← Book details Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 67 OF 90

Sashe 67

Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Ubangiji yayi miki albarka Saratu, ya zama jagoranki a rayuwa, ya baki aljannah mafificiya sakamakon biyayyar nan da kike yi mun a gidan duniya. Kada Allah ya nuna min ranar da Ameenu zai tozarta ni a idonki.�

Ta sunkuyar da kai cike da kunya, a ranta ko cewa take ai ko Aminu kullum yankar tsokar jikinta zai ke yi yasa a miya, zata daure ba tare data gayawa Daddyn ba. Ya ce,

“Abinda nake so dake a karshe shine ki ji abinda na ce da ke, ki bi mahaifiyarki su rakaki makaranta, ki maida hankali kan abinda ya kai ki, muma insha Allah zamu ke zuwa dibaku a kai-akai, in kun samu hutu ki zauna tare da su har mu ji me Al’ameen da Mamar sa suke ciki a san abin yi.

Da dai za’a hada auren ku da na su Najib ne amma ina ga yanzu za’a fara yin nasun, har sai tazo tukun (Hajiyar), kuma ki saki jiki da ‘yan uwanki don Allah.�

Cike da murmushi tace ‘I can do anything for your sake, Dad (zan iya yin komi domin ka Babana)� ya ce,

“To Allah yayi miki albarka.�

Mu karasa a littafi na hudu kuma na karshe insha Allahu. Taku har abada,

� Sumayyah Abdulkadir.

How much do you like this story?
5/14/22, 09:26 - Ummi Tandama😇: ____________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book four

*@Takori*

Page1ï¸âƒ£

Alkawarin da ta yiwa Daddy bata karya ba. Ranakun da suka biyo baya, ta karesu ne cikin farin cikin da walwala ga kowa. Kowa a gidan yayi mamakin canzawarta haka farat daya sai dai babu wanda ya tambayi dalilin canzawar tata.

Ko babu komi ta samu courage da relief daga rudanin da zuciyarta ke ciki. Alameen bai zo ba a washegari, ta tabbatar duk inda yake yana bisa hanyar neman Hajiyar sa, a Dubai ne ko a Kadunan ne oho su suka sani!

Ta tabbatarwa kanta lallai wanda ya rasa abokin shawara abin tausayi ne, ita dama tun fil azal Daddy ne abokin shawararta sai ko Ya Faisal wanda a yanzu baya yi da ita, da wuya su bata shawarar da in tabi bata ganin yakini a ciki. Hankalin kowa ya kwanta musamman yan uwanta da basu san wainar da suke soyawa ita da Babanta ba, wadanda a yanzu sabon shafin soyayya ne mai karfi aka bude koko in ce ake kara kullawa tsakanin Najib da Hidayah.

Wayewar garin litinin sukayi sallama da kowa har da Daddy da kansa a rakiyarsu (Airport) din Abuja, Najib da Hidayah dai kamar bazaa rabu ba illa sun yi alkawarin kasancewa a waya a kullum kamin a mallaka masu juna, hakannan shi Najib din za suke zuwa da Daddy.

Zahra taki barin Haj. Hadiza kememe har shidewa ta shiga yi da Khaleel ya dage sai ya amsheta, kawai sai aka ji Anti Saratu ta ce,

sai ku tafi da ita a yayeta, in ma zaku rike na baku halak malak. Ban sani ba dai ko Daddin Ameenu na da uzuri? Daddy yayi murmushi yace umh-uhm, Allah ya kiyaye hanya Zahrah, Zahrah Allah ya kai ku lafiya!

Haj. Hadiza ta rungume Zahra tsam-tsam har da hawayenta, ta rasa bakin godiya bisa dimbin karamcin wadannan mutane, bata san me zata yi ta saka musu ba itama banda mallakawa yayansu tsala-tsalan yan matan ta, sai Ambassador ne kema Daddyn matukar godiya, su kadai suka san me suka kukkula kan auren yayan su ba tare da sanin yayan bama.

Kwanan Intisar kwata-kwata ukku a gidan mahaifiyarta a kasar Korea, Abbansu ya maida ta Riyadh. Makarantar da fi so a rayuwarta, makarantarta ta baya, makarnatar da ta zamo silar warwarewar alamuran ta da gajarta bakin-cikin rayuwarta, tunda kuwa anan ne ta hadu da su Hidayah, har suka dangana ta ga mahaifiyarta.

Makarantar da ko a mafarki bata kara yin na dawowa cikinta ba, don tana ganin bazata kuma samun irin wannan gatan ba. To haka alamarin Ubangiji yake, don haka yake cewa La Taknadu min Rahmatullah (Wato kada ku fidda rai da rahmar Allah) domin buwayar shi ta wuce mithali. Hakannan duk wani SIRADI a rayuwa da sannu in an yi hakuri zaa tsallakeshi, ba kuma inda hakuri da fawwalawa Allah alamura baya kai dan adam.

Ta daga kanta sama a cikin ajinsu, kana ta sunkuyar. Ta yi duba ga rayuwarta mai juyawa tamkar a majigi. Ta kara jin tsoron Allah, tsigar jikinta ya tashi yarrrr! Ta kara tsarkake shi a zuciyarta, kadaitaccen sarki mai juya alamura yadda yaso. Tayi duba izuwa wahalolin da ta sha a rayuwa, wai yanzu duk sun zama tarihi. Ita kanta duniyar haka take, no condition is parmanent (ba wani yanayi da yake tabbatacce). Saratu ta watsar da tunanin komi ta rungumi karatun ta bil-hakki. Har yanzu burinta yana nan kan son gyara rayuwar alummah!

Ta girgiza da labarin mutuwar mutuminta Dr.Alhassan, bayan auren sa da kawarta Rabikha. Ta jima tana yi mai Addu’ar Rahma da gafara wurin Ubangiji. An kai ta aji shidda ne, don haka bata wasa. Da yawan Malaman da ta sani a da, basu bane a yanzu, wasu an canza su, wasu an kara masu girma.

Ita kanta shugabar makarantar da ta sani a da Ayyush Siddik ba ita bace a yanzu. Tace ashe ko ina ma haka abubuwa ke juyawa ba a kanta kadai ba! Bata kuma kara bi ta kan komi ba sai karatunta, ga wayar yan uwanta tana samu akai-akai, sai dai Alameen ko sau daya bai kira ta ba.

Ranar da suka fara jarrabawar gwaji Haj. Hadiza da Ambassada suka je mata, ba karamin farin ciki tayi ba, don rabonta da ganin wani nata watanni bakwai kenan. Anan ne suke gaya mata Hunainah ta wuce Jamiar Alazhar Hidayah kuma an daura auren su da Najib suna honey-moon a can Al-kahiran, tayi mamaki kwarai da Hidayah bata gaya mata ba, gashi kuma suna waya.

Daga baya ne ta tuna cewa Hidayah ta sha gaya mata bata son ta rigata yin aure, so take ayi komi nasu tare. In kuma hakan bata samu ba ita kam bazata ji dadin yin auren ba.

Auren Hidayah da Najib ya tabbaar mata har yanzu Alameen bai dawo daga gun Mamarsa ba! Ko dai ta ja rayin sa kan nata, ko kuma wani mummunan alamari zai faru, wanda take gudu, take guje masa. Ko kuma kwata-kwata bata amince ba shi ya sa ya rabu da ita? Bata sani ba. Ba irin tunanin da baya zuwa mata a rai amman ta ki gasgata kowanne, kowanne tana yi mai uzuri ne da cewa Alamin zai dawo gareta komi rintsi ba zai bari Hajiya ta rabasu ba.

Ramadhan 20/10 Hijriyyah
Allah Sarki! Alameen Bello ne ke tafe cikin motarshi (ash colour Rio), sanye da Jamfa da wando na bakin yadin Filted. Ya saya raunnanar kwayar idonshi cikin bakin dark glasses akan hanyarshi ta zuwa air-port din garin Abuja domin dauko mahaifiyarsa da jirgin data shigo daga Dubai zai sauketa a yau.

Yayi parking a inda aka tanada domin adana motoci ya karasa reception ya samu gefen wata kujera ya rage tsawo. Kada kaso ka tona zuciyar sa da ke bugu da sauri-da-sauri mai cikke da kunci, fargaba gami da igiyar so da ta yi mata dabaibayi.

Idan har ka san Dr. Alameen Bello a da, to a yanzu sai ka wuceshi ba tare da ka shaida shi ba; gaba daya ya kare, sai tsayin da karan hancin gami da fararen idanun kadai.

Yayi zaman akalla mintuna talatin kamin a fara shelar landing din jirgin. Tamkar kazar da kwai ya fashewa a ciki, ya mike yana mai dauriya da karfafa kansa da cewa akwai jin kai na uwa, akwai kauna ta Uwa ga dan ta. In ta kalleni ai zata tausaya mini, ita kanta tasan ba haka na dawo ba, tasan na zamo mara amfani, zan kuma kare rayuwa ta a hakan muddin bata bani abinda zuciyata ke muradi ba, zan gaya mata zuciya na ciwo, duk wani bugu da take yi Intisar ne a ciki, zan fadi, zata rasa ni muddin tayi min shamaki da Halimanaaa.

Bai sani ba, ta dade a tsaye gaban sa, sanye da koriyar atamfa sufa, ta yane jikinta da yalwataccen mayafi, ta dade tana nazarin mugun zabgewar da yayi, kai da alama baya ganin abinda yake gabansa ma, baya jin taku balle gane abinda ke faruwa a gabansa. Ta mika hannuwa ta rungume shi ta soma kuka ta ce,

“Ameenu mutuwa zaka yi ne?�

A sannan ne ya dawo hayyacinsa, ya runtse ido cike da farin cikin saukar ta lafiya, ya russuna ya dauki Jakarta ya rataya yajata har zuwa inda ya adana motarsa. Ya bude mata gidan baya ta shiga ya rufe, ya aje jakar a gefe ya zago ya zauna mazaunin shi, ya kakaro murmushi mai kwantar da hankali ya ce,

“Nayi fama da cuta ne Hajiya, amma alhamdulillahi naji sauki, nayi zaton an fada maki?�

Tayi ajiyar zuciya tace ban zaci abin yayi kamarin haka ba, shin me ke damun ka? Ya lumshe ido yayi murmushi, ya bude su duka a kan ta ya ce,

“Ciwon Zuciya!�

Wadannan su ne kalami mafi muni da ta taba ji a rayuwarta, suka kuma diran mata tamkar kibiya a kahon zuci. Muryar ta na karkarwa tace kai ko meke damunka, da har ya janyo hakan? Me ka rasa a rayuwa da zaka sanyama ranka damuwa? Yayi murmushi yace in kin so Hajiyana, zan iya murmurewa kamar ban taba yi ba, haka in kin so, zai iya zama ajali na. Tace (tana mai girgiza kai da karfi)

kada Allah ya nuna min wannan ranar!

Daga haka ta ja bakinta tayi shiru. Ganin ya dau hanyar gidan Babansa ta daka mai tsawa mai firgitarwa ta ce,

“Kai, ina zaka kai ni? Gidan Babana zaka kai ni! Ko baka ji ba?� Ya ce,

“Na ji Hajiya na, kuma a bisa umarnin ki nake har kullum.�

Ya karkatar da kan motar ya dauki hanyar Kaduna. Sai da tayi sallah, ta huta suna hira da mahaifiyar ta kan kayan da ta turo daga can Dubai din, ya shigo daga masallacin da ke kofar gidan, bayan ya samu jamin sallar laasar, duk suka dube shi.
Chapter 67 · 0% Book details