukar da komi nata dominsa, take son sa tamkar ta fidda zuciyarta, ayya rayuwa!
Ta daure ta share wasu azababbun hawaye da suka biyo kumatun ta a guje ta ce, “Intisar, Al’ameen ya gaya mun bazamu taba samun kwanciyar hankali ba in har baki yarda da maganar auren ku ba. Don Allah Intisar ki taimake ni.�
Aunty ta juya ta fita, bata iya jure ganin wannan abin tausayi. Ita Ihsan din ce ta ke bata tausayi, ta tabbata ba karamin so takewa mijinta ba, abinda tayi mata da yawa baza su iya ba, dazu akan idonta Aminu ya turo kofa ya rufesu har da mukulli amma sai cewa tayi.
“Allah dai yasa ya shawo kanta. Don na lura Intissar akwai zucciya.�
Intisar ta dago don babatun Ihsan ya isheta, fuskar nan jike sharab da hawaye ta dubeta sosai ta ce,
“Ina ganin mutuncin ki, don haka don Allah don Annabi Anti Ihsan ba ruwan ki, ki rabu da Al’ameen kawai, shi bai ji tausayi na ba sadda yake kwallo dani har na zamo nakasashshiya? Hajiyarsa bata ji tausayi na ba a sadda Daddy ke kwallo da ni ba a gabanta, da sadda take fyaula mun kebur? Take sa min shocking? Ke har da kan ki kike son in auri mijin ki ashe karya kike ba son shi kike ba.
Baki sani ba, ni fa tunda fari ba son mijinki nake ba, kaddarar Allah ta hada mu a kichin kuma kaddarar ta raba, don haka ki tafi don Allah ina bukatar hutu, ina maku addu’a Allah ya baku kwanciyar hankalin ba sai tare da ni ba, ke ni ba wani aure da zan yi, da din ma dana amsa masa rashin galihu ne da rashin abin yi, yanzu kuwa ina da abinyi ina da galihu, ba wanda ya isa yayi kwallo da ni ban yi karar sa an fitar mun hakki na ba, ki je ki lallashi abinki ke daya ko ke ba mace bace baki ishe shi ba?�
Ta fiddo mata ido cikin barazana kamar gaske, bayan a zahiri ji take kamar ta makureta ta huce.
Ihsan tayi murmushi ta mike, a ranta ko cewa take lallai wannan yarinyace, danya (fresh), kalaminta kadai zaka ji ka tabbatar kurucci dangin hauka na dawainiya da ita, har akwai wata ‘ya mace mai cikakken hankali ta kuma san abinda takeyi da zata budi baki tace wai bata son Al’ameen Bello?
Ta mike ta na rataya jakarta ta nufi kofa ta ce,
“Ki dai kara baiwa zuciyar ki shawara Intisar, Al’ameen mai matukar son ki ne tsakani da Allah. Ba fata nake miki ba, amma ba zaki samu miji da ke son ki tamkar yadda ya ke son ki ba.�
Intisar ta bita da hararar haushi, kar ta samu din, wannan dan iskan mijin nata? Yau kam kunya da tozarci tagama jin shi a rayuwar ta. Da wane ido zata dubi Faisal?
Wane kalami gareta na wanke kanta daga sunan mayaudariya, maciyiya amana, butulu kuma mai manta alkhairi a idon Faisal? Sai ta kara jin tsanar Al’ameen ninkin baninkin na da, dubi yadda yake wa matarshi don wai kurum tana sonshi. Itama idan ya aureta wata rana ya sami wadda ya fiso fiye da ita ba mamaki ya turota lallasar yarinyar da yake son, tab! In ita ce ai za’a yi kata’i. Bata san wannan duk yana cikin wayewar Ihsan da duniya ne ba, ko ba komi zata sayo ma kanta daraja da soyayya a zuciyar mijinta, gaskiyar Hajjo ne Ihsan da Aminu sun fita wayo, ba kuma tsaranta bane a budewar kai da Ilmi.
How much do you like this story?
5/11/22, 08:13 - Ummi Tandama😇: ______________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
*@Takori*
Page7ï¸âƒ£
Su Inteesar bayan sun baro gidan Al’ameen da aka tashi taron har suka zo gida kuka take. Ba kukan komi ba ne face na nadama da tsanar kanta! Amma su ‘yan uwan basu san haka ba, sai tausarta suke da kalami masu dadi. Wai ashe Al’ameen din Hajiya ne take ta wannan hakilon akansa, amma Al’ameen ya yaudareta kuma har abada bazata taba yafe masa ba! In ya ce tayi masa karya itama ai yayi mata karyar.
Hajjo da ba’a rabata da abin dariya tace “kai ni Haj. Saratu Al’ameen ya burgeni. Fau, gaskiya jan kumatu yau yaga wuta. Ai ko ni ce Aminu abinda zanyi miki kenan.
Ciwon zuciya ya kamani akan ki, in samu kaina da kyar kice bazaki aureni ba kan wani shirmenki da bai shafeni ba.�
A ranta ta ce, “Allah sarki! Baki san ko wace uwar sa ba, da ba zaki ga laifi na ba! Baki san ya nake da uwar sa ba, da in banda zuciyar muslunci ba zaki ce in gaishe shi ba balle aure.�
Hajiya Hadiza ta ce, “Ai wannan ma bazata sabu ba, wannan irin butulci dame yayi kama? Anti Saratu ta juyo ta dubesu sannu a hankali kana Intissar din ta dake ta rasgar kuka. Ita kadai tasan kukan me Intisar take, halinda zuciyarta ke ciki da nadamar da ke tattare da ita. Tayi kwafa ta ce,
“Tunda dai tace batayi don Allah a bar zancen nan, wai Haj. Hadiza da me Instisar zata ji ne? Sabon sauyin zuciyarta ko maganar Aminu? Ba ciwon zuciya ba in ma ciwon mutuwa ne Aminu yasa Intisar fiye da wannan kuma sun cancanci dubun wannan daga gareta, duk da ba laifinsu bane.
Kar ki manta Aminu ne ya makantar da Intisar da hannunsa, da Allah ya tashi saka mata sai ya saka mata ta hanyar daura mai masifar sonta, don haka mu kyale Intisar taji da abinda ya dameta� Har suka kawo gida zancen kenan. Haj. Hadiza ta ce,
“Haba Mamar Intisar, maimakon ki lallasheta sai ki dada tunzurata? Ai babu ramuwar gayya tsakanin wa da kaninsa kuma abinda Allah ya kaddara to sai ya faru.
Ba Aminu ne ya jawo mata laluran ido ba illah Allah ya kaddara zata gamu da laluran ido ta dalilinsa, kuma Allah ya haramta rumuwar gayya, sannan abinda ya wuce shekara goma sha biyar ba’a tada shi ba sai yanzu don Aminu yana son ta?
Kome Babarsa tayi mata ai ba sa’ar ta bace da zata ce zata rama! Da ita mai hankali da halarci ce bazata bude baki a gaban Brigadier tace bazata auri jininsa ba, koda kuwa ace yankar naman jikinta Hajiyar Aminu ke yi a kalla yaci darajar mahaifinsa da ‘yan uwansa dake sonta.
Mutamin da ya daukota a daji bai san ko ‘yar waye ba. Ya hada da nashi ya rike bai kyamaceta ba duk da cewa bai sani bama ko shegiya ce, ya sota ya kaunaceta ya kula da dawiniyar rayuwarta shekaru goma sha takwas! Sai don wani dan gajeren sabani ya faru da bai taka kara ya karya ba tace bata son jininsa balle dansa na cikinsa, don ta tabbata shegiyar!
Ai idan ni na haifeki, na shayar dake mamana to baki da miji sai Jinin Bello Makarfi sai ko in sune sukace basa so to wannan kuwa. Ni dama ba kowa bace ke ‘yarsu ce, sai yadda suka ga dama da ke.
A ganinta ta hakanne kadai zata rama abinda sukai mata shi da mahaifiyarsa wanda har abada bazata manta ba, ba zata yafe mata ba kuma ba zata daina tunawa ba.
Bata san wannan hukuncin da ta yanke yai tsauri ba, domin son da Al’ameen ke mata Allah kadai ya san iyakarsa; ba na wasa bane, ya wuce ayi ramuwar gayya akansa yayi masa tsauri bazai iya dauka ba. Da kyar in bata yi kuskure ba, da kyar in hukuncinta ba zai zamo nadama mara amfani a gareta ba.
Ya cira hannunta ya aza bisa kirjinshi, tana iya jin nannauyan bugun da zuciyarsa ke yi akai-akai, jikinta ya soma sanyi, ya ce,
“Ki ji Intisar, kiji irin bugun da zuciyar nan ke yi a domin ki, saboda ke ne take ciwon da har abada bazata daina ba, ba kya tausayi na Intisar ba kya sona yanzun? Allah na rantse, in muka cigaba da tafiya a haka wata rana�. Wata rana bugawa zatayi gabadaya ta fashe kowa ya huta, ki taimake ni ki agaje ni, ki daina la’akari da laifin da ba nawa ba kina hukunta ni dashi don Allah?�
Ita dai ta zamo ‘pale� ko motsi ta kasa balle tayi kokarin yin wani abu, ta rasa abinda ke mata dadi shi kuma bakinshi bai yi shiru ba da gaya mata irin halin da zai shiga in ya rasata. Har ya kai ga kwantar da kansa bisa kafadunta.
Cikin wannan halin Faisal ya turo kofar falon ya shigo, fes idon shi a kan su, ya juya da sauri yana cewa, “Excuse me plz. Ya Aminu ban sani ba!�.
Ta mike a gigice ta banka dakin Anti, ta kifa kai bisa gado ta soma rera kuka sabo fil. Ina rowan mai neman kuka an jefeshi da dunkulen kashi.
Gabadaya suka zubo mata ido Anti da Ihsan suka yo kanta Anti ta ce,
“To kin gani Ihsan mijinki kullum sai yasa min ‘ya kuka, don haka ki je ki ja kayan ki ku tafi.� Ta sake kuluwa ta shaka ance Al’amin mijin Ihsan, ta sake tsugewa da kuka.
Ihsan ta matsa jikin gadon ta dago kanta ta aza bisa cinyarta tana murmushi tace “Haba little sister na, kin hana mun miji sakat ko tausayinshi ba kya ji, jiya saura kadan ya sakeni, don Allah kiyi hakuri ki bamu hadin kai ko na samu kan Al’ameen nima…�
Ta soma fidda kwalla itama, wani tukuki na cinta a rai, wai yau itace da kanta ke rokon wata ‘yar ficikar yarinya ta so mijin ta, Aminunta data gama shan bakar wahala a kansa, ta sadaukar da komi nata dominsa, take son sa tamkar ta fidda zuciyarta, ayya rayuwa!
Ta daure ta share wasu azababbun hawaye da suka biyo kumatun ta a guje ta ce, “Intisar, Al’ameen ya gaya mun bazamu taba samun kwanciyar hankali ba in har baki yarda da maganar auren ku ba. Don Allah Intisar ki taimake ni.�
Aunty ta juya ta fita, bata iya jure ganin wannan abin tausayi. Ita Ihsan din ce ta ke bata tausayi, ta tabbata ba karamin so takewa mijinta ba, abinda tayi mata da yawa baza su iya ba, dazu akan idonta Aminu ya turo kofa ya rufesu har da mukulli amma sai cewa tayi.
“Allah dai yasa ya shawo kanta. Don na lura Intissar akwai zucciya.�
Intisar ta dago don babatun Ihsan ya isheta, fuskar nan jike sharab da hawaye ta dubeta sosai ta ce,
“Ina ganin mutuncin ki, don haka don Allah don Annabi Anti Ihsan ba ruwan ki, ki rabu da Al’ameen kawai, shi bai ji tausayi na ba sadda yake kwallo dani har na zamo nakasashshiya? Hajiyarsa bata ji tausayi na ba a sadda Daddy ke kwallo da ni ba a gabanta, da sadda take fyaula mun kebur? Take sa min shocking? Ke har da kan ki kike son in auri mijin ki ashe karya kike ba son shi kike ba.
Baki sani ba, ni fa tunda fari ba son mijinki nake ba, kaddarar Allah ta hada mu a kichin kuma kaddarar ta raba, don haka ki tafi don Allah ina bukatar hutu, ina maku addu’a Allah ya baku kwanciyar hankalin ba sai tare da ni ba, ke ni ba wani aure da zan yi, da din ma dana amsa masa rashin galihu ne da rashin abin yi, yanzu kuwa ina da abinyi ina da galihu, ba wanda ya isa yayi kwallo da ni ban yi karar sa an fitar mun hakki na ba, ki je ki lallashi abinki ke daya ko ke ba mace bace baki ishe shi ba?�
Ta fiddo mata ido cikin barazana kamar gaske, bayan a zahiri ji take kamar ta makureta ta huce.
Ihsan tayi murmushi ta mike, a ranta ko cewa take lallai wannan yarinyace, danya (fresh), kalaminta kadai zaka ji ka tabbatar kurucci dangin hauka na dawainiya da ita, har akwai wata ‘ya mace mai cikakken hankali ta kuma san abinda takeyi da zata budi baki tace wai bata son Al’ameen Bello?
Ta mike ta na rataya jakarta ta nufi kofa ta ce,
“Ki dai kara baiwa zuciyar ki shawara Intisar, Al’ameen mai matukar son ki ne tsakani da Allah. Ba fata nake miki ba, amma ba zaki samu miji da ke son ki tamkar yadda ya ke son ki ba.�
Intisar ta bita da hararar haushi, kar ta samu din, wannan dan iskan mijin nata? Yau kam kunya da tozarci tagama jin shi a rayuwar ta. Da wane ido zata dubi Faisal?
Wane kalami gareta na wanke kanta daga sunan mayaudariya, maciyiya amana, butulu kuma mai manta alkhairi a idon Faisal? Sai ta kara jin tsanar Al’ameen ninkin baninkin na da, dubi yadda yake wa matarshi don wai kurum tana sonshi. Itama idan ya aureta wata rana ya sami wadda ya fiso fiye da ita ba mamaki ya turota lallasar yarinyar da yake son, tab! In ita ce ai za’a yi kata’i. Bata san wannan duk yana cikin wayewar Ihsan da duniya ne ba, ko ba komi zata sayo ma kanta daraja da soyayya a zuciyar mijinta, gaskiyar Hajjo ne Ihsan da Aminu sun fita wayo, ba kuma tsaranta bane a budewar kai da Ilmi.
How much do you like this story?
5/11/22, 08:13 - Ummi Tandama😇: ______________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
*@Takori*
Page7ï¸âƒ£
Su Inteesar bayan sun baro gidan Al’ameen da aka tashi taron har suka zo gida kuka take. Ba kukan komi ba ne face na nadama da tsanar kanta! Amma su ‘yan uwan basu san haka ba, sai tausarta suke da kalami masu dadi. Wai ashe Al’ameen din Hajiya ne take ta wannan hakilon akansa, amma Al’ameen ya yaudareta kuma har abada bazata taba yafe masa ba! In ya ce tayi masa karya itama ai yayi mata karyar.
Hajjo da ba’a rabata da abin dariya tace “kai ni Haj. Saratu Al’ameen ya burgeni. Fau, gaskiya jan kumatu yau yaga wuta. Ai ko ni ce Aminu abinda zanyi miki kenan.
Ciwon zuciya ya kamani akan ki, in samu kaina da kyar kice bazaki aureni ba kan wani shirmenki da bai shafeni ba.�
A ranta ta ce, “Allah sarki! Baki san ko wace uwar sa ba, da ba zaki ga laifi na ba! Baki san ya nake da uwar sa ba, da in banda zuciyar muslunci ba zaki ce in gaishe shi ba balle aure.�
Hajiya Hadiza ta ce, “Ai wannan ma bazata sabu ba, wannan irin butulci dame yayi kama? Anti Saratu ta juyo ta dubesu sannu a hankali kana Intissar din ta dake ta rasgar kuka. Ita kadai tasan kukan me Intisar take, halinda zuciyarta ke ciki da nadamar da ke tattare da ita. Tayi kwafa ta ce,
“Tunda dai tace batayi don Allah a bar zancen nan, wai Haj. Hadiza da me Instisar zata ji ne? Sabon sauyin zuciyarta ko maganar Aminu? Ba ciwon zuciya ba in ma ciwon mutuwa ne Aminu yasa Intisar fiye da wannan kuma sun cancanci dubun wannan daga gareta, duk da ba laifinsu bane.
Kar ki manta Aminu ne ya makantar da Intisar da hannunsa, da Allah ya tashi saka mata sai ya saka mata ta hanyar daura mai masifar sonta, don haka mu kyale Intisar taji da abinda ya dameta� Har suka kawo gida zancen kenan. Haj. Hadiza ta ce,
“Haba Mamar Intisar, maimakon ki lallasheta sai ki dada tunzurata? Ai babu ramuwar gayya tsakanin wa da kaninsa kuma abinda Allah ya kaddara to sai ya faru.
Ba Aminu ne ya jawo mata laluran ido ba illah Allah ya kaddara zata gamu da laluran ido ta dalilinsa, kuma Allah ya haramta rumuwar gayya, sannan abinda ya wuce shekara goma sha biyar ba’a tada shi ba sai yanzu don Aminu yana son ta?
Kome Babarsa tayi mata ai ba sa’ar ta bace da zata ce zata rama! Da ita mai hankali da halarci ce bazata bude baki a gaban Brigadier tace bazata auri jininsa ba, koda kuwa ace yankar naman jikinta Hajiyar Aminu ke yi a kalla yaci darajar mahaifinsa da ‘yan uwansa dake sonta.
Mutamin da ya daukota a daji bai san ko ‘yar waye ba. Ya hada da nashi ya rike bai kyamaceta ba duk da cewa bai sani bama ko shegiya ce, ya sota ya kaunaceta ya kula da dawiniyar rayuwarta shekaru goma sha takwas! Sai don wani dan gajeren sabani ya faru da bai taka kara ya karya ba tace bata son jininsa balle dansa na cikinsa, don ta tabbata shegiyar!
Ai idan ni na haifeki, na shayar dake mamana to baki da miji sai Jinin Bello Makarfi sai ko in sune sukace basa so to wannan kuwa. Ni dama ba kowa bace ke ‘yarsu ce, sai yadda suka ga dama da ke.