← Book details Shareef Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 50 OF 75

Sashe 50

Shareef Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Daga Aakifan har Yusaira suka sheƙe da dariya, dayake suna wuri ɗaya har da tafa wa,
Sai kuma suka haɗa kai suna ƙus-ƙus-ƙus

Sadiq yace, "to gulman ya isa haka a tashi mu tafi, wlh ga kiran Ammee nan ma ya shigo, ku shirya mu wuce."
Ya ƙare maganar yana daukar wayan

Umarni ta ba shi a kan, "yanzu su dawo gida zaman ya isa haka nan."

Dayake a handsfree ya saka wayan duk suna ji,
Dolen su suka tashi suka koma É—akin Maryamu suka hau kimtsa wa

Bayan sun gama Yusaira tace, "Ma'am, ai sai ki je ki É—auko mana Na'ilah a É—akin sa tunda zamu wuce."

Harara ta watsa musu tace, "Ai kuwa baku shirya tafiya ba kenan."

"To kina nufin mu zamu shiga mu É—auko ta?" A cewar Yusairan tana dalalo ido waje

Sai ta zauna a kan kujera tana mayar da É—ankwali goshi da faÉ—in, "ahaf; ai sai kuyi kuma."

Tsaki Sadiq ya ja yace, "kuna ɓata min lokaci don Allah."

Aakifah tace, "to ai kana jin mu da ita, mun ce ta kira mana Na'ilah ta ƙi, kuma ka ga ba yanda za a yi mu je da kanmu."

Wuce wa yayi zuwa ɗakin SHAREEF ɗin batare da ya ce musu komai ba, a bakin ƙofan ya tsaya yana nocking

"Amma wlh kin ji kunya Maryam, ki sauya hali, Mace da Mijinta but sai shegen girman kan tsiya, bari ki ji Allah irin su Yaya SHAREEF ba abun wasa bane kin samu kar ki bari damar ki ta kufce, ki lallaɓa sa ki samu zuciyarsa tun kafin lokaci ya ƙure miki."
A cewar Aakifah ƙasa-ƙasa take maganar kar Sadiq ya jiyo su

Maryamu zata yi magana suka haɗa ido da SHAREEF da ya fito daga ɗakin tare da Na'ilah, ɗauke kanta tayi tana sake turo ɗankwali gaban goshi, ta miƙe tana cewa, "ku mu je in taka muku har bakin motan."

Suma basu ce komai ba tunda suna ganin SHAREEF É—in,
Don tahowa yayi zai zauna a kan kujerar,
Sai da suka yi masa sallama sannan suka bar falon

Har bakin mota ta raka su, sai da ta ga sun shiga sannan ta mammaka musu duka tace, "tukuicin abun da ku ka yi min kenan, sai mun yi waya zan sake rama wa, don tsab nake da amsar maganar ku."
Tana É—aga musu hannu take ta dariya sabida ganin yanda suka sauya fuska sun ji dukan da tayi musu,
"Ku gaishe min da su Ammee."

Banza suka yi da ita har Sadiq ya ja motan zuwa bakin gate,
Dayake ba a rigada an saka Mai gadi ba, dole shi ya fito ya bude ya fitar da motan, sannan ya zo ya rufe musu ƙofan

Maryamu tana tsaye a wurin har lokacin; take mishi magana,
"yaya Sadiq wai yaushe zaka koma ne?"

Bai rigada ya fita ba sai yace mata, "zuwa jibi insha Allahu."

"To Allah ya kaimu, don Allah ka sake zuwa kafin ka tafi."

"No ba lokaci Maryam, na tafi."
Ya ɗaga mata hannu ya rufe ƙofan

Juya wa tayi ta shiga cikin gidan

SHAREEF na zaune duk yana jin maganar da suka gama yi da Sadiq ɗin, dayake ƙofan falon a bude ne yana jiyo muryoyin su

Tana shigowa suka haÉ—a idanu, sai da ta watsa mishi harara before ta É—auke kanta ta nufi wurin kujeran, kayanta da ke wurin har yanzu ta kwashe ta nufi cikin É—akin ta

Yayinda SHAREEF yana kallonta but ya gaza yin mata magana, wani irin shakkarta ne ya kama sa, sai dai ido da ya zuba mata yana haɗiyar yawu kamar wani maye, lallai ɗan hakin da ka raina... A yau ga shi wacce ya raina ta ƙere wa sa'ar sa,
Yana son ya bi ta yayi mata magana, amma kallon da take watsa mishi shi ne dalilin da yasa ya ji shakka ya kasa buɗe bakin sa, yana kallo ta shige ɗaki yana ji tamkar ya miƙe ya bi ta,
Amma haka nan ya zauna a wurin yana jiran ko zata fito, sai kallon wurin yake yi

Yayinda Maryamu kuma tana shiga ɗaki wayanta ta soma ƙara, wurin gadonta ta nufa tunda a kai ta ajiye, ta zauna a kan gadon tana duba wayan,
Ganin sunan Innar su sai tayi saurin É—auka tana kwaÉ—a mata kira cikin farin ciki

"Hmm sallaman kenan kiran suna na wato? Ke dai baza ki taɓa sauya wa ba ko?"

Tura baki tayi da cewan, "kai Inna, koyaushe baza mu riƙa maganar arziki ba sai kin min faɗa?"

"Au iyee! Ni kike fada wa haka Maryamu?"

"Sorry Inna, wlh suɓul da baka ne."

Ƙwafa Inna tayi tana cewa, "za ki ci ubanki ne tunda ba ki da kunya, dama mai zai sa in kira ki in ba da dalili ba?"

Kamar zata yi kuka tace, "ki yi haƙuri don Allah, wlh na sauya ba kamar yadda kika sanni bane a baya, nayi hankali."

"Ni ba wannan yasa na kira ki ba, jiya da muka koma gida da dare Matar Yayanku Naziru ta haihu, na kira wayan Hajiya Khadijah ba ya shiga, idan kin same ta ki sanar mata."

Farin ciki ne ya cika Maryamu, cikin murna tace, "wayyo Inna, ashe ina nan zuwa nan kusa?"

"Kina nan zuwa nan kusan ƙaniyar ki, ke fa ba ki da hankali wlh, ki sanar mata da saƙon saura ki ce kin manta, na faɗa ne kawai don su sani ba wai zuwa zasu yi ba; bare ke ƴar kaɗan kaɗa miya, sha-sha-sha, kuma wlh idan ba ki natsu kin yi abun da yakai ki ba ke da mai sama, don aure ba abun wasa bane."

Turɓune fuska tayi tace, "Inna meye kuma na min baki? Haba don Allah."

"Ba baki nayi miki ba Maryamu, na san ba ki da hankali tunda har kika iya furta min maganganun nan a kan ba kya son auren nan, na san za ki iya yin komai, aure dai ibadan Allah ne, duk abun da kika yi walau mai kyau ko mara kyau akwai lada da zunubin da ake rubuta miki, shiyasa nace miki ke da Allan ki tunda yana kallon ki, gidan aure ba gidan wasa bane hanyar neman aljannar ki ne, duk abun da za ki yi kina tunanin babu komai to ana nan ana rubuta miki sakamakon shi, kuma za ki girbe abun da kika shuka, ki natsu Maryamu ki yi biyayya ga Mijinki, abun da yake so ki yi masa in har bai saɓa hanya ba, ban da rashin kunya wlh ki kiyaye kanki na faɗa miki, ke kaɗai kika samu wannan gatan duk a wannan gidan namu, kowa sai maganar ki yake yi, idan kika ce za ki yi wasa da damar ki za ki yi dana-sani a nan gaba Maryamu, mutanen nan sun ɗauki ragamar komai a kanki sun mayar da ke tamkar ƴarsu, duk abun da Yaya Ahmad zai yi wa ɗansa na cikin sa yayi miki domin gata, ki saka musu wurin yin biyayya ga ɗansu, kar in ji kar in gani Maryamu, na ja miki kunne kar in ji kar in gani.
Ki gaishe da mai gidan, Umman Shatima ma tana gaishe ki."
Daga haka ta kashe wayarta

Tabar Maryamu da waya a hannu tana kallo kamar zata fashe da kuka, ba ƙaramin sanyi jikinta yayi ba, hakan ne yasa ta kwanta tayi shiru tana faman tunani,
Daga baya sai ta miƙe zaune ta kira Momy domin sanar mata da haihuwar

Sun jima suna waya da ita, har da Ammee duk sun gaisa suna ta mata nasiha suna ƙara wayar mata da kai a kan zamantakewar aure

Bayan sun gama wayan ne ta miƙe ta fita,
A lokacin babu SHAREEF a falon, kai tsaye kitchen ta nufa ta soma ƙoƙarin ɗaura girkin dare, duk da a lokacin kusan shida saura ne, kuma abincin da suka yi ɗazu babu yawa duk sun cinye,
Dalilin da yasa take son girka wa kenan, maganganun Inna ne yasa ta É—aura sanwan abincin su biyu

Bare dama Momy ta sake jan kunnenta a kan girkin, "kar ta sake ta riƙa ɗaura abinci babu Mijinta, komai ta girka tayi da nasa."

Tana aikin tana mita a yanzu, "ai wlh koda na É—aura abincin nan ajiye wa zan dinga yi, idan bazai ci ba yabar sa in har Ni zan ce mishi ya ci, wlh sai na rama abin da yayi min don bazan yarda ba, dole ya san daraja na, Ni fa haushin sa nake ji, Ni fa na tsane shi wlh."

"Kin tsane Ni ko?"
SHAREEF yayi furucin da ke tsaye a bakin ƙofa tun soma maganar nata.
[28/04, 8:50 AM] نفيسة OumƊahira: 🌱🌱🌱🌱🌱

       *SHAREEF*
           _SexyBoy_
🌱🌱🌱🌱🌱

_Writer: Nafisat Isma'il Lawal_
_Wattpad: UmmuDahirah_

*Littafina na kuÉ—i ne, ki biya ki karanta, zaku iya samu na a kan wannan numban wayan. 07065334256.*

__________
*BOOK2*
_______________*PAGE26*
_____Da sauri ta juya tana kallon shi, ko kusa bata san da zuwan shi wurin ba sai tsinkayan muryansa tayi, tsuke fuska tayi ganin yanda shima ya haÉ—e ran yana kallonta,
Sai ta juyar da kai ta ci gaba da abun da take yi

Tahowa yayi inda take, ya tsaya dai-dai bayanta kamar zai haÉ—e da ita

Hucin numfashinsa ne ya sake ankarar da ita, ta juya da sauri tana bin sa da kallo, ganin shi gab da ita sai tayi saurin ja da baya tana haÉ—e wa da kantan kitchen É—in, duk da haka babu tazara a tsakanin su, yatsina fuska tayi tana faÉ—in, "wai meye haka; ka zo ka tsaya min a nan kamar zaka faÉ—o jikina?"

"So nake yi na faÉ—o ai, faÉ—a min waye kika tsana?"

Ido cikin ido take kallonsa, batare da tsoro ko shakkarsa ba tace, "kai na tsana." Ta sake ƙwalalo masa ido, "na tsane ka nace, mugu azzalumi..."

Saurin rufe mata bakin yayi da hannunsa É—aya, "kar ki sake kira na da azzalumi."

Ƙoƙarin cizon hannun take yi, sai yayi saurin cire hannunsa tun kafin ta kama mishi fata

A fusace tace, "idan kuma na ƙi fa?"

Tsira mata ido yayi, in cool voice yace, "zan yi haƙuri."
Chapter 50 · 0% Book details