Sashe 57
Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duk wata dibara da yake jin zai iya, a matsayin shi na likita yayi domin isa ga dakin barcin su inda ya aje magungunan cikin lokas, hannunsa na dama dafe da kirjinshi hakannan bugun zuciyar na kara karuwa fiye da farkon farawarshi, yana bin bango sannu a hankali da taimakon Allah ya isa ga lokar, yayi amfani da hannun hagunshi wurin fiddo magungunan.
Ihsan ta shigo, ganin halin da yake ciki bata san sanda ta saki flask din shayin da ke hannunta ba da tray din gaba daya, ta karasa da gudu ta tallabeshi, ta ce,
“Aminu, wayyo! Kirjin ne? Ka ga tun jiya baka sha magani ba, ka manta me Alfered ya ce, wayyo ni Ihsan na banu.�
Ya yi mata alamar ta kawo mai ruwa, ta jinginar dashi jikin gadon ta tusa mai filo a baya ya jingina sosai, da gudu ta sake yin kichin ta fiddo ruwa mai sanyi da tambulan ta dawo ta mika mai kana ta cicciri magungunan ilahirin jikinta babu inda baya rawa, tasa mai abaki tasa mai kofin ya kora magungunan da ruwa, daga shi har ita sunyi wujiga-wujiga idanuwansu sunyi jazur. Ta ce,
“I’m Sorry� ya dubeta da jan idon yayi murmushi itama tayi karfin hali ta kakaro iya fatar kyakkyawan bakinta tace “You’ve to rest, pls Aminu, I don’t want to lose u, ka dinga kula, don Allah?�
Wasu hawayen suka silmiyo ta gefen idonta. Ya kallet cikin jimami bai san me zai ce mata ba. To ba zai iya fadar mai dadi ba, da yace da ita yadda bata son ta rasashi haka shima baya son rasa Intisar.
Tausayinta ba inda bai bi tsoka mai gudanar da jinni a jikin sa ba, to amma ya zaiyi? Kamin ta ankara barci mai nauyi yayi awon gaba dashi, ta sauka gefen gadon ta zuba mishi ido kuri, tana mai kara kaunar kowacce halitta a jikinsa.
Haka kawai taji gabanta na faduwa lokaci-lokaci a duk sanda ta dubi Al’ameen, ta kai hannu ta share mai gumin da keta yankowa daga goshinsa, da taga wannan bazai mata ba, sai ta mike ta dauro alwalla da ada bata damu da ita ba, ta bude Al’kur’anin shi dake aje bisa durowa ta soma karanto mai ayoyin neman sauki data koya daga gareshi.
Karfe hudu na yamma ya mike tangarau cike da kuzari tamkar wanda bai da wata lalura, cikin hamzari ya fada toilet yayi (freshen-up) ya dauro alwalla kamin ya fito Ihsan ta shigo rike da kofin tangaran cikke da danyar madarar shanu mai sanyi wadda shanta ya zame wa Aminu lazim a duk yammci, ta aza bisa ‘centre table� ta koma ta shiryo reduced fat and salt meal bisa dan madaidaicin tray wato abincin masu cardiac/hypertension problem.
Ta zauna gefen gadon tana kallonshi yana sallah, zuciyarta cike da jin dadin ganin samun saukinsa, ya shafa Addu’an ya juyo ya sakar mata lallausar murmushi ba tayi nawa ba wajen mayar masa, yaja yatsar kafarta dake kusa dashi ya daga gira cikin tsokana yace
“Kai Ihsan, irin wannan tagumi haka, ranar da na mutu ashe ke sai asibiti…� ta yi sulu ta rufe mai baki da tausasan yatsunta, kamin ya ankara sai hawaye sharr! Wani na korar wani.
Ya janyo matarshi tsantsan yana dariya ya ce,
“I’m Sorry, haba Ihsan kamar ba likita matar likita ba. Ni na isa in mutu, ban aje masu yi min Addu’a ba? So take care of urself b’cos I care!�
Ta dago ta dubeshi cikin rauni da karaya.
“Ka manta ne mahaifan ta lalace already? Are u dreaming? (kana mafarki ne) Ban ki ba dai daga Little Sister Intisar zamu samu masu yi mana Addu’a a gidan nan.� Ya girgiza kai cikin rashin kulawa da maganarta, ya ce,
“Ai ni yau Baban Babe ne, to Maman ga bakina a bamu abinci…� ya bude baki har ya bata dariya, ta dauko kofin madararshi sai ya girgiza kai ya maida hannunta inda ta dauko kofin yana cewa
“I need only you (ke kadai kawai nake so).�
Tai kasa da murya, sai in har ka kasa kunne ne zaka ji cewa da tayi
“U are always welcome!�
Ita dai al’amuran Al’ameen Bello, daga jiya zuwa yau na bata mamaki. Haka kawai ta ji jikinta yayi sanyi, kuma so da tausayin Al’ameen na kara dawainiya da ita, second bayan second, minti bayan minti, awa bayan awa da bazata ce so da tausayin Al’ameen ne ba.
How much do you like this story?
5/11/22, 08:13 - Ummi Tandama😇: ____________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book three
*@Takori*
Page8ï¸âƒ£
A kalaminshi na karshe, wadanda kuma suke kalmomi na karshe a littafin da alama ma yanzun ya rubuta;
‘To in haka ne shi meye ribar sa a rayuwa? Da me ya yi riba da me ya tsira? Bai gani ba! Bai ci riba da son Intisar ba, bai ga amfanin ilmin daya nema don ta huta da shi ba, tunda Al’ameen billonnaire ne, baya bukatar a agaza masa, bai ga ranar da son da ya shekara yi mata yai masa ba. He is but a real loser! To amma tunda don ita ya nema, shi mai mallaka mata duk abinda ya mallaka a duniya ne koda kuwa ta auri Aminu ne ko waninsa, tunda dama tunda fari ya alkawartawa ransa hakan.� Ragowar bata iya ta karasa ba, saboda kwakwalwar ba zata iya ganewa ba…�.balle ta fassarawa zuciyar ta!
Inteesar ta daga ido sama tamkar mai kididdiga adadin juyawar fanka, wasu irin hawaye ne marasa dandano bare launi ke tsere ‘one after the other� (bi-da-bi) kan kyakkyawar farar fuskar ta. Abubuwa da dama ta tuna a wannan lokacin, wato kuruciyarsu da Faisal can baya.
Ashe dama abinda take ji game da shi a lokacin itama ‘son� ne? Gaba daya jikinta ba inda bai diba ba cikin kaduwa, dimuwa da razana, a take zazzabi mai zafi ya soma kokarin rufeta, saboda karkarwa da ilahirin jikin ta ke yi littafin ya zame ya fadi kan kafarta, dai-dai lokacin da Faisal ya murda kofar bandakin ya fito gabadayan sa.
Daure da towel faffada iya kungushi yana ‘combing� sumar kanshi sai ya daskare cikin matsanancin mamaki, suka dubi juna a gaggauce idanunta face-face da hawaye, tayi saurin juya mai baya, kana ta doshi kofa tana cewa.
“Dama Daddy ne yace in kirawo ka, kada a kara zama cin abinci kana gida baka zo ba� ta sheka da gudu zata bar dakin abin tsautsayi, sai gilashin ya fado ta kuma taka shi da kafarta hannun ya lankwashe amma saboda quality (karkon) gilashin bai fashe ba, kamin ta russuna ya isa gareshi sai suka russuna a tare, hannunshi ya riga isa bisa gilashin don haka natan sai ya sauka akan nashin, shi yai nasarar daukowa, yasa karfi wajen gyara lankwashewar da yayi, a yayin da ta jingina da bango idanunta a runtse, hakannan hawayen basu fasa kwarara ba kamar an sunce fanfo.
Ba komi take tunawa ba a lokacin face ranar da ya cire mata gilashi ta baya, lokacin ana shirye-shiryen tafiyarsu Riyadh ita da Khaleel, ta dinga bin inuwarsa a hasale tana “bani gilas dina Ya Faisal, kaga bana so� haka dukan da ya sha da filo da wakokin da ya kanyi mata na “come on beautiful Babe, Maman?�
Cikin nutsuwa ya maida mata gilashinta, suka sake dubar juna a susuce sai ta kara da gudu.
Ya dade anan tsaye yana tunanin me ta gani ya sata kuka? Me ta gani ya gigita ta haka? Bai yi tsammanin zata sake kulawa da al’amarinsa ba a yanzun dai da ta ke cikin son Yayan shi Ameenu?
Intisar dakinta ta nufa agigicenta ta maida kofar ta rufe ta murza key. Ta jigina da kofar ta sake runtse idonta da karfi, tamkar mai son farkawa daga mafarki. Abubuwanne ke tariyo mata can baya tamkar a majigi. Ta tabbatar Faisal shine mutumin da ta fara so a rayuwarta kuma mutumin da bazata taba samun mai kaunarta a duniya tamkar shi ba. Tausayinshi, yagama narkar da duk wani tunani da ta mallaka. Ta zargi kanta da cin amana ta kuma kirayi kanta da ‘butulu� dan adam mai manta alkhairi.
To amma wani bangare na zuciyarta ya kalubalanci hakan da hujjar cewa, a lokacinta da Faisal tsammani suke su ‘yan uwan junane sabanin haduwarta da Al’ameen. Hakannan Al’ameen shi ya koyar dai ta son shi, shi ya kimsa mata son shi karfi da yaji, bata san so na soyayya ba sai akan shi, don haka bata jin Allah zai kamata da wannan hakkin na Faisal sai dai kaso mafi rinjaye na zuciyarta na karfafata da cewa, yanzu ne ya dace tayi wani abu, yanzu ne ya dace ta sadaukar da kanta da soyayyarta (son da takewa Al’ameen) don nunawa Faisal wannan kaunar da ya wanzar da rayuwarshi nuna mata, tun tana a tsumman goyo. To wai ma ya akai ta so Al’ameen? Bata sani ba, illa may be because he is unikue (watakila don shi din na daban ne).
Ta yaya? Ta yaya zata nunawa Faisal din kauna bayan a yanzun ya nuna baya da lokacinta ma? Ta tambayi kanta, lokaci guda ta bawa kanta amsa da cewa ta hanyar auren shi mana Intisar? Amsar tayi mata nauyi a baka da zuci, wai Intisar matar Faisal in banda Allah mai juya al’amura ina wannan abu zai taba zuwa masu a rai?
A lokacin ne kuma ta tuna shima fa Faisal dan Hajiya ne! Wannan zuri’ar da tayi alkawarin ba zata sake kulawa ba! Wannan zuri’ar data nuna mata kiyayyar da ba wani mahaluki a doron kasa da ya taba nuna mata! Wannan zuri’ar da idan ta aura, ta sake jefa kanta cikin bala’I da masifa ne watakila ma fiye da na baya. Bayan yanzun da cikakken gatanta, ga Aunty, Daddy, uwa-uba dangi da uwa mahaifiya masu so da kaunarta. Zuri’ar Haj. Nafi? Ta girgiza kai da karfi, ire-iren maganganun Haj. kadai ke dawo mata wasu na bin wasu.
“Wai me yasa kike son ‘ya’yana ne, bayan ni na tsaneki? Har kullum mutum kanyi nisa ne da jinin makiyin shi, Saratu banda ke! Don naji ance komi Faisal kike ambato, har kuka kika yi da ya bar kasar, yayi maki kama da ‘ya’yan mutsiyatan kauye ne?
Ihsan ta shigo, ganin halin da yake ciki bata san sanda ta saki flask din shayin da ke hannunta ba da tray din gaba daya, ta karasa da gudu ta tallabeshi, ta ce,
“Aminu, wayyo! Kirjin ne? Ka ga tun jiya baka sha magani ba, ka manta me Alfered ya ce, wayyo ni Ihsan na banu.�
Ya yi mata alamar ta kawo mai ruwa, ta jinginar dashi jikin gadon ta tusa mai filo a baya ya jingina sosai, da gudu ta sake yin kichin ta fiddo ruwa mai sanyi da tambulan ta dawo ta mika mai kana ta cicciri magungunan ilahirin jikinta babu inda baya rawa, tasa mai abaki tasa mai kofin ya kora magungunan da ruwa, daga shi har ita sunyi wujiga-wujiga idanuwansu sunyi jazur. Ta ce,
“I’m Sorry� ya dubeta da jan idon yayi murmushi itama tayi karfin hali ta kakaro iya fatar kyakkyawan bakinta tace “You’ve to rest, pls Aminu, I don’t want to lose u, ka dinga kula, don Allah?�
Wasu hawayen suka silmiyo ta gefen idonta. Ya kallet cikin jimami bai san me zai ce mata ba. To ba zai iya fadar mai dadi ba, da yace da ita yadda bata son ta rasashi haka shima baya son rasa Intisar.
Tausayinta ba inda bai bi tsoka mai gudanar da jinni a jikin sa ba, to amma ya zaiyi? Kamin ta ankara barci mai nauyi yayi awon gaba dashi, ta sauka gefen gadon ta zuba mishi ido kuri, tana mai kara kaunar kowacce halitta a jikinsa.
Haka kawai taji gabanta na faduwa lokaci-lokaci a duk sanda ta dubi Al’ameen, ta kai hannu ta share mai gumin da keta yankowa daga goshinsa, da taga wannan bazai mata ba, sai ta mike ta dauro alwalla da ada bata damu da ita ba, ta bude Al’kur’anin shi dake aje bisa durowa ta soma karanto mai ayoyin neman sauki data koya daga gareshi.
Karfe hudu na yamma ya mike tangarau cike da kuzari tamkar wanda bai da wata lalura, cikin hamzari ya fada toilet yayi (freshen-up) ya dauro alwalla kamin ya fito Ihsan ta shigo rike da kofin tangaran cikke da danyar madarar shanu mai sanyi wadda shanta ya zame wa Aminu lazim a duk yammci, ta aza bisa ‘centre table� ta koma ta shiryo reduced fat and salt meal bisa dan madaidaicin tray wato abincin masu cardiac/hypertension problem.
Ta zauna gefen gadon tana kallonshi yana sallah, zuciyarta cike da jin dadin ganin samun saukinsa, ya shafa Addu’an ya juyo ya sakar mata lallausar murmushi ba tayi nawa ba wajen mayar masa, yaja yatsar kafarta dake kusa dashi ya daga gira cikin tsokana yace
“Kai Ihsan, irin wannan tagumi haka, ranar da na mutu ashe ke sai asibiti…� ta yi sulu ta rufe mai baki da tausasan yatsunta, kamin ya ankara sai hawaye sharr! Wani na korar wani.
Ya janyo matarshi tsantsan yana dariya ya ce,
“I’m Sorry, haba Ihsan kamar ba likita matar likita ba. Ni na isa in mutu, ban aje masu yi min Addu’a ba? So take care of urself b’cos I care!�
Ta dago ta dubeshi cikin rauni da karaya.
“Ka manta ne mahaifan ta lalace already? Are u dreaming? (kana mafarki ne) Ban ki ba dai daga Little Sister Intisar zamu samu masu yi mana Addu’a a gidan nan.� Ya girgiza kai cikin rashin kulawa da maganarta, ya ce,
“Ai ni yau Baban Babe ne, to Maman ga bakina a bamu abinci…� ya bude baki har ya bata dariya, ta dauko kofin madararshi sai ya girgiza kai ya maida hannunta inda ta dauko kofin yana cewa
“I need only you (ke kadai kawai nake so).�
Tai kasa da murya, sai in har ka kasa kunne ne zaka ji cewa da tayi
“U are always welcome!�
Ita dai al’amuran Al’ameen Bello, daga jiya zuwa yau na bata mamaki. Haka kawai ta ji jikinta yayi sanyi, kuma so da tausayin Al’ameen na kara dawainiya da ita, second bayan second, minti bayan minti, awa bayan awa da bazata ce so da tausayin Al’ameen ne ba.
How much do you like this story?
5/11/22, 08:13 - Ummi Tandama😇: ____________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book three
*@Takori*
Page8ï¸âƒ£
A kalaminshi na karshe, wadanda kuma suke kalmomi na karshe a littafin da alama ma yanzun ya rubuta;
‘To in haka ne shi meye ribar sa a rayuwa? Da me ya yi riba da me ya tsira? Bai gani ba! Bai ci riba da son Intisar ba, bai ga amfanin ilmin daya nema don ta huta da shi ba, tunda Al’ameen billonnaire ne, baya bukatar a agaza masa, bai ga ranar da son da ya shekara yi mata yai masa ba. He is but a real loser! To amma tunda don ita ya nema, shi mai mallaka mata duk abinda ya mallaka a duniya ne koda kuwa ta auri Aminu ne ko waninsa, tunda dama tunda fari ya alkawartawa ransa hakan.� Ragowar bata iya ta karasa ba, saboda kwakwalwar ba zata iya ganewa ba…�.balle ta fassarawa zuciyar ta!
Inteesar ta daga ido sama tamkar mai kididdiga adadin juyawar fanka, wasu irin hawaye ne marasa dandano bare launi ke tsere ‘one after the other� (bi-da-bi) kan kyakkyawar farar fuskar ta. Abubuwa da dama ta tuna a wannan lokacin, wato kuruciyarsu da Faisal can baya.
Ashe dama abinda take ji game da shi a lokacin itama ‘son� ne? Gaba daya jikinta ba inda bai diba ba cikin kaduwa, dimuwa da razana, a take zazzabi mai zafi ya soma kokarin rufeta, saboda karkarwa da ilahirin jikin ta ke yi littafin ya zame ya fadi kan kafarta, dai-dai lokacin da Faisal ya murda kofar bandakin ya fito gabadayan sa.
Daure da towel faffada iya kungushi yana ‘combing� sumar kanshi sai ya daskare cikin matsanancin mamaki, suka dubi juna a gaggauce idanunta face-face da hawaye, tayi saurin juya mai baya, kana ta doshi kofa tana cewa.
“Dama Daddy ne yace in kirawo ka, kada a kara zama cin abinci kana gida baka zo ba� ta sheka da gudu zata bar dakin abin tsautsayi, sai gilashin ya fado ta kuma taka shi da kafarta hannun ya lankwashe amma saboda quality (karkon) gilashin bai fashe ba, kamin ta russuna ya isa gareshi sai suka russuna a tare, hannunshi ya riga isa bisa gilashin don haka natan sai ya sauka akan nashin, shi yai nasarar daukowa, yasa karfi wajen gyara lankwashewar da yayi, a yayin da ta jingina da bango idanunta a runtse, hakannan hawayen basu fasa kwarara ba kamar an sunce fanfo.
Ba komi take tunawa ba a lokacin face ranar da ya cire mata gilashi ta baya, lokacin ana shirye-shiryen tafiyarsu Riyadh ita da Khaleel, ta dinga bin inuwarsa a hasale tana “bani gilas dina Ya Faisal, kaga bana so� haka dukan da ya sha da filo da wakokin da ya kanyi mata na “come on beautiful Babe, Maman?�
Cikin nutsuwa ya maida mata gilashinta, suka sake dubar juna a susuce sai ta kara da gudu.
Ya dade anan tsaye yana tunanin me ta gani ya sata kuka? Me ta gani ya gigita ta haka? Bai yi tsammanin zata sake kulawa da al’amarinsa ba a yanzun dai da ta ke cikin son Yayan shi Ameenu?
Intisar dakinta ta nufa agigicenta ta maida kofar ta rufe ta murza key. Ta jigina da kofar ta sake runtse idonta da karfi, tamkar mai son farkawa daga mafarki. Abubuwanne ke tariyo mata can baya tamkar a majigi. Ta tabbatar Faisal shine mutumin da ta fara so a rayuwarta kuma mutumin da bazata taba samun mai kaunarta a duniya tamkar shi ba. Tausayinshi, yagama narkar da duk wani tunani da ta mallaka. Ta zargi kanta da cin amana ta kuma kirayi kanta da ‘butulu� dan adam mai manta alkhairi.
To amma wani bangare na zuciyarta ya kalubalanci hakan da hujjar cewa, a lokacinta da Faisal tsammani suke su ‘yan uwan junane sabanin haduwarta da Al’ameen. Hakannan Al’ameen shi ya koyar dai ta son shi, shi ya kimsa mata son shi karfi da yaji, bata san so na soyayya ba sai akan shi, don haka bata jin Allah zai kamata da wannan hakkin na Faisal sai dai kaso mafi rinjaye na zuciyarta na karfafata da cewa, yanzu ne ya dace tayi wani abu, yanzu ne ya dace ta sadaukar da kanta da soyayyarta (son da takewa Al’ameen) don nunawa Faisal wannan kaunar da ya wanzar da rayuwarshi nuna mata, tun tana a tsumman goyo. To wai ma ya akai ta so Al’ameen? Bata sani ba, illa may be because he is unikue (watakila don shi din na daban ne).
Ta yaya? Ta yaya zata nunawa Faisal din kauna bayan a yanzun ya nuna baya da lokacinta ma? Ta tambayi kanta, lokaci guda ta bawa kanta amsa da cewa ta hanyar auren shi mana Intisar? Amsar tayi mata nauyi a baka da zuci, wai Intisar matar Faisal in banda Allah mai juya al’amura ina wannan abu zai taba zuwa masu a rai?
A lokacin ne kuma ta tuna shima fa Faisal dan Hajiya ne! Wannan zuri’ar da tayi alkawarin ba zata sake kulawa ba! Wannan zuri’ar data nuna mata kiyayyar da ba wani mahaluki a doron kasa da ya taba nuna mata! Wannan zuri’ar da idan ta aura, ta sake jefa kanta cikin bala’I da masifa ne watakila ma fiye da na baya. Bayan yanzun da cikakken gatanta, ga Aunty, Daddy, uwa-uba dangi da uwa mahaifiya masu so da kaunarta. Zuri’ar Haj. Nafi? Ta girgiza kai da karfi, ire-iren maganganun Haj. kadai ke dawo mata wasu na bin wasu.
“Wai me yasa kike son ‘ya’yana ne, bayan ni na tsaneki? Har kullum mutum kanyi nisa ne da jinin makiyin shi, Saratu banda ke! Don naji ance komi Faisal kike ambato, har kuka kika yi da ya bar kasar, yayi maki kama da ‘ya’yan mutsiyatan kauye ne?