Sashe 60
Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wata rana irin ta yau bazaki ganmu ba sai ki san inda kuma zaki je tunda in kina da kunya bazaki cigaba da zama a gidan ubansa ba!�
Anti Saratu ta ce, “A’aaah! Ya isa haka nan, sai ko in ikon haihuwa da shayarwa zaki nuna min Haj. Hadiza, amma in ba hakaba ni Saratu na rantse in har Intisar bata so bazata auri Aminu ba.� Inteesar ta kara fashewa da kuka a ranta cewa take
“Ni Saratu na shiga uku, tsakanina da Al’ameen Allah Ya isa, yau ina zansa kaina gashi ya janyo su Mama suna fada a kaina?�
Hidayah da Hunainah kuwa rungume suke da ‘yar uwarsu suna tayata koka abinda take kokamawa, da baza su ce ga hakikaninsa ba, ba suce ko uffan ba don baya daga cikin tarbiyyarsu tsoma baki a maganar manya in har ba an nemi jin ta bakinsu ba, amma kam da sunbi bayan Mamarsu da Antin su Hajjo don a duniya ba su ga wanda ya dace da Yayar su kamar Al’ameen ba.
A ranar mutanen Makarfi suka koma, Daddy yayiwa Minister Hassan da Ambasada masauki a gidan saukar bakin gidan shugaban kasa su da matan su. Ba yadda Anti Saratu bata yi da Intisar ta bi Hajiya Hadiza masaukinsu ba amma ta kiya, gani take kamar zasu gudu da ita su rabata da Mamarta, gani take in ta yi hakan ta yiwa Antin butulci, ba don bata son uwarta ba illa a yanzu da komi ya bayyana gareta take tausayin Anti Saratu, wai ashe ba itace mahaifiyarta ba amma tayi mata irin wannan rikon da wata uwar bazata yiwa dan cikinta ba, take jin ciwonta, ciwon da uwa mahaifiya zata jiwa dan ta. Matsayin data riki Anti Saratu na uwa, bai ragu ba ko kadan a zuciyarta sai ma karuwa da yayi, haka matsayin uwarta shima daban.
Ba wani sakar mata fuska Haj. Hadiza takeyi can ba shiyasa tafi shakuwa da Hajjo cikin dan lokaci, su dama su Hunainah ba bakinta bane, haka Baban su yadda yake janta a jiki, sai take kwatantashi da Daddy.
In ka ganta cikin kannen ta kamar ‘yan uku, sun zamo tamkar wasu tsoka daya kowanne ji yake da dan uwan sa, motsi kadan daya zai yi ta tambayeshi menene? Su su Hajia Hadiza ma sun ce nan da kwanan uku zasu tafi saboda shirye-shiryen tafiyar su Hunainah makaranta. Sun sami (admission) a Jami’ar Al-Azhar dake Cairo ba kuma sun zo ne don su tafi da ita ba, ta ce da Aunty Saratu har abada Intisar tana nan a diyarta wannan shi yasa Anti Saratu kukan dadi.
Zarah kuwa ta zamo ‘yar Haj. Hadiza don ko nono Zahra taki amsa koyaushe tana jikin ta tun kwanakin da Antin tayi tana jinyar Intisar bata kula da ita ba Haj. Hadiza ke bata madara suka saba, da hankali ya natsa ne ta bata kememe ta ki amsa, sai ta lafe jikin Haj. Hadiza.
Anti ta ce, “Tunda kin yaye kanki ai shikenan� suma su Hunainah na matukar son Zahra da kula da ita, har fada suke akan daukanta da girmansu da komi.
A daren ranar Intisar na kwancea falon Anti duk yatsun Al’ameen sun fito rada-rada a farar fuskarta, haushi da takaici duk ba wanda babu a zuciyar nan, ga tunanin Ya Faisal, ta rasa abinda yasa yanzu ko gaisuwa bayaso ta hadasu, hakannan duk inda ya san zasu hadu a gidan to yana kokarin yaga cewa ya kaucewa wannan hanyar, in kuma guri ya kure sun hadun to ba dai ya daga ido ya dubeta ba, ya kuma bi ya daure wannan lallausar fuskar da a kullum ke tarairaya da sata nishadi tamkar bai taba sanin ta ba dadai duniyar.
Sa’annan bayan sun shigo su Najib duk sun shigo sun mata sannu da jiki anyi raha da ‘yan dararraku na abinda ya faru tsakaninsu dasu Hidayah amma banda shi.
Ta rasa wane irin laifi ne tayi mishi haka da zafi, ta dauka a yanzu ne ya dace dangantakar su ta fi ta da. Ko zata ki kula ‘ya’yan Haj. Nafi don Babarsu, ta kula su darajar kaunar da su ke nuna mata, amma ba don uwarsu ba.
Don Ko da suka ji gaskiyar dangantakar su a yanzun sai ma suka kara dagewa wajen jan ta a jiki, basa hada son ta da na kowa cikin kannensu maza, banda Ya FAISAL din ta kadai.
Shi a ranar ma ya fara zuwa aikin da ya samu a NNPC na nan Abuja kasancewar shi trained din kasar Ingila don haka bai sha wahalar samun aikin ba. Don haka ne bai zama sam, in ya fita tun safe sai dare. In ranta yayi dubu to a dugunzume yake da damuwa.
Hakikah ta damu da Faisal can baya fiye da kowa a duniya. Wannan dadaddar kaunaar mara algus tana nan har inda yau ke motsi, illa sauya matan da yayi farat daya ke damunta.
Zarah ta rarrafo ta kama kafafunta tana kallonta, bata kula taba sai Hunainah ce ta miko hannu zata dauketa tana cewa
“My sweat Zarah, share wannan kada ta make ki.�
Dai � dai lokacin da Hidayah ta fito daga toilet din dake makale da falon, da alama wanka tayi, kanta cikin “shower-cap� tana daure da faffadan towel, fatar nan lub-lub tamkar masu shiga wankan inji ga dogon wuya tubarkallah kamar barewa sak Yayarsu.
Ta fannin kirar jiki kam basu da maraba illa fasalin fuska kowa da zubin tashi, haka complexion ya banbanta.
Intisar doguwace siririya, fara tas, tamkar kirar larabawan Muritania ko ko mutanen Sirreleon. Shape din fuskarta oval mai kayatattun idanu da wadatar gassun gira, ido da sumar kai. Komi nata tamkar ita ta zaba caras-cas, kuma zam-zam ya dace da ita, tana da labba jazur sirara tamkar yankar reza, wanda in tai murmushi sai ta zama tamkar ‘yar flower (rose) yayinda Hunainah take doguwa kakkaura, kalar coffee, irinsu ne ake kira doguwar mace alkyabbar mata, ga tsayi, ga zati, duk tafi Yayun habewa da cika ido kai sai kace itace Yayar, nan ko girman kasar larabawa ce kawai kunfi shekarun ku buloras, kwata-kwata bana zata cika shekaru goma sha shidda, tana da kyawun da kai tsaye za’a kira manyan kyau, komi a waje, idanduna dara-dara farare kal, in tana kallon ka sai ka dauka hawaye zatai saboda wani sheki da kyalli da kwayar idonta keyi tamkar an diga masu mai me maiko.
Sabanin Intisar shiru-shiru mai sanyi, ita Hunainah ‘yar yi ce zakakuwa, da ba’a takalanta ta kyale, duk gemun mutun baya bata tsoro haka duk rawanin sa in ya shiga hancin ta zata fyato shi, ko da suke makaranta itace mai tare masu fada idan Hidayah ta tsokalo, da bakin rashin mutunci wa ‘ya’yan larabawan da duk suka kawo masu wargi.
Tafi Hidayah son Intisar kuma jinin su yafi gamuwa ko sanda suke makarantar ma sun fi jituwa, duk da halin su ya babanta.
Hidayah dabance a cikinsu, domin dai ita yarinya ce mai jin kanta, ‘yar gayu kuma wayayya mai son hulda da kawaye masu ilmi, don ita takan ce bata a layin kucaki (su Hunainah), ko larabawa da turawan ma da suke tare dasu sai masu aji take kawance, akwai kuma son yawon bude ido garuruwan kawayenta dai-dai ne bata jefa kafarta ba, don haka duk ta fisu budadden ido, idan ta juya harshe zuwa larabci sai ka rantse tsatson King Abdul-Azeez ce, haka in ta murda turanci bazaka ce ba Afro-America bace, haka in ta juya Faransanci, yaren manyan kasashe dai-dai ne bata iya ba. Hidayah Bashir kenan.
Tana da matsakaicin tsaho da dogon wuya kuma tafi Hunainah haske, amma bata kai Intisar ba, gatanan dai mai sheki kamar tarwada.
Ta zazzarewa kanwar ido “kawota nan, ko in make ki wallahi, ban ce da ke in ta tashi ki gayamin ba, ina jin ki wani ‘your sweat Zarah� banza mummuna, bakauya.
Kamin Hunainah ta mayar da martani Najib ya shigo cikin takunshi na kasaita na ‘ya’yan Daddy ya coge jikin kofar shigowa, ya zuba hannuwa cikin aljihun shudin Jeans dake jikinshi yayi dariya a cikin kallon Hidayah ya ce,
“Uh, su seniority manya� ai da ta daga ido taga shine sai ta saki Zarah jikin Hunainar ta falla da gudu dakin Anti.
A yadda ta fado mata dakin sai data firgita ta mike a hanzarce sukai cirko-cirko, ta ce, “Ke lafiya, sai kace wadda aka jeho ko sallama kamar wadda ta ga dodo?�
Ta cira kai ta dubi Anti Saratu ta mayar wani gefen bata san me zata ce mata ba, ta sauke sassanyan numfashi ta ce da ita me? Najib ya ganta cikin kayan wanka bayan dama can ya takura mata da kallo tun a asibiti da shigar mata hanci da kudundune?
Ta yi ajiyar zuciya ta ce, “Barshi ma dai kawai Anti� cikin murya mai kwantar da hankali da sassauci Anti ta ce,
“Hidayah, wani abin tsoro kika gani?� Tace� Lalah, actually nothing. Tambayar ki zanyi ki bani wet-lips.�
Anti ta saki dariya ta juya mata baya tana cewa.
“In kin duba kan mudubin Saratu, babu nau’in kayan kwalliyar da babu. Bayan haka na ganki da ‘kit� mai cikke da kayan kwalliya ‘wet-lips� kala-kala. Wai meyasa ‘ya’ya na suke firgita ‘yan mata ne?
Saratu ta taba sharce dan yatsa da wuka tana firan dankali saboda firgitar ganin Aminu na, to ke, karki zare don Allah.�
Ta bude baki galala! Tana kallon Antin kamar wawuya, Anti ta fita da gudu-gudunta amma bata motsa daga inda take ba. Hunainah ta shigo tana mata dariyar shegantaka ta ce,
“Yaya Najib yace ya soke ‘seniority� dinki daga yau, in kika sake takuramin zamu taru muyi miki dan banzan dukan da zaki kasa motsi.� Ta kyabe baki tana zira doguwar rigarta tana cewa,
“In seniority ne yanzu na fara, ki je ki gaya masa.�
Ba yadda bai yi ba ta fito taki, duk Anti Saratu na jin su, da ya gaji da magiyar har dakin ya bita ya tarkatota falon yana cewa,
Anti Saratu ta ce, “A’aaah! Ya isa haka nan, sai ko in ikon haihuwa da shayarwa zaki nuna min Haj. Hadiza, amma in ba hakaba ni Saratu na rantse in har Intisar bata so bazata auri Aminu ba.� Inteesar ta kara fashewa da kuka a ranta cewa take
“Ni Saratu na shiga uku, tsakanina da Al’ameen Allah Ya isa, yau ina zansa kaina gashi ya janyo su Mama suna fada a kaina?�
Hidayah da Hunainah kuwa rungume suke da ‘yar uwarsu suna tayata koka abinda take kokamawa, da baza su ce ga hakikaninsa ba, ba suce ko uffan ba don baya daga cikin tarbiyyarsu tsoma baki a maganar manya in har ba an nemi jin ta bakinsu ba, amma kam da sunbi bayan Mamarsu da Antin su Hajjo don a duniya ba su ga wanda ya dace da Yayar su kamar Al’ameen ba.
A ranar mutanen Makarfi suka koma, Daddy yayiwa Minister Hassan da Ambasada masauki a gidan saukar bakin gidan shugaban kasa su da matan su. Ba yadda Anti Saratu bata yi da Intisar ta bi Hajiya Hadiza masaukinsu ba amma ta kiya, gani take kamar zasu gudu da ita su rabata da Mamarta, gani take in ta yi hakan ta yiwa Antin butulci, ba don bata son uwarta ba illa a yanzu da komi ya bayyana gareta take tausayin Anti Saratu, wai ashe ba itace mahaifiyarta ba amma tayi mata irin wannan rikon da wata uwar bazata yiwa dan cikinta ba, take jin ciwonta, ciwon da uwa mahaifiya zata jiwa dan ta. Matsayin data riki Anti Saratu na uwa, bai ragu ba ko kadan a zuciyarta sai ma karuwa da yayi, haka matsayin uwarta shima daban.
Ba wani sakar mata fuska Haj. Hadiza takeyi can ba shiyasa tafi shakuwa da Hajjo cikin dan lokaci, su dama su Hunainah ba bakinta bane, haka Baban su yadda yake janta a jiki, sai take kwatantashi da Daddy.
In ka ganta cikin kannen ta kamar ‘yan uku, sun zamo tamkar wasu tsoka daya kowanne ji yake da dan uwan sa, motsi kadan daya zai yi ta tambayeshi menene? Su su Hajia Hadiza ma sun ce nan da kwanan uku zasu tafi saboda shirye-shiryen tafiyar su Hunainah makaranta. Sun sami (admission) a Jami’ar Al-Azhar dake Cairo ba kuma sun zo ne don su tafi da ita ba, ta ce da Aunty Saratu har abada Intisar tana nan a diyarta wannan shi yasa Anti Saratu kukan dadi.
Zarah kuwa ta zamo ‘yar Haj. Hadiza don ko nono Zahra taki amsa koyaushe tana jikin ta tun kwanakin da Antin tayi tana jinyar Intisar bata kula da ita ba Haj. Hadiza ke bata madara suka saba, da hankali ya natsa ne ta bata kememe ta ki amsa, sai ta lafe jikin Haj. Hadiza.
Anti ta ce, “Tunda kin yaye kanki ai shikenan� suma su Hunainah na matukar son Zahra da kula da ita, har fada suke akan daukanta da girmansu da komi.
A daren ranar Intisar na kwancea falon Anti duk yatsun Al’ameen sun fito rada-rada a farar fuskarta, haushi da takaici duk ba wanda babu a zuciyar nan, ga tunanin Ya Faisal, ta rasa abinda yasa yanzu ko gaisuwa bayaso ta hadasu, hakannan duk inda ya san zasu hadu a gidan to yana kokarin yaga cewa ya kaucewa wannan hanyar, in kuma guri ya kure sun hadun to ba dai ya daga ido ya dubeta ba, ya kuma bi ya daure wannan lallausar fuskar da a kullum ke tarairaya da sata nishadi tamkar bai taba sanin ta ba dadai duniyar.
Sa’annan bayan sun shigo su Najib duk sun shigo sun mata sannu da jiki anyi raha da ‘yan dararraku na abinda ya faru tsakaninsu dasu Hidayah amma banda shi.
Ta rasa wane irin laifi ne tayi mishi haka da zafi, ta dauka a yanzu ne ya dace dangantakar su ta fi ta da. Ko zata ki kula ‘ya’yan Haj. Nafi don Babarsu, ta kula su darajar kaunar da su ke nuna mata, amma ba don uwarsu ba.
Don Ko da suka ji gaskiyar dangantakar su a yanzun sai ma suka kara dagewa wajen jan ta a jiki, basa hada son ta da na kowa cikin kannensu maza, banda Ya FAISAL din ta kadai.
Shi a ranar ma ya fara zuwa aikin da ya samu a NNPC na nan Abuja kasancewar shi trained din kasar Ingila don haka bai sha wahalar samun aikin ba. Don haka ne bai zama sam, in ya fita tun safe sai dare. In ranta yayi dubu to a dugunzume yake da damuwa.
Hakikah ta damu da Faisal can baya fiye da kowa a duniya. Wannan dadaddar kaunaar mara algus tana nan har inda yau ke motsi, illa sauya matan da yayi farat daya ke damunta.
Zarah ta rarrafo ta kama kafafunta tana kallonta, bata kula taba sai Hunainah ce ta miko hannu zata dauketa tana cewa
“My sweat Zarah, share wannan kada ta make ki.�
Dai � dai lokacin da Hidayah ta fito daga toilet din dake makale da falon, da alama wanka tayi, kanta cikin “shower-cap� tana daure da faffadan towel, fatar nan lub-lub tamkar masu shiga wankan inji ga dogon wuya tubarkallah kamar barewa sak Yayarsu.
Ta fannin kirar jiki kam basu da maraba illa fasalin fuska kowa da zubin tashi, haka complexion ya banbanta.
Intisar doguwace siririya, fara tas, tamkar kirar larabawan Muritania ko ko mutanen Sirreleon. Shape din fuskarta oval mai kayatattun idanu da wadatar gassun gira, ido da sumar kai. Komi nata tamkar ita ta zaba caras-cas, kuma zam-zam ya dace da ita, tana da labba jazur sirara tamkar yankar reza, wanda in tai murmushi sai ta zama tamkar ‘yar flower (rose) yayinda Hunainah take doguwa kakkaura, kalar coffee, irinsu ne ake kira doguwar mace alkyabbar mata, ga tsayi, ga zati, duk tafi Yayun habewa da cika ido kai sai kace itace Yayar, nan ko girman kasar larabawa ce kawai kunfi shekarun ku buloras, kwata-kwata bana zata cika shekaru goma sha shidda, tana da kyawun da kai tsaye za’a kira manyan kyau, komi a waje, idanduna dara-dara farare kal, in tana kallon ka sai ka dauka hawaye zatai saboda wani sheki da kyalli da kwayar idonta keyi tamkar an diga masu mai me maiko.
Sabanin Intisar shiru-shiru mai sanyi, ita Hunainah ‘yar yi ce zakakuwa, da ba’a takalanta ta kyale, duk gemun mutun baya bata tsoro haka duk rawanin sa in ya shiga hancin ta zata fyato shi, ko da suke makaranta itace mai tare masu fada idan Hidayah ta tsokalo, da bakin rashin mutunci wa ‘ya’yan larabawan da duk suka kawo masu wargi.
Tafi Hidayah son Intisar kuma jinin su yafi gamuwa ko sanda suke makarantar ma sun fi jituwa, duk da halin su ya babanta.
Hidayah dabance a cikinsu, domin dai ita yarinya ce mai jin kanta, ‘yar gayu kuma wayayya mai son hulda da kawaye masu ilmi, don ita takan ce bata a layin kucaki (su Hunainah), ko larabawa da turawan ma da suke tare dasu sai masu aji take kawance, akwai kuma son yawon bude ido garuruwan kawayenta dai-dai ne bata jefa kafarta ba, don haka duk ta fisu budadden ido, idan ta juya harshe zuwa larabci sai ka rantse tsatson King Abdul-Azeez ce, haka in ta murda turanci bazaka ce ba Afro-America bace, haka in ta juya Faransanci, yaren manyan kasashe dai-dai ne bata iya ba. Hidayah Bashir kenan.
Tana da matsakaicin tsaho da dogon wuya kuma tafi Hunainah haske, amma bata kai Intisar ba, gatanan dai mai sheki kamar tarwada.
Ta zazzarewa kanwar ido “kawota nan, ko in make ki wallahi, ban ce da ke in ta tashi ki gayamin ba, ina jin ki wani ‘your sweat Zarah� banza mummuna, bakauya.
Kamin Hunainah ta mayar da martani Najib ya shigo cikin takunshi na kasaita na ‘ya’yan Daddy ya coge jikin kofar shigowa, ya zuba hannuwa cikin aljihun shudin Jeans dake jikinshi yayi dariya a cikin kallon Hidayah ya ce,
“Uh, su seniority manya� ai da ta daga ido taga shine sai ta saki Zarah jikin Hunainar ta falla da gudu dakin Anti.
A yadda ta fado mata dakin sai data firgita ta mike a hanzarce sukai cirko-cirko, ta ce, “Ke lafiya, sai kace wadda aka jeho ko sallama kamar wadda ta ga dodo?�
Ta cira kai ta dubi Anti Saratu ta mayar wani gefen bata san me zata ce mata ba, ta sauke sassanyan numfashi ta ce da ita me? Najib ya ganta cikin kayan wanka bayan dama can ya takura mata da kallo tun a asibiti da shigar mata hanci da kudundune?
Ta yi ajiyar zuciya ta ce, “Barshi ma dai kawai Anti� cikin murya mai kwantar da hankali da sassauci Anti ta ce,
“Hidayah, wani abin tsoro kika gani?� Tace� Lalah, actually nothing. Tambayar ki zanyi ki bani wet-lips.�
Anti ta saki dariya ta juya mata baya tana cewa.
“In kin duba kan mudubin Saratu, babu nau’in kayan kwalliyar da babu. Bayan haka na ganki da ‘kit� mai cikke da kayan kwalliya ‘wet-lips� kala-kala. Wai meyasa ‘ya’ya na suke firgita ‘yan mata ne?
Saratu ta taba sharce dan yatsa da wuka tana firan dankali saboda firgitar ganin Aminu na, to ke, karki zare don Allah.�
Ta bude baki galala! Tana kallon Antin kamar wawuya, Anti ta fita da gudu-gudunta amma bata motsa daga inda take ba. Hunainah ta shigo tana mata dariyar shegantaka ta ce,
“Yaya Najib yace ya soke ‘seniority� dinki daga yau, in kika sake takuramin zamu taru muyi miki dan banzan dukan da zaki kasa motsi.� Ta kyabe baki tana zira doguwar rigarta tana cewa,
“In seniority ne yanzu na fara, ki je ki gaya masa.�
Ba yadda bai yi ba ta fito taki, duk Anti Saratu na jin su, da ya gaji da magiyar har dakin ya bita ya tarkatota falon yana cewa,