Sashe 81
Ni Zan Ladabi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A hankali ya saka hannunsa yana janye nata yana dagowa ya kalleta, sam hankalinsa ya tafi a wajen kallo bai ji shigowarta ba, koda yake bai kai ga rufe kofar ba ya zauna kallon
Shigar dake jikinta da ita da babu du daya, haka kuma dai ya ga after drss dinta baka ajiye saman hannun kujera
Kansa ya dan dauke yana sake maidawa saman TV ya ce" Baki kwonta ba?"
Risala ta yi farrr da idannuwanta tana zagayowa ta zauna daf da shi tana kallonsa ta ce" Ban kwonta ba, na kasa barcin, so nake na yi a nan"
Abinda yake yi ya dakatar dan kirjinsa take nunawa kuma tana son kwontawa a kai, ita fa a yanzu ba zaku gane bane, dwara da bata samu cikin ba, dan ta kula zumudin cikin kadai mijinsu ke yi, bai damu da mai dauke da cikin ba!, Dan haka gwara da aka yi haka ai
A hankali ya janye hannayenta yana kallonta ya ce" Kin san ai bama haka"
Risala ta turo baki tana cewa" Me yasa kake hannani rabarka a ranar da ita din bata gefenka?, Tunda ba zuwa take yi ta kwana ba ni na zo ai sai ka bani kulawa ko?"
"Ranakun da suke naki zan iya baki kulawa, wanda suke na yar uwarki baki da wannan damar, mu kiyaye kar ki shiga abinda kuma bai shafe ki ba" ya fada a tausashe yana sake dan matsawa kadan, domin du abinnan a idannuwan Uman biyu suke shigagu dadadu , koda ta nace ta kwana a bangarensa idan ranar ba tata bace ko daki basa hadawa, ya gwamace ya shige ya rufe ya kwonta idan ya je ya bi dare ya gano Uman biyu da cikinsa, da kuma twins ya masu addu'a
A hankali ta kawar da kanta gefe ranta na kuna, wannan jaraba da me ta yi kama ne? Bata san me yasa ABDUL ke yi mata haka ba, duda ita dadinta ne babu wanda ya san ainahin abinda yake faruwa a dakansa daga ita sai shi , sai mahalicinsu, ama idan yana mata haka sai ta ringa tunanin ba zai taba zubar da matar cen kwata kwata ba!,
A hankali ta ce" Dama zuwa na yi dan na yi godiya, kuma sai na kasa barci, shine zaka ki ko rabarka na yi ko?"
ABDUL ya yi shiru yana kallon TV din bai ce mata komai ba, dan ya gama magana ai da ita kuma
A hankali Amina ke sake rike kofar shigar zuciyarta na dokawa
Wayar da suka yi da dan gidan uncle dinsu, watau yayan mahaifinsu ya rikitata, bata san a inda ya samu numberta ba, batama san gaskiya ya fada ko karya ba, bata taba sannin idan ta ji dangin nata a wani hali zata girgiza haka ba, tunda ya fada mata maganar mutuwar zuciyarta ke bugawa da karfi, abin cikinta kuwa wani irin juyawa da ya yi ta tabata daga sama yanzu kasa yake kallo ko menene, uwa uba ciwon dake tashin mata wanda ta tabata na tsoratar da ta yi ne ya sakata haka
Ta rasa wa zata nufa da maganar, dole abin ya rikitata, gashi Fido na wajen lesson dinta, Biyu ne kawai a zaune da kayansu na masalaci sunna kallo
Sai da ya lafa mata sannan ta murda ta shiga zuciyarta na daf da tsintsinkewa
Wanda zata yiwa kuka ta ji sanyi sannan ya rakata take nema ido rufe
Da wani irin sauri Risala ta shige jikinsa lokaci daya ta nemi lalubar bakinsa a lokacin da su dukansu suka yi arba da Aminar da kana ganninta zaka fahimci hankalin ta ba a kwonce yake ba
A hankali ta sake dafe cikinta, sannan ta juya a hankali ba tare da ta furta koda A ba
Da karfi ya matsar da Risala gefe tamkar wata yar jaririya dan irin kautar da itan da ya yi da mamakinta yana mata wani kallon da ya tsoratata ya mike da dan sauri yana fadin" Aunty?"
Amina ta dan ja wani tukukin bakin ciki ya murdo ya sake murda mata cikinta
Da karfi ta duke dan har wani irin abu ta ji kamar yana bin kafarta ta rintse ido sosai tana ambaton Allah a zuciyarta
Dukowa ya yi hankalinsa tashe ya kamata yana dagota hadi da fadin" Aunty, menene? Bakida lafiya ne? Me yake damunki plz?"
Hannunta cikin nasa yake, a damke take da hannun nasa dan abinda ke mata zabtu zab zab zab kamar zai summar da ita
Gaba dayansa ya zauna a wajen yana kokarin rungumota jikinsa,
Sai da ya rungumeta sosai yana shafa bayanta a hankali a hankali yana duban wajen da Risala ya ce" Ki dauko min wayata mana "
Rai bace ta mike ta nufi ciki, ya sake rungumo Amina a jikinsa daidai ciwon ya lafa mata ta samu a hankali ta ringa janye jikinta har ta raba jikinta da nasa tana rintse idannuwanta
Cike da damuwa ya ce" Aunty?"
Amina ta bude idannuwanta ta sake zuba masa su, wannan wani irin wulakanci ne marar misali ne a rayuwa? Me ta yiwa wannan mutumen ne? Ai dole ya kireta aunty mana, tunda ya hadata da kayan nauyi ya zo yana kwakular yar yarinya
Hannunsa ya kai zai tabata, a hankali ta janye nata hannayen muryarta na rawa tana kallonsa ta ce" ABDUL, kar ka taba ni dan Allah, cin kashin ya isa hakanan, sannan ka sawake min, wanda na gani ya wadatar!"
Kirjinsa sai da ya mugun doka masa, yana kallonta da kallo mai dauke da mamakinta n kafiyarta da kuma mamakin kennan ba zata taba sonsa ba? Ya ce" Me yasa kika kasance mai furtawa miji ya sakeki bayan ba kyau? Babu kyau mace ta nemi saki a wajen mijinta haka kawai ba laifin da na maki?"
"Kake kiran ba laifin da ka yi min?, ABDUL babu laifin da ka yi min?, ABDUL tunda na dauki cikin nan ka yi watsi da ni, da ni da banza duka daya a wajenka, babu ruwanka yaya na kwana, ko yaya na tashi? Babu ruwanka da komai nawa, baka zuwa ind.................................................................." Idannuwanta ta rintse wani ciwon na sake murda mata
Cikin ciwon ta dake ture shi da dan karfi ta ce" Ka daina tabani nace, idan takamarka ni hadaka aka yi da ni, ka sani nima hakan take! Hadani aka yida kai, bayanshi ba wani abin!, Ka salameni na je na karasa haka, ya isheni haka!"
A sanyaye , jikinsa da zuciyarsa na tsintsinkewa ya sake tareta a hankali ya ce" Ki yi a hankali Plz, ki yi a hankali, ki tashi na kirawo docter dinki ta duba min ke, tun yaushe kike jin ciwo ne? Amina dan Allah ki bar rigimar nan haka kin ji?"
Fashewa ta yi da kuka tana sake tureshi ta ciciba a hankali ta mike daidai Risala ta fito da wayar tana kallonsa ido cikin ido ta ce" Ka bani waje na wuce, ka sani ko kaine autan maza kafata ba zata kuma takowa nan ba!, Idan kana so ka mayar da ita cikinka dan so, hakina da kuke shiga ku je ku kuka sani!"
Gaba daya ta rikice ta rikitashi ta hannashi rabarta ta kuma ki saurarawa
Wayar ya fizga a hannun Risala ya wuce ciki yana lalubar jalabiyarsa dan ya bita bangarensa, gaba daya hankalinsa a kololuwar tashe
Ya dan jima ciki dan bai iya rudewa ba a rayuwa, da kyar ya samo rigar da ya saka ya fito
Abinda ya sake bashi haushi da Risala, tan tsaye hannayenta harde sai jikiga take yi
Kallonta ya yi ya ce" Baki bita ba?"
Risala ta wani kalle shi ta ce"ina zan bita ni kums?"
ABDUL ya yi wani irin kwafa ya fice da sauri bai ce mata komai ba
Dorect bangeren Aminar ya karasa
Yana zuwa ya tambayi ko tana dakinta? Domin dawowar su Fido kennan , ita da Biyu sunna zaune
Yannayinsa ya shedawa firdausi ba lafiya ba, mikewa ta yi ta shige dakin Amina, sai dai ta tarar kayan aminar a watse a kasa, kamar wani abu ta dauka, ko wani ya daukar mata
Hankalinta ta ji yana neman tashi ta fito da sauri ta yi kicin,
Cenma bata sameta ba, ta dawo tana fada masa bata ganta ba, kuma ga yadda ta samu kayanta
A tsayen da yake sai da ya ji kamar za'a maka shi da kasa dan wani irin juuuuuuuuuuuuuuuuuuuuu da ya ji kansa ya kwasa
Labulen dakin ya sake rikewa da dan karfi idannuwansa rintse har ya ji numfashinsa na dawowa a hankali sannan ya fita
Wasa wasa nan da nan aka tada hankalin du wani wanda ya kwana ya tashi a gidan nan ana neman UMAN biyu
Abinda ya fi komai dagawa wa'inda ke tsaron kofar gidan hankali shine, sun raja'a , a kallon ball din da ake ce ta chealsy da baban club din da suke support , ya zamto kowa hankalinsa ya dauku wajen ihun ball din da aka saka wace ta shiga a ba zata, babu wanda ya san idan ta fita ko tana cikin gidan......nan fa suka rarabu, suka haukace kowa ya kama hanyar da zai nemeta a cikin gidan, wanda ABDUL bai taba dana sannin yin ginni mai girma ba sai yau a rayuwa
Dare kara yi yake ama basu ganta ba
A hankali ya karasa wajen mota ya bude ya shiga yana danna kiran Muhammat
Muhammat ya karaso da sauri yana amsa shi
Ky din mota ya tambaya yana duban sitiyarin motar
Muhammat ya ce" Sir koma gefen cen na tuka ka"
A hankali ya girgiza kansa yana kallonsa ya ce" Ka bani ky plz"
Miko masa ky din ya yi sabban ya je da sauri ya shiga wata motar ya tayar ya dakata yana kallonsa har ya tada ya fita a gidan
Biye yake da shi a hankali har suka karaso kan kwanar da zata idasa shi gidan Baba mai shanu, yana ta dube duben hanya domin ya tabata idan ta fito daga gida ba zata tarbi kowa da bacin ranta ba sai wanda zai saurareta
Ido Muhammat ya zarro lokaci daya yana taka wani wawan birki sakamakon wani mai baban babur da ya shawo kwana a guje ya maku jikin barin da ABDUL din ke tuki, watau bangaren da yake zaune yana tuki
Shigar dake jikinta da ita da babu du daya, haka kuma dai ya ga after drss dinta baka ajiye saman hannun kujera
Kansa ya dan dauke yana sake maidawa saman TV ya ce" Baki kwonta ba?"
Risala ta yi farrr da idannuwanta tana zagayowa ta zauna daf da shi tana kallonsa ta ce" Ban kwonta ba, na kasa barcin, so nake na yi a nan"
Abinda yake yi ya dakatar dan kirjinsa take nunawa kuma tana son kwontawa a kai, ita fa a yanzu ba zaku gane bane, dwara da bata samu cikin ba, dan ta kula zumudin cikin kadai mijinsu ke yi, bai damu da mai dauke da cikin ba!, Dan haka gwara da aka yi haka ai
A hankali ya janye hannayenta yana kallonta ya ce" Kin san ai bama haka"
Risala ta turo baki tana cewa" Me yasa kake hannani rabarka a ranar da ita din bata gefenka?, Tunda ba zuwa take yi ta kwana ba ni na zo ai sai ka bani kulawa ko?"
"Ranakun da suke naki zan iya baki kulawa, wanda suke na yar uwarki baki da wannan damar, mu kiyaye kar ki shiga abinda kuma bai shafe ki ba" ya fada a tausashe yana sake dan matsawa kadan, domin du abinnan a idannuwan Uman biyu suke shigagu dadadu , koda ta nace ta kwana a bangarensa idan ranar ba tata bace ko daki basa hadawa, ya gwamace ya shige ya rufe ya kwonta idan ya je ya bi dare ya gano Uman biyu da cikinsa, da kuma twins ya masu addu'a
A hankali ta kawar da kanta gefe ranta na kuna, wannan jaraba da me ta yi kama ne? Bata san me yasa ABDUL ke yi mata haka ba, duda ita dadinta ne babu wanda ya san ainahin abinda yake faruwa a dakansa daga ita sai shi , sai mahalicinsu, ama idan yana mata haka sai ta ringa tunanin ba zai taba zubar da matar cen kwata kwata ba!,
A hankali ta ce" Dama zuwa na yi dan na yi godiya, kuma sai na kasa barci, shine zaka ki ko rabarka na yi ko?"
ABDUL ya yi shiru yana kallon TV din bai ce mata komai ba, dan ya gama magana ai da ita kuma
A hankali Amina ke sake rike kofar shigar zuciyarta na dokawa
Wayar da suka yi da dan gidan uncle dinsu, watau yayan mahaifinsu ya rikitata, bata san a inda ya samu numberta ba, batama san gaskiya ya fada ko karya ba, bata taba sannin idan ta ji dangin nata a wani hali zata girgiza haka ba, tunda ya fada mata maganar mutuwar zuciyarta ke bugawa da karfi, abin cikinta kuwa wani irin juyawa da ya yi ta tabata daga sama yanzu kasa yake kallo ko menene, uwa uba ciwon dake tashin mata wanda ta tabata na tsoratar da ta yi ne ya sakata haka
Ta rasa wa zata nufa da maganar, dole abin ya rikitata, gashi Fido na wajen lesson dinta, Biyu ne kawai a zaune da kayansu na masalaci sunna kallo
Sai da ya lafa mata sannan ta murda ta shiga zuciyarta na daf da tsintsinkewa
Wanda zata yiwa kuka ta ji sanyi sannan ya rakata take nema ido rufe
Da wani irin sauri Risala ta shige jikinsa lokaci daya ta nemi lalubar bakinsa a lokacin da su dukansu suka yi arba da Aminar da kana ganninta zaka fahimci hankalin ta ba a kwonce yake ba
A hankali ta sake dafe cikinta, sannan ta juya a hankali ba tare da ta furta koda A ba
Da karfi ya matsar da Risala gefe tamkar wata yar jaririya dan irin kautar da itan da ya yi da mamakinta yana mata wani kallon da ya tsoratata ya mike da dan sauri yana fadin" Aunty?"
Amina ta dan ja wani tukukin bakin ciki ya murdo ya sake murda mata cikinta
Da karfi ta duke dan har wani irin abu ta ji kamar yana bin kafarta ta rintse ido sosai tana ambaton Allah a zuciyarta
Dukowa ya yi hankalinsa tashe ya kamata yana dagota hadi da fadin" Aunty, menene? Bakida lafiya ne? Me yake damunki plz?"
Hannunta cikin nasa yake, a damke take da hannun nasa dan abinda ke mata zabtu zab zab zab kamar zai summar da ita
Gaba dayansa ya zauna a wajen yana kokarin rungumota jikinsa,
Sai da ya rungumeta sosai yana shafa bayanta a hankali a hankali yana duban wajen da Risala ya ce" Ki dauko min wayata mana "
Rai bace ta mike ta nufi ciki, ya sake rungumo Amina a jikinsa daidai ciwon ya lafa mata ta samu a hankali ta ringa janye jikinta har ta raba jikinta da nasa tana rintse idannuwanta
Cike da damuwa ya ce" Aunty?"
Amina ta bude idannuwanta ta sake zuba masa su, wannan wani irin wulakanci ne marar misali ne a rayuwa? Me ta yiwa wannan mutumen ne? Ai dole ya kireta aunty mana, tunda ya hadata da kayan nauyi ya zo yana kwakular yar yarinya
Hannunsa ya kai zai tabata, a hankali ta janye nata hannayen muryarta na rawa tana kallonsa ta ce" ABDUL, kar ka taba ni dan Allah, cin kashin ya isa hakanan, sannan ka sawake min, wanda na gani ya wadatar!"
Kirjinsa sai da ya mugun doka masa, yana kallonta da kallo mai dauke da mamakinta n kafiyarta da kuma mamakin kennan ba zata taba sonsa ba? Ya ce" Me yasa kika kasance mai furtawa miji ya sakeki bayan ba kyau? Babu kyau mace ta nemi saki a wajen mijinta haka kawai ba laifin da na maki?"
"Kake kiran ba laifin da ka yi min?, ABDUL babu laifin da ka yi min?, ABDUL tunda na dauki cikin nan ka yi watsi da ni, da ni da banza duka daya a wajenka, babu ruwanka yaya na kwana, ko yaya na tashi? Babu ruwanka da komai nawa, baka zuwa ind.................................................................." Idannuwanta ta rintse wani ciwon na sake murda mata
Cikin ciwon ta dake ture shi da dan karfi ta ce" Ka daina tabani nace, idan takamarka ni hadaka aka yi da ni, ka sani nima hakan take! Hadani aka yida kai, bayanshi ba wani abin!, Ka salameni na je na karasa haka, ya isheni haka!"
A sanyaye , jikinsa da zuciyarsa na tsintsinkewa ya sake tareta a hankali ya ce" Ki yi a hankali Plz, ki yi a hankali, ki tashi na kirawo docter dinki ta duba min ke, tun yaushe kike jin ciwo ne? Amina dan Allah ki bar rigimar nan haka kin ji?"
Fashewa ta yi da kuka tana sake tureshi ta ciciba a hankali ta mike daidai Risala ta fito da wayar tana kallonsa ido cikin ido ta ce" Ka bani waje na wuce, ka sani ko kaine autan maza kafata ba zata kuma takowa nan ba!, Idan kana so ka mayar da ita cikinka dan so, hakina da kuke shiga ku je ku kuka sani!"
Gaba daya ta rikice ta rikitashi ta hannashi rabarta ta kuma ki saurarawa
Wayar ya fizga a hannun Risala ya wuce ciki yana lalubar jalabiyarsa dan ya bita bangarensa, gaba daya hankalinsa a kololuwar tashe
Ya dan jima ciki dan bai iya rudewa ba a rayuwa, da kyar ya samo rigar da ya saka ya fito
Abinda ya sake bashi haushi da Risala, tan tsaye hannayenta harde sai jikiga take yi
Kallonta ya yi ya ce" Baki bita ba?"
Risala ta wani kalle shi ta ce"ina zan bita ni kums?"
ABDUL ya yi wani irin kwafa ya fice da sauri bai ce mata komai ba
Dorect bangeren Aminar ya karasa
Yana zuwa ya tambayi ko tana dakinta? Domin dawowar su Fido kennan , ita da Biyu sunna zaune
Yannayinsa ya shedawa firdausi ba lafiya ba, mikewa ta yi ta shige dakin Amina, sai dai ta tarar kayan aminar a watse a kasa, kamar wani abu ta dauka, ko wani ya daukar mata
Hankalinta ta ji yana neman tashi ta fito da sauri ta yi kicin,
Cenma bata sameta ba, ta dawo tana fada masa bata ganta ba, kuma ga yadda ta samu kayanta
A tsayen da yake sai da ya ji kamar za'a maka shi da kasa dan wani irin juuuuuuuuuuuuuuuuuuuuu da ya ji kansa ya kwasa
Labulen dakin ya sake rikewa da dan karfi idannuwansa rintse har ya ji numfashinsa na dawowa a hankali sannan ya fita
Wasa wasa nan da nan aka tada hankalin du wani wanda ya kwana ya tashi a gidan nan ana neman UMAN biyu
Abinda ya fi komai dagawa wa'inda ke tsaron kofar gidan hankali shine, sun raja'a , a kallon ball din da ake ce ta chealsy da baban club din da suke support , ya zamto kowa hankalinsa ya dauku wajen ihun ball din da aka saka wace ta shiga a ba zata, babu wanda ya san idan ta fita ko tana cikin gidan......nan fa suka rarabu, suka haukace kowa ya kama hanyar da zai nemeta a cikin gidan, wanda ABDUL bai taba dana sannin yin ginni mai girma ba sai yau a rayuwa
Dare kara yi yake ama basu ganta ba
A hankali ya karasa wajen mota ya bude ya shiga yana danna kiran Muhammat
Muhammat ya karaso da sauri yana amsa shi
Ky din mota ya tambaya yana duban sitiyarin motar
Muhammat ya ce" Sir koma gefen cen na tuka ka"
A hankali ya girgiza kansa yana kallonsa ya ce" Ka bani ky plz"
Miko masa ky din ya yi sabban ya je da sauri ya shiga wata motar ya tayar ya dakata yana kallonsa har ya tada ya fita a gidan
Biye yake da shi a hankali har suka karaso kan kwanar da zata idasa shi gidan Baba mai shanu, yana ta dube duben hanya domin ya tabata idan ta fito daga gida ba zata tarbi kowa da bacin ranta ba sai wanda zai saurareta
Ido Muhammat ya zarro lokaci daya yana taka wani wawan birki sakamakon wani mai baban babur da ya shawo kwana a guje ya maku jikin barin da ABDUL din ke tuki, watau bangaren da yake zaune yana tuki