Sashe 36
Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shekara na zagayowa na haife ki Hidayah, asalin sunan ki Rahmah, sunan mahaifiyar Bashir ne kika ci, Hajjo ne ta sa maki Hidayah to sai muma din muka kama.
A shekarar Bashir ya halarci kwasa-kwasai da dama a kasashe daban-daban, da ta kai har a ka yi mai karin girma daga matsayin da ya ke da shi a wajen aikin su zuwa (Consultant) na kasar Nijeriya a Faransa.
Hassan bai taba furta mana son Hajjo yake ba har ta kare makaranta, kwazon ta da basirar ta yasa Bashir yayi cuku-cukun da ya nema mata aji biyu na karamar sakandire ta kuma lashe gwajin duk da suka yi mata tas. Sai da ta kai aji hudu a sakandire ne Hassan ya fito karara ya gaya mana shi fa kamun Hajjo ya ke.
Daga ni har Bashir mun yi matukar farin-ciki ko da yake dama tuni mun dago shi, bini-bini kaji shi yana “kanwata, me ya hada ki da wancan karmasashshen Bafaranshen? Ke fa yarinya ce har yanzu, baki isa yin abuta da maza ba. Babban farin-ciki na shine na kasancewar Hassan 100% ya cika kamilin mutum dan babban gida a jihar Borno, don mahaifin shi sanannen malamin Addini ne, duk da zaman shegiyar kasa irin France, ya canza wasu daga kyawawan dabi’un shi duk da hakan ni da Bashir ba mu ji ko dar na wanke Hajjo mu ba shi auren ta ba tun kamin kammala karatun ta na sakandire don mun san Hajjo na da wayo dole ta canza Hassan, barin ma yanzun da kanta ya bude da rayuwar turai.
Idan kin gan mu a lokacin zaki rantse bamu san wata aba miyar kuka da kalkashi ba don gabadaya sajewa muke da mutanen kasar, duka harshen mu ya juye da Faransanci zallah sai ma Bashir da ya ke baki shi ke tona mu, amma ko Hassan fari ne sol.
Ranar da nayi haihuwata ta uku a duniya wato ke Hunainah, ranar ne Bashir ya kammala Ph D din sa in da muka kara samun ‘promotion�. Mun dawo gida anyi gagarumin auren Hassan da Hajjo a garin Biu ta jihar Borno da Shanono ta jihar Kano, biki irin wanda ba’a taba yi a Shanono ba. Bashir Uban amarya kuma babban aminin ango an ba Naira kashi haka Hassan, sun nuna basu da abin so da kauna kamar kanwar su Hajjo.
To ni ma komawa na yi kamar sarauniya wurin matan Hakimi ko numfashi ji suke kaman su min. ‘Ya’ya na kuwa ko makota basa bari su dauke su wai kar su shafa masu datti, ni ko na balle bakin jaka na kara jike su da ‘yan yanzu, ai sai na kara zama kamar kwan da kaza ta nasa yanzu-yanzunnan, ko motsi nayi a ce “Hajiya Hadiza, me kike so?�
An sa Hajjo a lalle akayi sunan Baby, inda Bashir ya wanken dattin rai na ya mayar mun da sunan Innar mu (Hannatu), ke Hannatu Baban ki ke kiran ki Hunainah har yau din da ta bi ki. Bakar fatar Bashir da farar fata na ya mai da ku kalar coffee mai haske da har ake maku kallon ruwa-biyu, ya kuma sanya ‘nationality� din ku ‘in doubt� (cikin shakku) bayan a zahiri gaba da baya ku Fulfulde ne ziryan.
Da Hajjo ta kare sakandire suka zo Borno gaida Abban su Hassan da baya da lafiya, ai kuwa fir ya hana Hassan komawa aiki France kasancewar shi babba a gidan su kuma shi kadai ne da namiji. Duk kannin shi mata ne a gidan auren su ga tsufa mai wahala da ya kamashi.
To Hassan da Hajjo ke ma kin san takaici ba sai an fada ba wai an katse masu rayuwa. A nan Maiduguri Hassan ya sayi kankareren gida na garari suka tare, inda Hajjo aka rufe bakin mahaifa kif aka afka Unimaid inda ta ke karatun (linguistic) harshen Faransa da Barbarci ziryan. Daga baya ne aiki ya cilla su Lagos inda Hassan ke aiki da ma’aikatar ilmi ta kasa wato Federal Ministry of Education.
Shekarun ki Hidayah shidda, Hunainah biyar aka yi wa Baban ku Ambasada a kasar Russia, bamu dade ba aka canza shi zuwa Jordan inda a nan ne kuka kare firamare. Muna da shekaru uku a nan Allah ya yi wa Ambasadan kasar Nigeria a Saudiyyah rasuwa, aka sake yi mana (transfer) na wucin gadi zuwa Saudi-Arabia kafin a fidda sabon Ambassada, inda muka zauna a birnin Riyadh. Aka kai ku makarantar sakandire ta kwana.
Ba zan manta ba, ba kuma zan taba mancewa ba, a dan tsukin na yi ta mafarke-mafarken wai na ga jaririya ta da aka sace. Kuka zo hutun ku na farko a aji daya da kawar ku idan baku mantaba, yau shekaru biyar kenan da faruwar al’amarin da har yau yake damuna a rai domin na tabbata wallahi Fatimah diyata na gani�.
Hajiya Hadizah ta yi shiru hawaye na bulbular mata, jikin ta ya hau rawa. Hidayah da Hunainah, da suka yi jigum suna sauraron ta da dukkan hankalin su, suka juya suka dubi juna a gigice, cikin tsananin mamaki da ta’ajjibi mara misaltuwa suka hada baki, wanda su kan su basu san su yi ba suka ce
“Saratu Bello Makarfi???�
Dubawar nan da za su yi Mamarsu numfashi dai-dai ta ke fitar wa ba kuma ta ko iya shaida wanda ke kanta alamun hawan jinin ta ya tashi kenan. Hidayah ta fashe da kuka tace “Mamar mu don Allah kar ki mutu ki bar mu, Mamar in kin mutu ya za mu yi?�
Karamar wato Hunainah ita ta yi hankalin kiran mahaifin su, masu aikin gidan mata suka taimaka wurin sanya ta a mota aka nufi asibitin da suke zuwa da ita.
A daren nan Ambasada da yaran shi ba su rintsa ba, suka kwashe labarin data basu kaf suka gaya mishi, shi kansa ba karamin girgiza yayi ba yace idan yarinyar na makarantar ku ta Riyadh har yanzu, mai zai hana mu je mu neme ta? Idan har hakan zai dawon da farin-cikin Hadizah?
Kawanaki uku bayan nan jirgin safe ne ya sauke su a birnin Riyadh, garin da rabon su da shi shekaru biyar kenan cif. Motar musamman aka tura ma Ambasadan daga Saudi-Embassy ta kwashe su zuwa Kingston College.
Su Hidayah sun ga makarantar su ta da ta samu sauye-sauye ta fannoni da dama musamman ta fuskar cigaba, hatta ‘principal� din da suka sani a da ba ita bace yanzun an canza a an kawo wata daga Asia maimakon Ayyush Siddiky da suka sani mutuniyar Madina.
Ita bata san ma yarinyar da su ke nema ba ta dai hada su da wani tsohon malami, malamin shine Sayyid-Ridhwan mai kula da shige da ficen dalibai ya kuma dade yana aiki a nan. Ga abinda yace da su,
“ayya! Yarinya mai hazaka irin Sarah, ban san maiyasa iyayaenta suka katse mata karatu ba a shekararta ta karshe. Inda duk kuka ganta ku baiwa iyayenta shawara su maido mana ita koda basu da ko sisin kobo ne, domin Saratou ‘yar baiwa ce�.
Daga Ambasadan har ‘ya’yan shi ji suka yi kamar su daura hannu a ka su rafsa ihu, Hunainah bata san sanda hawaye ya ziraro mata ba tasa hannu ta share. Su kanyi tunanin kaunar da sukewa Saratu Bello, a sanda suke makaranta, sun dauka kauna ce kurum ta haduwar jini daga Indallahi, da kuma ‘kualities� na ita Saratun da ke sawa kowa ke sonta a (Kingston), to ashe Saratu jinin su ke gauraye dana juna shiyasa suke jinta har kasusuwa da bargon jikin su, barin yanzun kuma da suka ji wai ashe diyar Maman su ce?
Ba abinda ke damun su kamar lafiyar mahaifiyar su da ke ta walagigi, tayi-bata yi ba Allah masani. A gidan saukar bakin da aka yiwa ambasadan masauki cikin su ba wanda ya rintsa, kowanne abinda ya ke sakawa daban ne dana dan uwansa, zuciyar kowannen su cike take da alhini da taraddadi.
Hidayah dake kwance cikin kilishi tana kallon sama sai ta mike a gaggauce ta takarkare kamar gyare ta shiga jerawa ‘yar uwarta kira, duk ta rude sai rawa jikin ta yake kamar mazari.
A gigice uban da ‘yar suka sauko daga bene inda garin sauka Hunainah ta sulmiyo daga matakala ta biyar amma bata kula ba ta gyagije ta mike, don sun dauka wani mugun abu ne ya faru da ita, a tare suke tambayar ta “lafiya?� Tayi wata irin ajiyar zuciya kamar an ce ga Saratu a gaban su ta rungume ‘yar uwar ta tace “na tuna ne Daddy, Saratu ta taba gaya mana ita da iyayenta suna zaune ne a Lagos, kuma nan anguwar su Aunty Hajjo�
Hunainah ta ce, “kwarai anyi haka nima Daddy mantawa na yi.�
Ambasada Bashir sambo, bai yi barci ba a ranar sai da yayi masu ‘booking� din tikiti na jirgi mai zuwa Lagos din Nigeria a washegari. A yau kam sun samu sunyi barci cikin natsuwa har da minshari, sun tabbata wahalar da Mamar su ke ciki ta yanke daga yau tunda kuwa za su kawo mata Saratun ta har asibiti. (Anya kuwa?)
Dawowar Hajjo kenan daga Ajaokuta inda take bautar kasa, ta tadda baki ba zato ba tsammani amma ba tare da Uwar su ba. Hajjo uwar ‘ya’ya ukku biyu maza da ‘yar auta mace, tuni ta hau tsallen murna kaman yarinya karama don har girman Hajjon bata bar wautarta ta kuruciya ba. Hassan ya je Maiduguri gabatar da wani aiki a ranar take tsammanin shi. To amma me?
Daga uban har ‘ya’yan fuska babu annuri, duk ta bi ta tsargu, abinda ta kawo ma ranta kawai Yayar ta ta rasu wajen haihuwa dan tuni ta san tana da ciki, tun bata nemi bayani ba ta soma kuka tace “yanzu shikenan ni daya na rage a duniyar Kawu Bashir?�
A shekarar Bashir ya halarci kwasa-kwasai da dama a kasashe daban-daban, da ta kai har a ka yi mai karin girma daga matsayin da ya ke da shi a wajen aikin su zuwa (Consultant) na kasar Nijeriya a Faransa.
Hassan bai taba furta mana son Hajjo yake ba har ta kare makaranta, kwazon ta da basirar ta yasa Bashir yayi cuku-cukun da ya nema mata aji biyu na karamar sakandire ta kuma lashe gwajin duk da suka yi mata tas. Sai da ta kai aji hudu a sakandire ne Hassan ya fito karara ya gaya mana shi fa kamun Hajjo ya ke.
Daga ni har Bashir mun yi matukar farin-ciki ko da yake dama tuni mun dago shi, bini-bini kaji shi yana “kanwata, me ya hada ki da wancan karmasashshen Bafaranshen? Ke fa yarinya ce har yanzu, baki isa yin abuta da maza ba. Babban farin-ciki na shine na kasancewar Hassan 100% ya cika kamilin mutum dan babban gida a jihar Borno, don mahaifin shi sanannen malamin Addini ne, duk da zaman shegiyar kasa irin France, ya canza wasu daga kyawawan dabi’un shi duk da hakan ni da Bashir ba mu ji ko dar na wanke Hajjo mu ba shi auren ta ba tun kamin kammala karatun ta na sakandire don mun san Hajjo na da wayo dole ta canza Hassan, barin ma yanzun da kanta ya bude da rayuwar turai.
Idan kin gan mu a lokacin zaki rantse bamu san wata aba miyar kuka da kalkashi ba don gabadaya sajewa muke da mutanen kasar, duka harshen mu ya juye da Faransanci zallah sai ma Bashir da ya ke baki shi ke tona mu, amma ko Hassan fari ne sol.
Ranar da nayi haihuwata ta uku a duniya wato ke Hunainah, ranar ne Bashir ya kammala Ph D din sa in da muka kara samun ‘promotion�. Mun dawo gida anyi gagarumin auren Hassan da Hajjo a garin Biu ta jihar Borno da Shanono ta jihar Kano, biki irin wanda ba’a taba yi a Shanono ba. Bashir Uban amarya kuma babban aminin ango an ba Naira kashi haka Hassan, sun nuna basu da abin so da kauna kamar kanwar su Hajjo.
To ni ma komawa na yi kamar sarauniya wurin matan Hakimi ko numfashi ji suke kaman su min. ‘Ya’ya na kuwa ko makota basa bari su dauke su wai kar su shafa masu datti, ni ko na balle bakin jaka na kara jike su da ‘yan yanzu, ai sai na kara zama kamar kwan da kaza ta nasa yanzu-yanzunnan, ko motsi nayi a ce “Hajiya Hadiza, me kike so?�
An sa Hajjo a lalle akayi sunan Baby, inda Bashir ya wanken dattin rai na ya mayar mun da sunan Innar mu (Hannatu), ke Hannatu Baban ki ke kiran ki Hunainah har yau din da ta bi ki. Bakar fatar Bashir da farar fata na ya mai da ku kalar coffee mai haske da har ake maku kallon ruwa-biyu, ya kuma sanya ‘nationality� din ku ‘in doubt� (cikin shakku) bayan a zahiri gaba da baya ku Fulfulde ne ziryan.
Da Hajjo ta kare sakandire suka zo Borno gaida Abban su Hassan da baya da lafiya, ai kuwa fir ya hana Hassan komawa aiki France kasancewar shi babba a gidan su kuma shi kadai ne da namiji. Duk kannin shi mata ne a gidan auren su ga tsufa mai wahala da ya kamashi.
To Hassan da Hajjo ke ma kin san takaici ba sai an fada ba wai an katse masu rayuwa. A nan Maiduguri Hassan ya sayi kankareren gida na garari suka tare, inda Hajjo aka rufe bakin mahaifa kif aka afka Unimaid inda ta ke karatun (linguistic) harshen Faransa da Barbarci ziryan. Daga baya ne aiki ya cilla su Lagos inda Hassan ke aiki da ma’aikatar ilmi ta kasa wato Federal Ministry of Education.
Shekarun ki Hidayah shidda, Hunainah biyar aka yi wa Baban ku Ambasada a kasar Russia, bamu dade ba aka canza shi zuwa Jordan inda a nan ne kuka kare firamare. Muna da shekaru uku a nan Allah ya yi wa Ambasadan kasar Nigeria a Saudiyyah rasuwa, aka sake yi mana (transfer) na wucin gadi zuwa Saudi-Arabia kafin a fidda sabon Ambassada, inda muka zauna a birnin Riyadh. Aka kai ku makarantar sakandire ta kwana.
Ba zan manta ba, ba kuma zan taba mancewa ba, a dan tsukin na yi ta mafarke-mafarken wai na ga jaririya ta da aka sace. Kuka zo hutun ku na farko a aji daya da kawar ku idan baku mantaba, yau shekaru biyar kenan da faruwar al’amarin da har yau yake damuna a rai domin na tabbata wallahi Fatimah diyata na gani�.
Hajiya Hadizah ta yi shiru hawaye na bulbular mata, jikin ta ya hau rawa. Hidayah da Hunainah, da suka yi jigum suna sauraron ta da dukkan hankalin su, suka juya suka dubi juna a gigice, cikin tsananin mamaki da ta’ajjibi mara misaltuwa suka hada baki, wanda su kan su basu san su yi ba suka ce
“Saratu Bello Makarfi???�
Dubawar nan da za su yi Mamarsu numfashi dai-dai ta ke fitar wa ba kuma ta ko iya shaida wanda ke kanta alamun hawan jinin ta ya tashi kenan. Hidayah ta fashe da kuka tace “Mamar mu don Allah kar ki mutu ki bar mu, Mamar in kin mutu ya za mu yi?�
Karamar wato Hunainah ita ta yi hankalin kiran mahaifin su, masu aikin gidan mata suka taimaka wurin sanya ta a mota aka nufi asibitin da suke zuwa da ita.
A daren nan Ambasada da yaran shi ba su rintsa ba, suka kwashe labarin data basu kaf suka gaya mishi, shi kansa ba karamin girgiza yayi ba yace idan yarinyar na makarantar ku ta Riyadh har yanzu, mai zai hana mu je mu neme ta? Idan har hakan zai dawon da farin-cikin Hadizah?
Kawanaki uku bayan nan jirgin safe ne ya sauke su a birnin Riyadh, garin da rabon su da shi shekaru biyar kenan cif. Motar musamman aka tura ma Ambasadan daga Saudi-Embassy ta kwashe su zuwa Kingston College.
Su Hidayah sun ga makarantar su ta da ta samu sauye-sauye ta fannoni da dama musamman ta fuskar cigaba, hatta ‘principal� din da suka sani a da ba ita bace yanzun an canza a an kawo wata daga Asia maimakon Ayyush Siddiky da suka sani mutuniyar Madina.
Ita bata san ma yarinyar da su ke nema ba ta dai hada su da wani tsohon malami, malamin shine Sayyid-Ridhwan mai kula da shige da ficen dalibai ya kuma dade yana aiki a nan. Ga abinda yace da su,
“ayya! Yarinya mai hazaka irin Sarah, ban san maiyasa iyayaenta suka katse mata karatu ba a shekararta ta karshe. Inda duk kuka ganta ku baiwa iyayenta shawara su maido mana ita koda basu da ko sisin kobo ne, domin Saratou ‘yar baiwa ce�.
Daga Ambasadan har ‘ya’yan shi ji suka yi kamar su daura hannu a ka su rafsa ihu, Hunainah bata san sanda hawaye ya ziraro mata ba tasa hannu ta share. Su kanyi tunanin kaunar da sukewa Saratu Bello, a sanda suke makaranta, sun dauka kauna ce kurum ta haduwar jini daga Indallahi, da kuma ‘kualities� na ita Saratun da ke sawa kowa ke sonta a (Kingston), to ashe Saratu jinin su ke gauraye dana juna shiyasa suke jinta har kasusuwa da bargon jikin su, barin yanzun kuma da suka ji wai ashe diyar Maman su ce?
Ba abinda ke damun su kamar lafiyar mahaifiyar su da ke ta walagigi, tayi-bata yi ba Allah masani. A gidan saukar bakin da aka yiwa ambasadan masauki cikin su ba wanda ya rintsa, kowanne abinda ya ke sakawa daban ne dana dan uwansa, zuciyar kowannen su cike take da alhini da taraddadi.
Hidayah dake kwance cikin kilishi tana kallon sama sai ta mike a gaggauce ta takarkare kamar gyare ta shiga jerawa ‘yar uwarta kira, duk ta rude sai rawa jikin ta yake kamar mazari.
A gigice uban da ‘yar suka sauko daga bene inda garin sauka Hunainah ta sulmiyo daga matakala ta biyar amma bata kula ba ta gyagije ta mike, don sun dauka wani mugun abu ne ya faru da ita, a tare suke tambayar ta “lafiya?� Tayi wata irin ajiyar zuciya kamar an ce ga Saratu a gaban su ta rungume ‘yar uwar ta tace “na tuna ne Daddy, Saratu ta taba gaya mana ita da iyayenta suna zaune ne a Lagos, kuma nan anguwar su Aunty Hajjo�
Hunainah ta ce, “kwarai anyi haka nima Daddy mantawa na yi.�
Ambasada Bashir sambo, bai yi barci ba a ranar sai da yayi masu ‘booking� din tikiti na jirgi mai zuwa Lagos din Nigeria a washegari. A yau kam sun samu sunyi barci cikin natsuwa har da minshari, sun tabbata wahalar da Mamar su ke ciki ta yanke daga yau tunda kuwa za su kawo mata Saratun ta har asibiti. (Anya kuwa?)
Dawowar Hajjo kenan daga Ajaokuta inda take bautar kasa, ta tadda baki ba zato ba tsammani amma ba tare da Uwar su ba. Hajjo uwar ‘ya’ya ukku biyu maza da ‘yar auta mace, tuni ta hau tsallen murna kaman yarinya karama don har girman Hajjon bata bar wautarta ta kuruciya ba. Hassan ya je Maiduguri gabatar da wani aiki a ranar take tsammanin shi. To amma me?
Daga uban har ‘ya’yan fuska babu annuri, duk ta bi ta tsargu, abinda ta kawo ma ranta kawai Yayar ta ta rasu wajen haihuwa dan tuni ta san tana da ciki, tun bata nemi bayani ba ta soma kuka tace “yanzu shikenan ni daya na rage a duniyar Kawu Bashir?�