Sashe 80
Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Bari in bar maku wajen, sai ka ji dadin sawa ta kara raina nin tunda ita dama ba kunya ce ta ishe ta ba.�
Suka yi mata dariya dukkansu. Ba ta bi ta kan su ba ta dauki kwandon kayan abinci ta yi gaba, yayinda Amabassador Basheer ya shiga bata labarin rayuwar su tun daga ruga zuwa kauyen Shanono, har zuwa tahowar su kasar Faransa. Ba shakka ta ji tausayin maman ta sosai ta kuma kara jin kaunar ta a ranta.
Sun yi shirin barci ya lura Hadiza dai fushi take da shi, tana tsaye jikin mudubi tana sharce kanta data wanke cikin kumfar pert plus ya zagaya ta baya, kyawawan fuskokin su suka koma cikin mudubin ya ce,
“Wayyo ni Bishir ina zan sa kaina? Haddizana na fushi da ni a kan laifin da ban san na yi ba ta ce ba wani nan, kome kake yi mun kana sane, tunda ai na nuna maka bana so. Yarinyar nan fa kana mancewa diyar fari ce baa sakar masu baki haka�
Ya tuntsire da dariya ya juyo ta gaba daya ya ce “Don Allah Dijangala, yaushe zaki shigo gari ne?�
Babu inda wadannan kyawawan kafafun na Dije na basu taka cikin duniya ba, amma har yau tana abu tamkar tana cikin ruga ko kaugyen Shanono?
Ta kara kumbura amma sai tayi murmushi, don yadda ya kirata da Dije rabon shi da hakan tun dawowar shi daga Jamiar Nsukka dake kudu, ta ce,
“Ai ko Annabi (SAW) ma ya ce dan kauye sai yayi shekaru arbain a birni sannan ne zai zama dan birni. Ni ko yau shekaru na ashirin da takwas a birni, ka ga kenan har yau da saurana.� Ya yi dariya ya ce,
“Naji-naji ni dai hakanan nake son Dije na, ko ta zama yar birni ko bata zama ba. Bana fatan abinda zai bata mata rai balle ya raba ni da ita. Neman alfarmar Dije na nake ta dinga sassautawa Intisar tana nuna mata kulawar ta tamkar sauran yayan ta, domin ba shakka ita din abin tausayi ne. Har yau bata kai ga samun cikakken farin ciki a rayuwar ta ba.�
Washegari tun wajen karfe tara na safe Hajiya Hadiza ta shigo dakin da suke, a lokacin duk sunyi wanka suna shiryawa ta ce, “Me kuke shiri game da zuwan bakin?�
Intisar ta ce, “Wai su waye?� Hajiyan ta juya tana ce wa,
“Nima ban sani ba, amma tunda har Daddyn da kansa ya fadi zuwan su ai kin san masu muhimmanci ne.
Akwai komi a kitchen in da abinda baku samu ba sai ku yi magana a tura direba kasuwar yan kaba don ni bana jin shiga kitchen din nan a yau.�
Intisar ta ce a ranta ‘shiga kitchen ai sai mu manyan kuku.� Ta dauki mayafin Pakistan ruwan bula da ke jikinta ta yafa ta zura silipas ta fita tana cewa da Hunainah,
“Yi kwanciyarki ki huta, ni nan da kike gani ingarma ce a wannan fanning.�
Ta tuntsire da dariya ta ce, “Ah ah zan taya ki, ai in Allah ya ce ce ka huta sai ka huta, kuma tunda gani a yanzun ko mutuwa ce na ji na gani muyi ta tare.�
Tayi murmushin da ya tuna mata da wasu alamura da dama da suka gabata ta yi gaba tana cewa, “nagode sister, balle Insha Allah sai na riga ki mutuwa, ko ba komi zaki dage wurin ganin kullum ranar Allah kin yi min addua, kin taya ni yiwa Alameen kin kuma taya ni ganar da Ya Faisal abinda yake tunani game da ni ba hakan ya ke ba, illa dai ba zai taba saurara ta ba, da ya gane wasu abubuwa da kowa bai gane ba. Kwalla ta ciko idon ta, ta yi saurin fita don bata son Hunainah ta gani, ta san halinta yanzun sai ta fita damuwa, Hunainah ta yi dan jim, can kuma tayi tagumi tace
“Oh Allah! Ka dubi wannan baiwa taka, ka bata soyayyar nan da take nema mai barazanar raba ta da duk wani farin-cikin da take ciki.�
Wayar ta da ke kasan pillow ta shiga kida cikin daddadan sauti, kamar ta kyale ta bi bayan yar uwar ta sai kuma dai ta daga, ganin bakuwar lambar mai layin glo kuma ta nan cikin gida Nigeria ta sha mamaki, ta san dai dawowar ta kenan bata hadu da kowa ba balle ta bashi nambarta, gashi ba lambar Hidaya ba bata su Najib ba.
Cikin sassanyar muryar ta mai zaki da taushi ta ce,
“Yello! Hunainah Bashir ce a kan layin?�
Daga daya bangaren Hashim ya yi wata irin ajiyar zuciya, ya ce
“Don Allah Hunnainah, ki saurare ni kar ki katse, Hashim ne da kuka gamu da shi a filin jirgi, pls Hunainah help me, zuciyar zata narke in kika ki sauraron ta?�
Ta yi murmushi, muryar shi da yanayin maganar shi cikin nutsuwa su suka fi daukar hankalin ta, cikin kwantar da murya da ita kanta bata san ta yi ba, ta ce,
“To Hashim, mai ka ke so?�
Da sauri ya ce,
“Hunainah! Hunainah na ke so don Allah!! Ta kyalkyale da siririyar dariyar ta da tafi zakin sarewa a kunnuwan shi, ya kara kwanciya sosai a doguwar kujerar da ya ke kwance, ya kankame wayar gam kamar mai tsoron kada wani ya fizge, ya cigaba da magana cikin shauki da bege.
“Allah Hunnainah tun a Air-port din Cairo kika kwance mun kai, baki bar ni da wani tunani ba ko kankani sai naki, don Allah ki amshi kokon barana ki sammun gurbi a zuciyar ki ko yaya ne zan ji dadi in tsugunna a nan har zuwa sanda zaki bani babban gurbin.
Na yi maki alkawarin Insha-Allah ba zaki yi dana sani a kaina ba, ba za kiyi da na sani da zamowa na uban yayan ki ba, zan yi kokarin zama masoyi mai amana. Ki bar hadani da sauran mazan da aka ce kina tsoro don wallahi ni ke na ke tsoro Hunainah, sai yadda kika yi da ni. Cikin kwana dayan nan rak ba ki barni da tunanin komai ba sai na kyakkyawar fuskarki da fushin ki da kame mutuncin kanki. Ki yarda ba duk mazan ne muka taru muka zama daya ba, akwai masu soyayyar tsakani da Allah, wadanda zasu iya bada rayuwar su da komi da suka mallaka a domin ki Hunainah. Ki yarda da ni you are very special (ke ta musamman ce) ko zaayi yaudara ba zaa yaudare ki ba.�
Gaba daya ya kashe duk wata laka dake tare da ita, ta zamo pale duk wani kuduri da tunani da take da shi a kan maza, Hashim ya warware shi a yau.
A tsaye take a da, amma bata san sanda ta kai ga kwanciya bisa rug-carpet dake gaban gadon ta ba. Tana murmushi rungume da wayar kamkam ta kasa cewa komi yayinda shi kuma Hashim ya cigaba da ragargaza mata zuciya da dadadan kalaman shi har ta yarda ta amince ta kuma tabbatar wannan dai na daban ne, kuma shine Mr. Right din da ta ke nema. Muryar shi ta yi kasa sosai ya ce cikin matsananciyar damuwa.
“Plz Hunainah say something mana? Shin am I accepted? Ta ce cikin shagwabarta da ta saba yiwa kowa,
“To ai kai ne dadin bakin naka yayi yawa, bayan nasan matarka ma duk hakan kake fada mata?�
Ya kyalkyale da dariya ya ce,
“Eh mana, matata ma Hunainah duk haka nake gaya mata, amma nafi son Hunainah akan Hunainah.�
Ta ce, “Itama sunanta Hunainah?�
Yadda furucin ya fito daga bakin ta cike da kishi abin tausayi bai san sanda ya kankame fillon kujerar ba, tamkar ita din ne ya kankame ya ce,
“Sunan ta kenan Hunainah Bashir, I love her very- very much!.�
Ta ja wata irin kakakarfar ajiyar zuciya, wani dadi ya ratsa shi cikin murmushi ya ce,
“To ya, Hunny na, in zo Kano domin ki? Ba zaki haramta mun ganin wannan kyakkyawar fuskar ba, ba zaki yi mun rowar wanan daddadar muryar ba?�
Ta yi dariyar ta mai ban shaawa duk da baya ganin ta ya ji ta har cikin ran sa, ya ji ta har cikin jinni da jijiyoyi, tsuma kawai yake cike da bege saida ta ja aji ta ce,
“You are welcome.�
Ya ce, “gobe-goben nan fa?�
Ta ce, “Ahah sai dai next week ban gama hutawa ba tukunnah.�
Yayi shiru kusan minti uku bai ce uffan ba, ta yi zaton ajewa yayi har zata kashe itama sai ta ji ya ce,
“Kada ki yi mamaki kamin kwana bakwan da kika ambata kin ji labarin mutuwa na, kuma ke ce sanadi Hunainah.� Ta ce,
“Me yayi zafi Hashim ko yau ne ka zo, am sorry.�
Ya ji dadin saukin kanta da saurin amsa kuskuren ta, ya na son mace mai saukin kai da rashin amfani da soyayyar da ake mata tana azabtar da mai kaunarta, ya ce,
“Na gode Hunainah, ki gayar mun da Yayar mu kamin in zo mata gaisuwar surukai, wai don Allah ya sunan ta ne?�
Ta ce, “Saratu Intisar take, zata ji sakon ka yanzun nan, don ma ta fita ne da kun gaisa, zan je tana jira na.�
Ta lura in don ta shi ne su kwana suna yi ba zai gaji ba. Ya yi murmushi ya ce,
“Wai ke mai wayo, to ai ban gaji da jin sassanyar muryar nan ba Hunainah, ni ya za ki yi da ni to?�
Ta yi muramushi ta ce, “Zan kira ka in na gama Hashim ka yi hakuri, baki ne zamu yi� Ya ce,
“Shikenan Hunainah, sai me zaki dan ce mun da zan rinka tunawa kamin bakin su tafi?�
Ta yi dariya sosai tace,
“Wohoho Hashim! Me kake ci na baka na zuba? In dai Hunainah ce ka samu, Im only yours!�
Ya cillar da wayar ya rungume filon kujerar yana na gode, na gode Hunainah and Ill forever be yours too!�
How much do you like this story?
5/16/22, 07:35 - Ummi Tandama😇: ____________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book four
*@Takori*
Page8ï¸âƒ£
Da gudu ta fada kitchen din ta kankame yar uwar ta, ta daga ta cancaras tana juyi da ita a kitchen din ta ce,
Suka yi mata dariya dukkansu. Ba ta bi ta kan su ba ta dauki kwandon kayan abinci ta yi gaba, yayinda Amabassador Basheer ya shiga bata labarin rayuwar su tun daga ruga zuwa kauyen Shanono, har zuwa tahowar su kasar Faransa. Ba shakka ta ji tausayin maman ta sosai ta kuma kara jin kaunar ta a ranta.
Sun yi shirin barci ya lura Hadiza dai fushi take da shi, tana tsaye jikin mudubi tana sharce kanta data wanke cikin kumfar pert plus ya zagaya ta baya, kyawawan fuskokin su suka koma cikin mudubin ya ce,
“Wayyo ni Bishir ina zan sa kaina? Haddizana na fushi da ni a kan laifin da ban san na yi ba ta ce ba wani nan, kome kake yi mun kana sane, tunda ai na nuna maka bana so. Yarinyar nan fa kana mancewa diyar fari ce baa sakar masu baki haka�
Ya tuntsire da dariya ya juyo ta gaba daya ya ce “Don Allah Dijangala, yaushe zaki shigo gari ne?�
Babu inda wadannan kyawawan kafafun na Dije na basu taka cikin duniya ba, amma har yau tana abu tamkar tana cikin ruga ko kaugyen Shanono?
Ta kara kumbura amma sai tayi murmushi, don yadda ya kirata da Dije rabon shi da hakan tun dawowar shi daga Jamiar Nsukka dake kudu, ta ce,
“Ai ko Annabi (SAW) ma ya ce dan kauye sai yayi shekaru arbain a birni sannan ne zai zama dan birni. Ni ko yau shekaru na ashirin da takwas a birni, ka ga kenan har yau da saurana.� Ya yi dariya ya ce,
“Naji-naji ni dai hakanan nake son Dije na, ko ta zama yar birni ko bata zama ba. Bana fatan abinda zai bata mata rai balle ya raba ni da ita. Neman alfarmar Dije na nake ta dinga sassautawa Intisar tana nuna mata kulawar ta tamkar sauran yayan ta, domin ba shakka ita din abin tausayi ne. Har yau bata kai ga samun cikakken farin ciki a rayuwar ta ba.�
Washegari tun wajen karfe tara na safe Hajiya Hadiza ta shigo dakin da suke, a lokacin duk sunyi wanka suna shiryawa ta ce, “Me kuke shiri game da zuwan bakin?�
Intisar ta ce, “Wai su waye?� Hajiyan ta juya tana ce wa,
“Nima ban sani ba, amma tunda har Daddyn da kansa ya fadi zuwan su ai kin san masu muhimmanci ne.
Akwai komi a kitchen in da abinda baku samu ba sai ku yi magana a tura direba kasuwar yan kaba don ni bana jin shiga kitchen din nan a yau.�
Intisar ta ce a ranta ‘shiga kitchen ai sai mu manyan kuku.� Ta dauki mayafin Pakistan ruwan bula da ke jikinta ta yafa ta zura silipas ta fita tana cewa da Hunainah,
“Yi kwanciyarki ki huta, ni nan da kike gani ingarma ce a wannan fanning.�
Ta tuntsire da dariya ta ce, “Ah ah zan taya ki, ai in Allah ya ce ce ka huta sai ka huta, kuma tunda gani a yanzun ko mutuwa ce na ji na gani muyi ta tare.�
Tayi murmushin da ya tuna mata da wasu alamura da dama da suka gabata ta yi gaba tana cewa, “nagode sister, balle Insha Allah sai na riga ki mutuwa, ko ba komi zaki dage wurin ganin kullum ranar Allah kin yi min addua, kin taya ni yiwa Alameen kin kuma taya ni ganar da Ya Faisal abinda yake tunani game da ni ba hakan ya ke ba, illa dai ba zai taba saurara ta ba, da ya gane wasu abubuwa da kowa bai gane ba. Kwalla ta ciko idon ta, ta yi saurin fita don bata son Hunainah ta gani, ta san halinta yanzun sai ta fita damuwa, Hunainah ta yi dan jim, can kuma tayi tagumi tace
“Oh Allah! Ka dubi wannan baiwa taka, ka bata soyayyar nan da take nema mai barazanar raba ta da duk wani farin-cikin da take ciki.�
Wayar ta da ke kasan pillow ta shiga kida cikin daddadan sauti, kamar ta kyale ta bi bayan yar uwar ta sai kuma dai ta daga, ganin bakuwar lambar mai layin glo kuma ta nan cikin gida Nigeria ta sha mamaki, ta san dai dawowar ta kenan bata hadu da kowa ba balle ta bashi nambarta, gashi ba lambar Hidaya ba bata su Najib ba.
Cikin sassanyar muryar ta mai zaki da taushi ta ce,
“Yello! Hunainah Bashir ce a kan layin?�
Daga daya bangaren Hashim ya yi wata irin ajiyar zuciya, ya ce
“Don Allah Hunnainah, ki saurare ni kar ki katse, Hashim ne da kuka gamu da shi a filin jirgi, pls Hunainah help me, zuciyar zata narke in kika ki sauraron ta?�
Ta yi murmushi, muryar shi da yanayin maganar shi cikin nutsuwa su suka fi daukar hankalin ta, cikin kwantar da murya da ita kanta bata san ta yi ba, ta ce,
“To Hashim, mai ka ke so?�
Da sauri ya ce,
“Hunainah! Hunainah na ke so don Allah!! Ta kyalkyale da siririyar dariyar ta da tafi zakin sarewa a kunnuwan shi, ya kara kwanciya sosai a doguwar kujerar da ya ke kwance, ya kankame wayar gam kamar mai tsoron kada wani ya fizge, ya cigaba da magana cikin shauki da bege.
“Allah Hunnainah tun a Air-port din Cairo kika kwance mun kai, baki bar ni da wani tunani ba ko kankani sai naki, don Allah ki amshi kokon barana ki sammun gurbi a zuciyar ki ko yaya ne zan ji dadi in tsugunna a nan har zuwa sanda zaki bani babban gurbin.
Na yi maki alkawarin Insha-Allah ba zaki yi dana sani a kaina ba, ba za kiyi da na sani da zamowa na uban yayan ki ba, zan yi kokarin zama masoyi mai amana. Ki bar hadani da sauran mazan da aka ce kina tsoro don wallahi ni ke na ke tsoro Hunainah, sai yadda kika yi da ni. Cikin kwana dayan nan rak ba ki barni da tunanin komai ba sai na kyakkyawar fuskarki da fushin ki da kame mutuncin kanki. Ki yarda ba duk mazan ne muka taru muka zama daya ba, akwai masu soyayyar tsakani da Allah, wadanda zasu iya bada rayuwar su da komi da suka mallaka a domin ki Hunainah. Ki yarda da ni you are very special (ke ta musamman ce) ko zaayi yaudara ba zaa yaudare ki ba.�
Gaba daya ya kashe duk wata laka dake tare da ita, ta zamo pale duk wani kuduri da tunani da take da shi a kan maza, Hashim ya warware shi a yau.
A tsaye take a da, amma bata san sanda ta kai ga kwanciya bisa rug-carpet dake gaban gadon ta ba. Tana murmushi rungume da wayar kamkam ta kasa cewa komi yayinda shi kuma Hashim ya cigaba da ragargaza mata zuciya da dadadan kalaman shi har ta yarda ta amince ta kuma tabbatar wannan dai na daban ne, kuma shine Mr. Right din da ta ke nema. Muryar shi ta yi kasa sosai ya ce cikin matsananciyar damuwa.
“Plz Hunainah say something mana? Shin am I accepted? Ta ce cikin shagwabarta da ta saba yiwa kowa,
“To ai kai ne dadin bakin naka yayi yawa, bayan nasan matarka ma duk hakan kake fada mata?�
Ya kyalkyale da dariya ya ce,
“Eh mana, matata ma Hunainah duk haka nake gaya mata, amma nafi son Hunainah akan Hunainah.�
Ta ce, “Itama sunanta Hunainah?�
Yadda furucin ya fito daga bakin ta cike da kishi abin tausayi bai san sanda ya kankame fillon kujerar ba, tamkar ita din ne ya kankame ya ce,
“Sunan ta kenan Hunainah Bashir, I love her very- very much!.�
Ta ja wata irin kakakarfar ajiyar zuciya, wani dadi ya ratsa shi cikin murmushi ya ce,
“To ya, Hunny na, in zo Kano domin ki? Ba zaki haramta mun ganin wannan kyakkyawar fuskar ba, ba zaki yi mun rowar wanan daddadar muryar ba?�
Ta yi dariyar ta mai ban shaawa duk da baya ganin ta ya ji ta har cikin ran sa, ya ji ta har cikin jinni da jijiyoyi, tsuma kawai yake cike da bege saida ta ja aji ta ce,
“You are welcome.�
Ya ce, “gobe-goben nan fa?�
Ta ce, “Ahah sai dai next week ban gama hutawa ba tukunnah.�
Yayi shiru kusan minti uku bai ce uffan ba, ta yi zaton ajewa yayi har zata kashe itama sai ta ji ya ce,
“Kada ki yi mamaki kamin kwana bakwan da kika ambata kin ji labarin mutuwa na, kuma ke ce sanadi Hunainah.� Ta ce,
“Me yayi zafi Hashim ko yau ne ka zo, am sorry.�
Ya ji dadin saukin kanta da saurin amsa kuskuren ta, ya na son mace mai saukin kai da rashin amfani da soyayyar da ake mata tana azabtar da mai kaunarta, ya ce,
“Na gode Hunainah, ki gayar mun da Yayar mu kamin in zo mata gaisuwar surukai, wai don Allah ya sunan ta ne?�
Ta ce, “Saratu Intisar take, zata ji sakon ka yanzun nan, don ma ta fita ne da kun gaisa, zan je tana jira na.�
Ta lura in don ta shi ne su kwana suna yi ba zai gaji ba. Ya yi murmushi ya ce,
“Wai ke mai wayo, to ai ban gaji da jin sassanyar muryar nan ba Hunainah, ni ya za ki yi da ni to?�
Ta yi muramushi ta ce, “Zan kira ka in na gama Hashim ka yi hakuri, baki ne zamu yi� Ya ce,
“Shikenan Hunainah, sai me zaki dan ce mun da zan rinka tunawa kamin bakin su tafi?�
Ta yi dariya sosai tace,
“Wohoho Hashim! Me kake ci na baka na zuba? In dai Hunainah ce ka samu, Im only yours!�
Ya cillar da wayar ya rungume filon kujerar yana na gode, na gode Hunainah and Ill forever be yours too!�
How much do you like this story?
5/16/22, 07:35 - Ummi Tandama😇: ____________________________
*âœðŸ? SIRADIN RAYUWAâœðŸ?*
Book four
*@Takori*
Page8ï¸âƒ£
Da gudu ta fada kitchen din ta kankame yar uwar ta, ta daga ta cancaras tana juyi da ita a kitchen din ta ce,