Sashe 68
Siradin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Babar Hajiya, wadda ta fara tsufa sosai amma yanayi irin na hutu da daular da take ciki ke son boye tsufan nata karfi da yaji, tana ta tsokanarsa yadda ta saba amma a yau bai iya ya tanka ba, taraddadin dake zuciyarsa kadai ya ishe shi. Ta dubi Hajiyar cike da alamar tambaya tace,
“Shin me ke damun Mai gidana ne, duk ya lalace haka? Ciwo ko matsala? Hajiya ta kyabe baki tace umh masa! Ni ma haka na gan shi, munafurcin su can da su da uban su zai cinye amma ba ni ba, na fi karfin kurwar su Intasar Allah! Tunda ku sun lashe ku, to ku je kuyi ta bin su na yafewa Saratu, sai ta je ta kara jika malaminta, na yarda ita na haifawa ku, na amince yayan tara da nayi nakudar ku na haife cikin wahala da kaka-ni-kayi, duka nata ne, ni kuma ina rokon Allah ya bani masu jin kaina.�
Ta soma sheshshekar kuka. Ya ji guiwoyinsa sunyi sanyi kalau, fiye da shigowarsa. Ya tabbata rashin nasara, ya tabbata garesa, Shi kadai yasan yadda kukanta ke girgiza zuciyarsa. Ya alkawartama ran sa idan ta hanashi zai hanu, shi kuma yayi jinyar zuciyarsa har sai ta mance da Intisar! Zai zabi Hajiyarsa akanta!! Zai zabi mahaifiyarsa akan soyayyarsa!!! Zai zabi farin-cikin Hajiya akan na shi, domin samun tsira a gidan duniya da tserewa daga azabar lahira. Duk da haka zai fadi, domin ta yanke masa hukunci.
Ya zamo daga cikin kujera yazo har inda take, cikin kaskantar da kai da tsananin girmamawa ya ce,
“Hajiyana, ba mayya bace Intisar, ki daina illata ta hakan nan, ki daina fadin muggan kalami akanta don Allah? In Iyayenta suka ji zasu yi kararki. A yanzu haka tana tare da Iyayenta bata gidan mu.
Na zo ne neman amincewar ki, kan abinda zuciyata ke so da albarkarki. Ina mai neman yardar ki kan son auren Intisar diyar Aunty Amarya, a sabili da azabar sonta da ke neman hallakani. Ki ceci rayuwata Hajiya, ki ji tausayina. Ki daina laakari da hujjojin ki marassa madafa.
Intisar ta ki ni, ta bujire wa ingantacciyar soyayyar da take mun saboda ke, saboda sanin halinki na rashin kyautayi da adalci a gareta. Ki taimake ni ki nuna masu ba haka bane, ke ma uwa ce mai tausayi da jin kai tamkar sauran iyaye, ke ma uwace da ta san ciwon dan ta, take kuma son duk abinda yake so.
Bijirewar ki na nufin alamura da dama cikin rayuwata. Ba na nufina in tursasa ki bisa raayina ba, Illa ki ji kai na ki tausaya mun., ki yi min alfarma cikin dimbin alfarmomin ki da basa karewa a gareni. To a yau ma ina neman alfarmar ki irin wadda ban taba nema ba! Ina kuma mai tabbatar maki zan yi biyayya ga duk hukuncin da ki ka yanke a gare ni.�
Ya sunkuyar da kai yana mai sauraron hukuncin nata.
A zaune take kurum tana mai sauraron kowacce kalma da kowanne harafi dake fita daga bakinsa, tana kuma auna ta a bisa maauni na hankali da tunaninta. Ta kasa gasgata me kunnuwanta suke jiyo mata, ta dauki alamarin cikin irin mafarke-mafarken da take a dan tsukin game da yayanta da Intisar.
Sun fi minti talatin shiru, babu wanda yayi koda kwakkwaran nunfashi balle hadiyar miyau. Sai a lokacinne wasu zafafan hawaye suke zubo mata, wadanda ita kadai ta san ko na menene, ita kadai ta san me take sakawa take kuma warwarewa a zuciyar nan tata. Bakin-ciki ne? Farin-ciki ne? Tausayi ne? Nadama ce? Ita kadai ta barma kan ta sani.
Hukunci na karshe data yanke shine mikewa ta bar masa falon, ba tare da ta ce da shi komi ba. Alameen ya ji hantar cikin sa ta kada, yayan hanjin sa sun dunkule waje daya. Ya yi nadamar furta kalaman sa ga mahaifiyar sa, data daukaka kaunarsa a zuciyarta fiye da ta kowa a duniya. Wadda burinta a kullum shine dawwamar su cikin gata da farin-ciki.
Amma a yau, sakamakon ta shine zabar wadanda ta ki jinni a duniya fiye da kowa a matsayin abinda yake so da kauna mai tsanani, yake burin ya zamo wani bangare koko ginshiki na rayuwarsa, kuma wai har yake gaya mata in har bata amince ba, zata yi asarar shi itama. Anya Hajiyar ta cancanci wadannan kalami?
A lokacin ya ji ya tsani kan sa, ya tsani komi dake cikin duniyar kuma ya tsani ita kanta Intisar. A ganin sa duk ita ta jawo masa, samun sabani da Hajiyar sa. Yayi nadamar dawowar sa Nigeria a yau. Inama bai biyewa Ihsan sun dawo ba! Inama. Inama Sai ya ji wasu dunkulallun hawaya sun kwararo bisa kundukukin sa.
Ya mike cikin yankewar buri da fidda rai da komi na rayuwar duniyar ya nufi dakin da Hajiyar ta shiga, yasa hannu ya murda kofar sai ya jita gam-gam da mukulli.
Ya juya ga kakar sa Haj Iyami, wadda ke zaune cikin kujera tana kallonsu kawai cikin rashin fahimtar abinda suke ciki. Ya zauna a gabanta ya kama kafafunta ya shiga rera mata kuka mai matukar motsa zuciya, yana magiyar ta nema masa gafarar Hajiya, in ba hakaba bai san yadda zai yi da rayuwar shi ba.
Ta kai hannunta kansa tana shafawa tace ya isa Maigida na, ko Nafi zata yi fushi da kowa a duniya bazata yi fushi da kai ba! Ta na sonka, son da kai din baka sani ba, na tabbata ba kai ka sata kuka ba, ita kadai tasan dalilin kukanta. Ka tashi ka tafi gida, dare yayi, gobe ka dawo lokacin ta nutsu sai mu zauna a yi maganar.
Ina! Alameen ya tabbatar mata bai zuwa ko nan da can batare da ya san hukuncin da Hajiyar ta yanke a kansa ba. Ta kada ta raya harta gaji tace tunda kwana zaka yi, to ga makullan sassan baki can bisa T.V ni zan je inyi sallah. To a lokacin ne shima kunnen sa ya jiyo mai kiraye-kirayen sallar maghriba da ake ta yi a masallatai, ya mike ye fita, a masallacin ya samu dabinon da yai buda baki, ya sami jami a masallacin cikin gidan, bai baro masallacin ba saida akayi sallar Isha’i tare da shi, ya sake mikewa ya bade shafa’i da wutri.
Ya dade cikin sujjadarsa, yana mai zubar da hawaye, cikin kai kukansa ga Allah subhana, mai juya alamura yadda yaso, yana mai rokon sa da ya fidda Intisar a zuciyarshi, tunda Hajiya bata son ta, ya karfafa masa raunanniyar zuciyarshi, ya bashi ikon yin biyayya ga mahaifiyar shi, ya karkato da kafaffiyar zuciyarta ta yafe mishi! Ta fahinci ba ya da nufin tozarta ta, kuma ba shi ya daurawa kansa kaunar Intisar ba.
Abu ne da shima yafi karfin sa, yafi karfin iyawar sa, yafi karfin duk wani kokari da zai yi ya fidda ta a ran shi!! Ya bashi hakuri da dangana, ya sa yafi karfin zuciyarsa, domin shi kansa ya san yana cikin sahun mutanen da basa iya controlling zuciyar su musamman akan abinda ta ke tsananin so.
Har zuwa sanda ya koma cikin gidan, Hajiya bata bude kofarta ba, abinciccikan da Kakarshi ta sa shi a gaba da su domin yayi buda baki, bai iya ya hadiyi ko loma daya ba. Ya kara ramewa, ya kara zabgewa, ya kara susucewa yini daya rak, fiye da yadda yazo garin.
Sai da Assalatu Hajiya ta fito domin gabatar da alwallar sallar asubahi, ta ji wani abu ya tokare mata kofa sai rabewa tayi ta fito. Ba komi bane illa kyawawan kafafun Alameen da ke kwance a bakin kofar ta barci na dibarsa kadan-kadan, har ranta ta ji matukar tausayin shi. Wai Aminunta ne wannan?
Mutum maabocin kuzari, fara, kwarjini, ilmi na kwatance da cikar zati ya koma haka, duk a dalihin soyayyar Intisar. Wasu hawayen takaici suka zubo mata. Ba shakkah, Intisar, mayya ce! Furucin da ta dade tana yi a kan ta yau taga tabbacin sa.
Ta saki kurwar Faisal da Daddy Makarfi yanzu kuma ta dawo ta Aminun ta? Bazata taba amincewa ba!! Za tayi fito-na-fito da yarinyar nan a karo na biyu har sai taga karshen ta. Za tayi mata mai gabadaya ita da Saratu in ba hakaba, ta tabbata watarana daga ita har yayanta zuwa abinda ta mallaka, ba zasu tsira daga maitar yarinyar ba.
Tasa kafarta ta zungureshi yayi saurin bude ido, tare da hamzarin gurfana a gabanta yace cikin dusashshiyar murya.
Hajiya na, kin yafe mani? Tace kai ba na son zancen banza, tashin ka nayi ka je ka yi Sallah. Duk fadin gidan nan ka rasa inda zaka kwanta sai bakin kofa ta, salon ka jawo min magana ko me? Ya mike sum-sum-sum ya na fita daga falon yana waiwayonta, ta yi tsaki a ranta tace Allah ya isa tsakani na da wannan tsintattar mage.
Sai a lokacin ta tuna abinda yace da ita, wai Intisar bata gidansu, tana tare da iyayenta. Tace ni zaa gayawa karyar banza ko ko ni zaayiwa dadin baki wai don in yarda, yarinyar da aka kawo min ita daga daji, tun tana tsumman goyonta, yanzu haka ma wasu mutane Saratun ta debo aka biyasu su ce su iyayen Intisar din ne, don ta yarda a kakabawa danta to bazata taba amincewa ba.
Kwanan Alameen biyu kenan yana bin mahaifiyarsa tare da neman gafararta a bisa bacin ran daya lura bukatar shi ya sanya ta, amma taki ce masa komi iyakaci in ya dameta ta tashi ta bar masa wajen.
A na ukun ne Haj. Iyami dattijiya mai tsananin hangen nesa, ta samu Hajiyar a daki rike da hannun Alameen da bakin ciki, nadama da tashin hankali ke neman zautawa, ta zaunar da shi a gefenta amma shi din sai ya zame daga bakin gadon ya zauna bisa carpet a gefen kafafunta kansa a sunkuye, hakannan hawayensa basu bar diga bisa tafin kafarta ba.
Ta yi kira da kakkausar murya irin yadda bata taba yi ba. Ta ce Nafisa! Ke kam wace irin uwa ce? Na dade ban ga uwa mara tausayi irin ki ba. Ba haka ni da ubanki mu kai miki ba, mu kullum masu tausayi da kyautayi ne a gareki, tare da kaunar duk abinda ki ke so!
“Shin me ke damun Mai gidana ne, duk ya lalace haka? Ciwo ko matsala? Hajiya ta kyabe baki tace umh masa! Ni ma haka na gan shi, munafurcin su can da su da uban su zai cinye amma ba ni ba, na fi karfin kurwar su Intasar Allah! Tunda ku sun lashe ku, to ku je kuyi ta bin su na yafewa Saratu, sai ta je ta kara jika malaminta, na yarda ita na haifawa ku, na amince yayan tara da nayi nakudar ku na haife cikin wahala da kaka-ni-kayi, duka nata ne, ni kuma ina rokon Allah ya bani masu jin kaina.�
Ta soma sheshshekar kuka. Ya ji guiwoyinsa sunyi sanyi kalau, fiye da shigowarsa. Ya tabbata rashin nasara, ya tabbata garesa, Shi kadai yasan yadda kukanta ke girgiza zuciyarsa. Ya alkawartama ran sa idan ta hanashi zai hanu, shi kuma yayi jinyar zuciyarsa har sai ta mance da Intisar! Zai zabi Hajiyarsa akanta!! Zai zabi mahaifiyarsa akan soyayyarsa!!! Zai zabi farin-cikin Hajiya akan na shi, domin samun tsira a gidan duniya da tserewa daga azabar lahira. Duk da haka zai fadi, domin ta yanke masa hukunci.
Ya zamo daga cikin kujera yazo har inda take, cikin kaskantar da kai da tsananin girmamawa ya ce,
“Hajiyana, ba mayya bace Intisar, ki daina illata ta hakan nan, ki daina fadin muggan kalami akanta don Allah? In Iyayenta suka ji zasu yi kararki. A yanzu haka tana tare da Iyayenta bata gidan mu.
Na zo ne neman amincewar ki, kan abinda zuciyata ke so da albarkarki. Ina mai neman yardar ki kan son auren Intisar diyar Aunty Amarya, a sabili da azabar sonta da ke neman hallakani. Ki ceci rayuwata Hajiya, ki ji tausayina. Ki daina laakari da hujjojin ki marassa madafa.
Intisar ta ki ni, ta bujire wa ingantacciyar soyayyar da take mun saboda ke, saboda sanin halinki na rashin kyautayi da adalci a gareta. Ki taimake ni ki nuna masu ba haka bane, ke ma uwa ce mai tausayi da jin kai tamkar sauran iyaye, ke ma uwace da ta san ciwon dan ta, take kuma son duk abinda yake so.
Bijirewar ki na nufin alamura da dama cikin rayuwata. Ba na nufina in tursasa ki bisa raayina ba, Illa ki ji kai na ki tausaya mun., ki yi min alfarma cikin dimbin alfarmomin ki da basa karewa a gareni. To a yau ma ina neman alfarmar ki irin wadda ban taba nema ba! Ina kuma mai tabbatar maki zan yi biyayya ga duk hukuncin da ki ka yanke a gare ni.�
Ya sunkuyar da kai yana mai sauraron hukuncin nata.
A zaune take kurum tana mai sauraron kowacce kalma da kowanne harafi dake fita daga bakinsa, tana kuma auna ta a bisa maauni na hankali da tunaninta. Ta kasa gasgata me kunnuwanta suke jiyo mata, ta dauki alamarin cikin irin mafarke-mafarken da take a dan tsukin game da yayanta da Intisar.
Sun fi minti talatin shiru, babu wanda yayi koda kwakkwaran nunfashi balle hadiyar miyau. Sai a lokacinne wasu zafafan hawaye suke zubo mata, wadanda ita kadai ta san ko na menene, ita kadai ta san me take sakawa take kuma warwarewa a zuciyar nan tata. Bakin-ciki ne? Farin-ciki ne? Tausayi ne? Nadama ce? Ita kadai ta barma kan ta sani.
Hukunci na karshe data yanke shine mikewa ta bar masa falon, ba tare da ta ce da shi komi ba. Alameen ya ji hantar cikin sa ta kada, yayan hanjin sa sun dunkule waje daya. Ya yi nadamar furta kalaman sa ga mahaifiyar sa, data daukaka kaunarsa a zuciyarta fiye da ta kowa a duniya. Wadda burinta a kullum shine dawwamar su cikin gata da farin-ciki.
Amma a yau, sakamakon ta shine zabar wadanda ta ki jinni a duniya fiye da kowa a matsayin abinda yake so da kauna mai tsanani, yake burin ya zamo wani bangare koko ginshiki na rayuwarsa, kuma wai har yake gaya mata in har bata amince ba, zata yi asarar shi itama. Anya Hajiyar ta cancanci wadannan kalami?
A lokacin ya ji ya tsani kan sa, ya tsani komi dake cikin duniyar kuma ya tsani ita kanta Intisar. A ganin sa duk ita ta jawo masa, samun sabani da Hajiyar sa. Yayi nadamar dawowar sa Nigeria a yau. Inama bai biyewa Ihsan sun dawo ba! Inama. Inama Sai ya ji wasu dunkulallun hawaya sun kwararo bisa kundukukin sa.
Ya mike cikin yankewar buri da fidda rai da komi na rayuwar duniyar ya nufi dakin da Hajiyar ta shiga, yasa hannu ya murda kofar sai ya jita gam-gam da mukulli.
Ya juya ga kakar sa Haj Iyami, wadda ke zaune cikin kujera tana kallonsu kawai cikin rashin fahimtar abinda suke ciki. Ya zauna a gabanta ya kama kafafunta ya shiga rera mata kuka mai matukar motsa zuciya, yana magiyar ta nema masa gafarar Hajiya, in ba hakaba bai san yadda zai yi da rayuwar shi ba.
Ta kai hannunta kansa tana shafawa tace ya isa Maigida na, ko Nafi zata yi fushi da kowa a duniya bazata yi fushi da kai ba! Ta na sonka, son da kai din baka sani ba, na tabbata ba kai ka sata kuka ba, ita kadai tasan dalilin kukanta. Ka tashi ka tafi gida, dare yayi, gobe ka dawo lokacin ta nutsu sai mu zauna a yi maganar.
Ina! Alameen ya tabbatar mata bai zuwa ko nan da can batare da ya san hukuncin da Hajiyar ta yanke a kansa ba. Ta kada ta raya harta gaji tace tunda kwana zaka yi, to ga makullan sassan baki can bisa T.V ni zan je inyi sallah. To a lokacin ne shima kunnen sa ya jiyo mai kiraye-kirayen sallar maghriba da ake ta yi a masallatai, ya mike ye fita, a masallacin ya samu dabinon da yai buda baki, ya sami jami a masallacin cikin gidan, bai baro masallacin ba saida akayi sallar Isha’i tare da shi, ya sake mikewa ya bade shafa’i da wutri.
Ya dade cikin sujjadarsa, yana mai zubar da hawaye, cikin kai kukansa ga Allah subhana, mai juya alamura yadda yaso, yana mai rokon sa da ya fidda Intisar a zuciyarshi, tunda Hajiya bata son ta, ya karfafa masa raunanniyar zuciyarshi, ya bashi ikon yin biyayya ga mahaifiyar shi, ya karkato da kafaffiyar zuciyarta ta yafe mishi! Ta fahinci ba ya da nufin tozarta ta, kuma ba shi ya daurawa kansa kaunar Intisar ba.
Abu ne da shima yafi karfin sa, yafi karfin iyawar sa, yafi karfin duk wani kokari da zai yi ya fidda ta a ran shi!! Ya bashi hakuri da dangana, ya sa yafi karfin zuciyarsa, domin shi kansa ya san yana cikin sahun mutanen da basa iya controlling zuciyar su musamman akan abinda ta ke tsananin so.
Har zuwa sanda ya koma cikin gidan, Hajiya bata bude kofarta ba, abinciccikan da Kakarshi ta sa shi a gaba da su domin yayi buda baki, bai iya ya hadiyi ko loma daya ba. Ya kara ramewa, ya kara zabgewa, ya kara susucewa yini daya rak, fiye da yadda yazo garin.
Sai da Assalatu Hajiya ta fito domin gabatar da alwallar sallar asubahi, ta ji wani abu ya tokare mata kofa sai rabewa tayi ta fito. Ba komi bane illa kyawawan kafafun Alameen da ke kwance a bakin kofar ta barci na dibarsa kadan-kadan, har ranta ta ji matukar tausayin shi. Wai Aminunta ne wannan?
Mutum maabocin kuzari, fara, kwarjini, ilmi na kwatance da cikar zati ya koma haka, duk a dalihin soyayyar Intisar. Wasu hawayen takaici suka zubo mata. Ba shakkah, Intisar, mayya ce! Furucin da ta dade tana yi a kan ta yau taga tabbacin sa.
Ta saki kurwar Faisal da Daddy Makarfi yanzu kuma ta dawo ta Aminun ta? Bazata taba amincewa ba!! Za tayi fito-na-fito da yarinyar nan a karo na biyu har sai taga karshen ta. Za tayi mata mai gabadaya ita da Saratu in ba hakaba, ta tabbata watarana daga ita har yayanta zuwa abinda ta mallaka, ba zasu tsira daga maitar yarinyar ba.
Tasa kafarta ta zungureshi yayi saurin bude ido, tare da hamzarin gurfana a gabanta yace cikin dusashshiyar murya.
Hajiya na, kin yafe mani? Tace kai ba na son zancen banza, tashin ka nayi ka je ka yi Sallah. Duk fadin gidan nan ka rasa inda zaka kwanta sai bakin kofa ta, salon ka jawo min magana ko me? Ya mike sum-sum-sum ya na fita daga falon yana waiwayonta, ta yi tsaki a ranta tace Allah ya isa tsakani na da wannan tsintattar mage.
Sai a lokacin ta tuna abinda yace da ita, wai Intisar bata gidansu, tana tare da iyayenta. Tace ni zaa gayawa karyar banza ko ko ni zaayiwa dadin baki wai don in yarda, yarinyar da aka kawo min ita daga daji, tun tana tsumman goyonta, yanzu haka ma wasu mutane Saratun ta debo aka biyasu su ce su iyayen Intisar din ne, don ta yarda a kakabawa danta to bazata taba amincewa ba.
Kwanan Alameen biyu kenan yana bin mahaifiyarsa tare da neman gafararta a bisa bacin ran daya lura bukatar shi ya sanya ta, amma taki ce masa komi iyakaci in ya dameta ta tashi ta bar masa wajen.
A na ukun ne Haj. Iyami dattijiya mai tsananin hangen nesa, ta samu Hajiyar a daki rike da hannun Alameen da bakin ciki, nadama da tashin hankali ke neman zautawa, ta zaunar da shi a gefenta amma shi din sai ya zame daga bakin gadon ya zauna bisa carpet a gefen kafafunta kansa a sunkuye, hakannan hawayensa basu bar diga bisa tafin kafarta ba.
Ta yi kira da kakkausar murya irin yadda bata taba yi ba. Ta ce Nafisa! Ke kam wace irin uwa ce? Na dade ban ga uwa mara tausayi irin ki ba. Ba haka ni da ubanki mu kai miki ba, mu kullum masu tausayi da kyautayi ne a gareki, tare da kaunar duk abinda ki ke so!