Sashe 77
Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Babu ko tantama wannan Alameen Bello ne yake rike da shi a sanda mahaifiyar shi ta haife shi. In kasan photocophy na Alameen to wannan jaririn ne. A take ya lankaya mai sunan shi cikin kunnuwan shi wato Alameen Alameen Bello.
Sai dare aka fito da Ihsan zuwa dakin hutu, duk tayi wani fiyat ta zabge sabida wahala. A wannan dan tsukin ne kuma taga kauna da karimci daga lyaye da yan uwan Alameen irin wadda bata taba tsammanin zata samu ba. Ta tabbata ita yar gata ce amma Alameen ya fita gata gaba da baya, kuma kaunar da iyaye da yan uwan shi ke mishi, duk dimbin arzikin iyayenta ita bata samu koda kwatankwacin ta ba.
Ashe ba dimbin arziki da dukiya ne gata ba, aah, matsayin da kake da shi a zuciyar iyaye da yan uwan ka. Har aka basu sallama suka dawo gida bata san kukan Baby Alameen ba, koyaushe yana jikin Aunty Saratu da kannen mahaifin sa, iyakacin ta da shi shan nono kadai. Gaba daya sun dauki kaunar duniya sun aza bisan Alameen karami musamman Faisal da Najib da shiga goma fita goma sai sun ce a kawo masu yayansu.
Bayan sunan Alameen ne suka doshi Daddy da alfarmarsu na ya yafewa mahaifiyarsu kurakuranta, domin hakika tayi nadama mara iyaka. Daddy sai ya yi murmushin sa mai nufin alamura da dama kamar koyaushe zai yi wata magana mai muhimmanci. Ya ce,
“In don ni ne ai ba abinda tayi mun, ban da kaunata da take da ku yayan ta. Wadanda ta zalinta kam suna can inda suke, don haka ta je na yafe mata duniya da lahira. Amma maganar wai ta dawo dakinta bata taso ba, domin mai hali baya fasa halin sa.
A yanzu kam girma ya hau ni, ina bukatar hutu, bazan iya jurar tashin hankali ba. Don haka ku je ku tambayeta idan har ta shirya zama na amana da zuciya daya da duk wanda na kawo cikin gidan nan na ajiye, to ana maraba da ita. Idan kuma akasin haka ne a zuciyarta to don Allah ta nemi wani gidan don wallahi a yanzu bazan iya jure halinta ba!
To bayan dogon kai ruwa rana da kyar da sidin goshi Aunty Saratu ta shawo kan Daddyn ya yarda da komen Hajiyar da babu shakka ta darastu da rayuwar duniya. Har kasa ta tsugunna neman gafarar Saratun tare da alkawarta mata tazo ne su yi zama na amana da aminci na har abada. Saratu ta tabbatar mata duniya da lahira ta yafe mata domin yayanta sun gama mata komi a rayuwa. Ta nemi Intisar domin neman gafarar ta, inda ake sanar da ita tana Alkahira tana karatu.
*****
Bayan Shekara Daya
Faisal Bello Makarfi ke taka matattakalar da zata sadashi da falon Daddy Makarfi cikin sassarfa, sanye cikin farar shirt product din DKNY da bakin wandon Tokyo da misalin karfe shidda na yammacin ranar Lahadi. Isowar shi kenan cikin garin, kamar kullum, a yau ma ya saya kwayar idanun shi cikin bakin gilashi domin boye halin da kwayar idon shi ke ciki.
Ya yi sallama a babban falon kana ya jinkirta har ruwa sanda Daddyn yayi masa iznin shigowa. Zaune yake ya tasa allon computer (Laptop) a gabansa bisa tebir inda suke musayen sako da diyarshi Inteesar tana bashi labarin karatun su a makaranta. Ba tare da ya dauke hankalin shi daga computern ba ya amsa sallamarsa tare da nuna masa wajen zama daga gefen sa.
Aunty Saratu ta shigo dauke da babbar warmer da kofunan shan ruwa ta aza daga can kan dining tana murmushi tace aah bakin Ikko ne sai yanzu, kai da tun jiya muke tsammanin ka. Ya ce wallahi kuwa shirye shiryen tafiyana ne ya tsaida ni, kin san babu biza mai wuya irin ta U.K.
A sannan ne Daddy ya cira kai ya bishi da kallo na mamaki. Sannu a hankahi kuma cikin dan kankanin lokacin yayi nazarin wasu muhimman abubuwa da dama a tare da yaron. Ya sa hannu ya fidda mudubin idonsa ya kara duban Faisal sosai. Ta fahimci uban da dan na bukatar privacy domin tattauna matsalolinsu sai bata matsa da tambayar me zai je yi ba ta ce Allah ya shige mana gaba. Daga haka ta ba su waje.
Daddy ya ce cikin wata murya mai kama da umarni.
Faisal ina zaka je?
Yayi dan dawurwura na dabarbarcewa da rashin kwakkwarar hujja ya ce am eh, Daddy, admission dana nema tun shekarar baya a can Birmingham domin karo Ph D dina, har na manta kawai sai shekaranjiya suka aiko min, to shine nazo in yi muku sallama, zan ta fi.
Daddy ya ce Faisal, me ke damun ka? Kana kallon kan ka a mudubi kuwa? Tun bayan rasuwar Alameen na ke lura da kai babu cigaba a alamarinka, kullum kara lalacewa ka ke. Wannan ramar da kake tayi a kullum kamar kudin guzuri ta mece ce?
Yaji idanuwan sa sun ciko taf da hawaye amma yayi kokarin maida su. Cikin jarumtaka yace Allah babu komi Daddy.
Yace to kaima Faisal ko dan uwanka zaka bi ne ku barni ni daya? A wannan lokacin duk jarumtakarsa saida hawayen suka balle. Ya zare gilashin sa a lokacin ne Daddyn ya samu damar ganin yadda idanuwan sa suka fada sosai, baya ga kadawa da suka yi sukayi jawur kamar gauta. Ya ce,
“Ina adduar Allah ya bani tsawo ran da zan kula da kai a gaba dayan ragowar rayuwar ka, kamar yadda ka sadaukar da kuruciyarka wajen kulawa, hidimar mu da tarbiyyantar da mu.�
Ya ce, “In haka ne Faisal me yasa zaka bar ni? Me yasa baka son tsugunawa a waje daya? Yau kana can gobe kana nan kamar wani tsuntsu. Ka kasa tsayawa ka ginawa kanka rayuwa ta da namiji. Ba ka ko tunanin yin aure! Karatu dai karatu kadai Faisal kaman alhuda huda?
Duba kaga kanin bayanka matar sa tsohon ciki gareta, haihuwa yau ko gobe. Dubi Alameen ya tafi, amma ga Alameen Alameen nan na yawo cikin gidan nan yana tuna mana da shi muna yi mishi addua, ko ba zaka yi aure domin bukatar kanka da cikar mutuncika ba, kayi domin shi kansa ibada ce mai zaman kanta.
Ban san me kake nufi da rayuwar ka ba, ban san meye planning dinka a rayuwar nan ba. Ina jiye maka tsoron kazo duniyar a banza ka koma a hofi. In kana ganin bani iya yi maka maganin matsalarka to a kalla zan baka shawara wadda kai a shekarun ka bazaka hangosu ba. Ko kuma mutuwar Alameen ce ta ke nukurkusar ka har yanzun? Take neman kayar da kai tun karfin ka bai kare ba?�
Yasa hankici ya share idonsa ya share dogon karan hancinsa ya ce,
“Aah Daddy, na riga nayi tawakkalin cewa ya tafi, ba kuma zai kara dawowa ba.� Ya ce,
“Madallah, ni dai da zaka bi son raina da ka hakura da tafiyar nan ka rungumi aikin ka an kuma daura maku aure da matar marigayi Ihsan da ka faranta mini, ko ba komai yarinyar ta nuna mana ita mai kaunar mu ce ba wai abinda muka mallaka ba. na dade ina kissima yiwuwar hakan a zuciyata ba tun yau ba..�
Ya dago cikin wani irin yanayi na firgici da tashin hankali ya dubi mahaifinsa, kana cikin nutsuwa yace
“Daddy! Na rokeka alfarma, don girman Allah koda wasa kada ka kara tunanin zancen nan balle ka fada wani ya ji. Kada ka bari alamarin yayi tasiri a zuciyarka don Allah? Yaya ma zaayi ka yi wannan tunanin? Zaka karasani kwanana bai kare ba.
Ka bar ni in ji da ciwon da zuciyata ke yi. Ba matar da Alameen ya aura akan yana so ya tafi ya bari ba don ba ya so ba, ko yarinyar da ya taba nema bazan iya aure ba balle matar sa. Kayi min uziri ka karbi hanzari na, in dai tafiya ce na fasa amma don Allah, kada ka kara ce min wani abu makamancin wannan.
Daddy ya yi murmushi ya ce yaro dai yaro ne. To kaje ka kawo min yarinyar da kake so cikin kwanaki goma rak! Amma in ba haka ba zan daura aurenka da Ihsan a ranar da kwanakin nan suka cika. Na gaya maka na kara gaya maka babu wasa cikin magana ta.
Cikin matsananciyar damuwa ya ce ni bani da wata yarinya da na ke so. Ban taba son wata ya mace a duniya ba. Alameen kadai na ke so!!! Don haka na baka wuka da nama ka zartar da duk hukuncin da ka ga dama a kaina, ka zabamin ko wacece amma ka taimake ni Daddy kada ka aura min matar Alameen. Wallahi zan gudu in bar garin, don ni Ihsan Yaya ta nake ganinta.
Saura kadan dariya ta kwace masa amma ya cije ya daure yace shikenan, tashi je ka sai na neme ka. Sai dai ina mai gargadinka ka cire abinda ke damunka daga zuciyar ka domin tsira da lafiyarka. Babu wata cuta da Allah ya saukar a doron kasa da bai saukar da maganin ta ba. Ka kaiwa Sarki Allah kukan ka amma ba wannan damuwar da ka sawa ran ka ba babu gaira babu dalili.
Ya mike kamar wanda kwai ya fashewa a ciki ya doshi sassan Anti Saratu. Tun daga hangoshi Alameen karami ya watsar da kayan wasan shi ya rarrafo da hamzari ya kama kafafun shi, shi kuma yayi gaggawar russunawa ya daukeshi ya rungume a kirjin shi.
A lokacin ita Ihsan ta tafi asibitin Alameen Memorial da ake canzawa suna maimakon MERITIME. Ko ba don haka bama a dan tsukin bata samun zama sabida shirye shiryen bude asibitin da ya gabato, tana sa ran yaye Alameen karami ne ma cikin wannan watan mai kamawa domin hidimomin sun mata yawa, ga tafiyar ta karin karatu saura watanni (3) kacal.
A kan Alameen bata da kaico ta san Anti Saratu na iya kokarin ta a kan sa, haka Hajiyar Alameen duk wani buri da tattalinta ya taallaka ne a kan dan yaron da bai ma san ko shi wane ne ba. Motsi kadan zata shigo sassan Antin tana ina maigidana ne? Ban ji duriyar sa ba tun dazu, wane shagalin yake yi ne?
Sai dare aka fito da Ihsan zuwa dakin hutu, duk tayi wani fiyat ta zabge sabida wahala. A wannan dan tsukin ne kuma taga kauna da karimci daga lyaye da yan uwan Alameen irin wadda bata taba tsammanin zata samu ba. Ta tabbata ita yar gata ce amma Alameen ya fita gata gaba da baya, kuma kaunar da iyaye da yan uwan shi ke mishi, duk dimbin arzikin iyayenta ita bata samu koda kwatankwacin ta ba.
Ashe ba dimbin arziki da dukiya ne gata ba, aah, matsayin da kake da shi a zuciyar iyaye da yan uwan ka. Har aka basu sallama suka dawo gida bata san kukan Baby Alameen ba, koyaushe yana jikin Aunty Saratu da kannen mahaifin sa, iyakacin ta da shi shan nono kadai. Gaba daya sun dauki kaunar duniya sun aza bisan Alameen karami musamman Faisal da Najib da shiga goma fita goma sai sun ce a kawo masu yayansu.
Bayan sunan Alameen ne suka doshi Daddy da alfarmarsu na ya yafewa mahaifiyarsu kurakuranta, domin hakika tayi nadama mara iyaka. Daddy sai ya yi murmushin sa mai nufin alamura da dama kamar koyaushe zai yi wata magana mai muhimmanci. Ya ce,
“In don ni ne ai ba abinda tayi mun, ban da kaunata da take da ku yayan ta. Wadanda ta zalinta kam suna can inda suke, don haka ta je na yafe mata duniya da lahira. Amma maganar wai ta dawo dakinta bata taso ba, domin mai hali baya fasa halin sa.
A yanzu kam girma ya hau ni, ina bukatar hutu, bazan iya jurar tashin hankali ba. Don haka ku je ku tambayeta idan har ta shirya zama na amana da zuciya daya da duk wanda na kawo cikin gidan nan na ajiye, to ana maraba da ita. Idan kuma akasin haka ne a zuciyarta to don Allah ta nemi wani gidan don wallahi a yanzu bazan iya jure halinta ba!
To bayan dogon kai ruwa rana da kyar da sidin goshi Aunty Saratu ta shawo kan Daddyn ya yarda da komen Hajiyar da babu shakka ta darastu da rayuwar duniya. Har kasa ta tsugunna neman gafarar Saratun tare da alkawarta mata tazo ne su yi zama na amana da aminci na har abada. Saratu ta tabbatar mata duniya da lahira ta yafe mata domin yayanta sun gama mata komi a rayuwa. Ta nemi Intisar domin neman gafarar ta, inda ake sanar da ita tana Alkahira tana karatu.
*****
Bayan Shekara Daya
Faisal Bello Makarfi ke taka matattakalar da zata sadashi da falon Daddy Makarfi cikin sassarfa, sanye cikin farar shirt product din DKNY da bakin wandon Tokyo da misalin karfe shidda na yammacin ranar Lahadi. Isowar shi kenan cikin garin, kamar kullum, a yau ma ya saya kwayar idanun shi cikin bakin gilashi domin boye halin da kwayar idon shi ke ciki.
Ya yi sallama a babban falon kana ya jinkirta har ruwa sanda Daddyn yayi masa iznin shigowa. Zaune yake ya tasa allon computer (Laptop) a gabansa bisa tebir inda suke musayen sako da diyarshi Inteesar tana bashi labarin karatun su a makaranta. Ba tare da ya dauke hankalin shi daga computern ba ya amsa sallamarsa tare da nuna masa wajen zama daga gefen sa.
Aunty Saratu ta shigo dauke da babbar warmer da kofunan shan ruwa ta aza daga can kan dining tana murmushi tace aah bakin Ikko ne sai yanzu, kai da tun jiya muke tsammanin ka. Ya ce wallahi kuwa shirye shiryen tafiyana ne ya tsaida ni, kin san babu biza mai wuya irin ta U.K.
A sannan ne Daddy ya cira kai ya bishi da kallo na mamaki. Sannu a hankahi kuma cikin dan kankanin lokacin yayi nazarin wasu muhimman abubuwa da dama a tare da yaron. Ya sa hannu ya fidda mudubin idonsa ya kara duban Faisal sosai. Ta fahimci uban da dan na bukatar privacy domin tattauna matsalolinsu sai bata matsa da tambayar me zai je yi ba ta ce Allah ya shige mana gaba. Daga haka ta ba su waje.
Daddy ya ce cikin wata murya mai kama da umarni.
Faisal ina zaka je?
Yayi dan dawurwura na dabarbarcewa da rashin kwakkwarar hujja ya ce am eh, Daddy, admission dana nema tun shekarar baya a can Birmingham domin karo Ph D dina, har na manta kawai sai shekaranjiya suka aiko min, to shine nazo in yi muku sallama, zan ta fi.
Daddy ya ce Faisal, me ke damun ka? Kana kallon kan ka a mudubi kuwa? Tun bayan rasuwar Alameen na ke lura da kai babu cigaba a alamarinka, kullum kara lalacewa ka ke. Wannan ramar da kake tayi a kullum kamar kudin guzuri ta mece ce?
Yaji idanuwan sa sun ciko taf da hawaye amma yayi kokarin maida su. Cikin jarumtaka yace Allah babu komi Daddy.
Yace to kaima Faisal ko dan uwanka zaka bi ne ku barni ni daya? A wannan lokacin duk jarumtakarsa saida hawayen suka balle. Ya zare gilashin sa a lokacin ne Daddyn ya samu damar ganin yadda idanuwan sa suka fada sosai, baya ga kadawa da suka yi sukayi jawur kamar gauta. Ya ce,
“Ina adduar Allah ya bani tsawo ran da zan kula da kai a gaba dayan ragowar rayuwar ka, kamar yadda ka sadaukar da kuruciyarka wajen kulawa, hidimar mu da tarbiyyantar da mu.�
Ya ce, “In haka ne Faisal me yasa zaka bar ni? Me yasa baka son tsugunawa a waje daya? Yau kana can gobe kana nan kamar wani tsuntsu. Ka kasa tsayawa ka ginawa kanka rayuwa ta da namiji. Ba ka ko tunanin yin aure! Karatu dai karatu kadai Faisal kaman alhuda huda?
Duba kaga kanin bayanka matar sa tsohon ciki gareta, haihuwa yau ko gobe. Dubi Alameen ya tafi, amma ga Alameen Alameen nan na yawo cikin gidan nan yana tuna mana da shi muna yi mishi addua, ko ba zaka yi aure domin bukatar kanka da cikar mutuncika ba, kayi domin shi kansa ibada ce mai zaman kanta.
Ban san me kake nufi da rayuwar ka ba, ban san meye planning dinka a rayuwar nan ba. Ina jiye maka tsoron kazo duniyar a banza ka koma a hofi. In kana ganin bani iya yi maka maganin matsalarka to a kalla zan baka shawara wadda kai a shekarun ka bazaka hangosu ba. Ko kuma mutuwar Alameen ce ta ke nukurkusar ka har yanzun? Take neman kayar da kai tun karfin ka bai kare ba?�
Yasa hankici ya share idonsa ya share dogon karan hancinsa ya ce,
“Aah Daddy, na riga nayi tawakkalin cewa ya tafi, ba kuma zai kara dawowa ba.� Ya ce,
“Madallah, ni dai da zaka bi son raina da ka hakura da tafiyar nan ka rungumi aikin ka an kuma daura maku aure da matar marigayi Ihsan da ka faranta mini, ko ba komai yarinyar ta nuna mana ita mai kaunar mu ce ba wai abinda muka mallaka ba. na dade ina kissima yiwuwar hakan a zuciyata ba tun yau ba..�
Ya dago cikin wani irin yanayi na firgici da tashin hankali ya dubi mahaifinsa, kana cikin nutsuwa yace
“Daddy! Na rokeka alfarma, don girman Allah koda wasa kada ka kara tunanin zancen nan balle ka fada wani ya ji. Kada ka bari alamarin yayi tasiri a zuciyarka don Allah? Yaya ma zaayi ka yi wannan tunanin? Zaka karasani kwanana bai kare ba.
Ka bar ni in ji da ciwon da zuciyata ke yi. Ba matar da Alameen ya aura akan yana so ya tafi ya bari ba don ba ya so ba, ko yarinyar da ya taba nema bazan iya aure ba balle matar sa. Kayi min uziri ka karbi hanzari na, in dai tafiya ce na fasa amma don Allah, kada ka kara ce min wani abu makamancin wannan.
Daddy ya yi murmushi ya ce yaro dai yaro ne. To kaje ka kawo min yarinyar da kake so cikin kwanaki goma rak! Amma in ba haka ba zan daura aurenka da Ihsan a ranar da kwanakin nan suka cika. Na gaya maka na kara gaya maka babu wasa cikin magana ta.
Cikin matsananciyar damuwa ya ce ni bani da wata yarinya da na ke so. Ban taba son wata ya mace a duniya ba. Alameen kadai na ke so!!! Don haka na baka wuka da nama ka zartar da duk hukuncin da ka ga dama a kaina, ka zabamin ko wacece amma ka taimake ni Daddy kada ka aura min matar Alameen. Wallahi zan gudu in bar garin, don ni Ihsan Yaya ta nake ganinta.
Saura kadan dariya ta kwace masa amma ya cije ya daure yace shikenan, tashi je ka sai na neme ka. Sai dai ina mai gargadinka ka cire abinda ke damunka daga zuciyar ka domin tsira da lafiyarka. Babu wata cuta da Allah ya saukar a doron kasa da bai saukar da maganin ta ba. Ka kaiwa Sarki Allah kukan ka amma ba wannan damuwar da ka sawa ran ka ba babu gaira babu dalili.
Ya mike kamar wanda kwai ya fashewa a ciki ya doshi sassan Anti Saratu. Tun daga hangoshi Alameen karami ya watsar da kayan wasan shi ya rarrafo da hamzari ya kama kafafun shi, shi kuma yayi gaggawar russunawa ya daukeshi ya rungume a kirjin shi.
A lokacin ita Ihsan ta tafi asibitin Alameen Memorial da ake canzawa suna maimakon MERITIME. Ko ba don haka bama a dan tsukin bata samun zama sabida shirye shiryen bude asibitin da ya gabato, tana sa ran yaye Alameen karami ne ma cikin wannan watan mai kamawa domin hidimomin sun mata yawa, ga tafiyar ta karin karatu saura watanni (3) kacal.
A kan Alameen bata da kaico ta san Anti Saratu na iya kokarin ta a kan sa, haka Hajiyar Alameen duk wani buri da tattalinta ya taallaka ne a kan dan yaron da bai ma san ko shi wane ne ba. Motsi kadan zata shigo sassan Antin tana ina maigidana ne? Ban ji duriyar sa ba tun dazu, wane shagalin yake yi ne?