Sashe 77
Ni Zan Ladabi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hajia ta gyada kanta tana sake sauke wani numfashin ta ce" Yanzu ace da furfurata, na wulakanta kaina har yarinyar bayana tana irin haka da ni? Gaba daya na manta darajata ta shekarun da Allah ya bani, na manta mutuncina , da girman darajar da Allah ya luluba min,na wulakanta marainiyar Allah,na wulakantata bata taka min ba, bata kashe min ba, du a kan son kai, gashi yanzu an zageni ko budar baki na kasa yi dan gaskiya aka fada min, a kan son kaina da rufewar idannuwana................"
Abdul ya sake fuskantarta bai ce komai ba yana kallonta
Hajia ta sake girgiza kanta ta ce" baka sani ba fa, ita fa siyarma du haka take, ka ga zamu hadu da yayan cikinmu, wasu mun yi jikoki da su mu yi ta abubuwa kamar ba zamu mutu ba, a yi ta iface iface da manyan da kananan, mu yi ta tsare tsaren yadda zamu samu mu ci kudade ko na waye, mu yi ta shiga hakin junna, uwa uba ABDUL RA'UF kulun bama koshi da abinda muke samu, kulun burinmi mu samu sama da abinda muka samu, ba ruwanmu da wa zai ritsa ko wa zai jigata, idan dai kawunnanmu suka wucewa jifa to ya fada kan kowama......, Abdul bama kaunar a rabamu da talaka, ba ruwanmu da talaka, mun manta mu menene tushenmu, da yawanmu sun rasa aurensu a haka, wasu a cikin haka sun rasu, wasu sun dimiya basa tuna komai irin Allah ya kyalesun nan..... Abdul yau nice na jawa kaina wulakanci irin haka? Wai a kan dan cikinka ake gannin bak dace na taba ba dan kawai na nunawa yarinya tsana? Bata min komai ba dan kawai bata kwaliya irin ta yan matan zamani, bata gwali da abubuwan yan matan zamani shikenan ni ga kakar Gwamna dole gwamna ya auro matar gwamna ko? A haka idona ya rufe na dauko yar mararsa kunya na hada a cikin ahalina, idan da haihuwa itama ta haifo ta kuma bada tarbiya irin wace ta damu a gidansu.........."
A hankali ya kama hannunta yana murzawa
A tausashe ya ce" Hajia ya isa haka kin ji? Ki kwontar da hankalinki, abinda ya faru ki kadara wani mataki ne na samun cenji a rayuwarki, ke mutun ce, baiwa ce ke, ba zai taba yiwuwa ki rayu ba laifi a rayuwa, baban laifi shine na daukan alhakin bawa, Allah baya yafe wannan, ki yi kokari ki gyara mu'amalarki da kowa, ki kokarta ki daidaita mu'amalarki da jama'a, ba wai Mom twins kadai ba, kowama, bama kamar Alkali, a kusa kusa ban ga namiji mai hakuri da iyalinsa irinsa ba, ki yi kokari ki gyara hakan, sauran du saura ne marar karfi, domin kamar yadda kika ce, dama kika bada har yau aka ci maki zarafi haka, idan ba wannan damar dole a mutuntaki, mutun dama shi yake fara mutunta kansa , sai ki ga ana mutunta shi, hakan kuwa ta yannayin mu'amalarsa da mutanen dake zagaye da shi ne........."
Hajia kai take gyadawa har ya dasa Aya
A hankali ta yi murmushi ta ce" Ban taba tunanin zan ji kunyar Amina ba a rayuwa irin na yau"
Shima murmushin ya yi ya ce" bata rike ki ba, koda ta ji haushi ba zata wulakantaki ba"
"Hakane, tanada hakuri sosai, ta jima tana bautawa mijina , ama ba abinda ke shiga tsakanina da ita sai mugwayan kalamai..........na yi dana sannin wasu halayana, kuma in sha Allah sai na gyara abinda zai gyaru idan har inada sauran numfashi a duniya" Hajia ta sake fada tana kallon ABDUL
ABDUL ya ce" Allah ya aminta"
A nan dai suka ci gaba da dan zantawa, harta da masu girki da komai sai da ta sanar masa ga yadda za'a yi, uwa uba kayan da Amina zata yi anfani da shi na sunna, a gangaro kan irin kular da za'ana badawa na uwar da ƴaƴanta baki daya, abubuwa dai wanda shi da kansa sai da ya samu kansa da yin murmushin jin dadin hakan a zuciyarsa,
Ya san Uman biyu zata dube shi, ya san zata amsa shi, ya san yanzun da bata son Aunty hakan na nufin tana iya amsarshi a matsayin miji, idan kuwa ba haka ba bai san yaya zasu kare rayuwa ba, tunda shi dai ya san ita din kaunarsa ce, zuciyarsa ce, soyayarsa ce, jarabawar da zata rabashi da ita mai zafi ce, baya fatan ganninta, kai da ba dan kar ace wani abin sai yace gwara ta mutuwa da ita, wace ya san ya bar duniyar ne kwata kwata da ya yi wani tunanin daban
___________________________________
A hankali aka ci gaba da samun baki, aja amsar baki tare da alkhairansu
Kwonci tashi har ranar sunna ta zagayo yara suka dauki sunnan iyayensa mahaifa , ama suke masu kiranye da Ammar da amna dan kare sunnan
Taro ne aka yi na mamaki, taron da ya tara al'uma masu yawa, masu dauke da position din rayuwa kala kala
ABDUL RA'UF mai mutane ne, matasa da datijai babu wanda babu, masu hannu da shunni da mu du gamunan, taron da ya yi niyar cenza sutura sau uku irin na Uman biyu, tun ta farko da ya saka bai sake zaunawa bama bale ya cenza
Yana waje tare da jama'arsa ana shan sunna
A cikin gida kuwa tunda Risala ta bar bangaren nan sai a yau wunnin biki ta fito, shima a zuwan mahaifinta fatiha ya sameta ya yi mata wankin baban bargo da fada mata gaskiya mai dacin gaske, ya fada mata cewa idan ta yi wasa tana iya yin biyu babu, gwara ta sauke kanta ta yi zumunci da uwar gidanta su zauna lafiya
A dole ta shirya kanta cikin rantsatsiyar shada da gwala gwalai da rantsatsen mayafi ta je ta samu kujera ta kame tana dan dane danenta da dan kallon abinda ke faruwa, taron cike yake da manyan mutane jama'ar hajia da na ABDUL, wai abin arzikin da ake shigewa da shi dakin da aka ware dan kar a rikita dakin mai jego du na wannan matar ne? A dole ranta ya ci gaba da kunna na rufewar ido sai da ta yi da gaske sannan ta hanna kanta kuka tana biye da motsin kowa
Gani take yi kowa ya tsaneta
Gani take yi kowa a bayan kishiyarta yake
Gani take yi kishiyarta ta asirce mijinsu da danginsa ne
Gani take yi ba banza ba, wannan abin ba banza ba
Ba zata iya amincewa cewa matar da aka yi auren hadi da itane take da wannan taron a kanta da soyayar dangin miji, ita matar da aka auro dan soyaya an maida ita gefe ace kuma lafia ne
Sai dai ita ba zata iya wulakanta kanta haka ba
Babu wanda zata lashi kafarsa dan ta samu fada walahi
Kuma bata san kofar boka ba
Haka kuma.malami ba zai ci kudinta dan a karya ba
Ita kam ta bari da Allah kawai!, A ci gaba da nuna mata fifikota bari da Allah kawai!
Alhamdulilah taro ya ci lafiya ya tashi lafiya, jama'a na nesa da na kusa kowa ya kama gabansa an bar ma'aikata da gyaran gidansu,
Tun karfe bakwai yau Amina ta kwonta
Yaren kansu bata tsaya nemansu ba , sunna wajen Baba lauratu da ta dora ruwan zafi zata gasa masu jiki, idan sun gama tace su goya su, kanta tarwatsewa zai yi tsabar gajiya da ciwo
A hankali ta kwonta saman lalausar shinfidarta tana jan abin rufarta ta maida shi gefe ta kurawa waje daya ido ta afka a duniyar tunani
A yau ta ga abubuwan da bata taba tunanin zata iya gani ba a rayuwa na arziki da kauna da kwonciyar hankali
Kuma duka sun tarun mata ne dan ABDUL DINTA!,
Dan murmushi ta yi tana juyowa da dan karfi dan ta gyara kwoncintsa, sai dai me? Ido hudun da suka yi da shi ya sakata dan zarro ido tana dan mikewa tana kallonsa ta ce"
Abdul ya furzar da iskar dake bakinsa da dacin harshe ya ce" Ta shigo ne, sai irin ta tarar da Risala......to yau din ba lokacin Risalar bane, sai dai abin ya bata mata rai, ta yi fushinta sosai harma irin dai ta ce sai na saketan nan, Baba damuwata ban ganta ba, bata dakinta, bata bayi, bata ko'ina "
Baba ya dafe gaban goshinsa, a sanyaye ya ce" sai da na fada maka, horon nan da kake yi mata ya isa hakanan, sai da na sanar maka ya dace ka dubeta, ka yi mata uzuri, abinda nake son fahimta a kanta na fahimta, Abdul matarka na sonka , ba bata sonka ba, ama ka ki ka bude idannuwanka ka yi hakuri ka bta kulawar da ta dace da ita, ko dan abinda ke tare da ita......, Shin idan ba'a hakuri da mata za'a zauna da su ne? Kuma ita ai na ga da saukima ko?, To yanzu da ka fito ina kake tunanin ta tafi ne?"
Abdul ya dafe goshinsa shima , jikinsa du ya dauki ja abinka da farin mutun, ya ce" Nima ban sani ba, na yi tunanin ko wajenka zata zo?"
Hajia ta idasa saukowa har tana hade kafafuwanta ta Karaso da sauri tana fadin" Macen da lokacin haihuwarta bai cika ba kace tana nakuda ABDUL hankali ka daga mata har ya kaita da fara nakuda ko menene haka?"
ABDUL ya lumshe idannuwansa ya rasa amsar da zai basu,da ace zasu iya gane hallin da yake ciki, da sun hanzarta sun gabatar masa da ita a gabansa
Hajia ta ringa kai kawo tana ji Alkali na maganar ko gidan Baba Lauratu ta nufa? Ko gidansu? Ina zata je da daren nan ga ciki ga bacin rai?
Hijabinta ta gyara a jikinta tana nufar kofa ta ce" Ba inda zata je, nakuda ai ba abin wasa bace, tana cikin gidanta"
Kusan a tare suka mike sunna mara mata baya, kowane da abinda ke bakinsa suka shige mota daya baki dayansu Muhammat ya ja su suka sake komawa gidan
Cirko cirko suka same su ana ta maganar babu wanda ya fita da waya tsakanin Muhammat din da Sir din bale a yi kiransu a fada masu an ganta
Abdul ya sake fuskantarta bai ce komai ba yana kallonta
Hajia ta sake girgiza kanta ta ce" baka sani ba fa, ita fa siyarma du haka take, ka ga zamu hadu da yayan cikinmu, wasu mun yi jikoki da su mu yi ta abubuwa kamar ba zamu mutu ba, a yi ta iface iface da manyan da kananan, mu yi ta tsare tsaren yadda zamu samu mu ci kudade ko na waye, mu yi ta shiga hakin junna, uwa uba ABDUL RA'UF kulun bama koshi da abinda muke samu, kulun burinmi mu samu sama da abinda muka samu, ba ruwanmu da wa zai ritsa ko wa zai jigata, idan dai kawunnanmu suka wucewa jifa to ya fada kan kowama......, Abdul bama kaunar a rabamu da talaka, ba ruwanmu da talaka, mun manta mu menene tushenmu, da yawanmu sun rasa aurensu a haka, wasu a cikin haka sun rasu, wasu sun dimiya basa tuna komai irin Allah ya kyalesun nan..... Abdul yau nice na jawa kaina wulakanci irin haka? Wai a kan dan cikinka ake gannin bak dace na taba ba dan kawai na nunawa yarinya tsana? Bata min komai ba dan kawai bata kwaliya irin ta yan matan zamani, bata gwali da abubuwan yan matan zamani shikenan ni ga kakar Gwamna dole gwamna ya auro matar gwamna ko? A haka idona ya rufe na dauko yar mararsa kunya na hada a cikin ahalina, idan da haihuwa itama ta haifo ta kuma bada tarbiya irin wace ta damu a gidansu.........."
A hankali ya kama hannunta yana murzawa
A tausashe ya ce" Hajia ya isa haka kin ji? Ki kwontar da hankalinki, abinda ya faru ki kadara wani mataki ne na samun cenji a rayuwarki, ke mutun ce, baiwa ce ke, ba zai taba yiwuwa ki rayu ba laifi a rayuwa, baban laifi shine na daukan alhakin bawa, Allah baya yafe wannan, ki yi kokari ki gyara mu'amalarki da kowa, ki kokarta ki daidaita mu'amalarki da jama'a, ba wai Mom twins kadai ba, kowama, bama kamar Alkali, a kusa kusa ban ga namiji mai hakuri da iyalinsa irinsa ba, ki yi kokari ki gyara hakan, sauran du saura ne marar karfi, domin kamar yadda kika ce, dama kika bada har yau aka ci maki zarafi haka, idan ba wannan damar dole a mutuntaki, mutun dama shi yake fara mutunta kansa , sai ki ga ana mutunta shi, hakan kuwa ta yannayin mu'amalarsa da mutanen dake zagaye da shi ne........."
Hajia kai take gyadawa har ya dasa Aya
A hankali ta yi murmushi ta ce" Ban taba tunanin zan ji kunyar Amina ba a rayuwa irin na yau"
Shima murmushin ya yi ya ce" bata rike ki ba, koda ta ji haushi ba zata wulakantaki ba"
"Hakane, tanada hakuri sosai, ta jima tana bautawa mijina , ama ba abinda ke shiga tsakanina da ita sai mugwayan kalamai..........na yi dana sannin wasu halayana, kuma in sha Allah sai na gyara abinda zai gyaru idan har inada sauran numfashi a duniya" Hajia ta sake fada tana kallon ABDUL
ABDUL ya ce" Allah ya aminta"
A nan dai suka ci gaba da dan zantawa, harta da masu girki da komai sai da ta sanar masa ga yadda za'a yi, uwa uba kayan da Amina zata yi anfani da shi na sunna, a gangaro kan irin kular da za'ana badawa na uwar da ƴaƴanta baki daya, abubuwa dai wanda shi da kansa sai da ya samu kansa da yin murmushin jin dadin hakan a zuciyarsa,
Ya san Uman biyu zata dube shi, ya san zata amsa shi, ya san yanzun da bata son Aunty hakan na nufin tana iya amsarshi a matsayin miji, idan kuwa ba haka ba bai san yaya zasu kare rayuwa ba, tunda shi dai ya san ita din kaunarsa ce, zuciyarsa ce, soyayarsa ce, jarabawar da zata rabashi da ita mai zafi ce, baya fatan ganninta, kai da ba dan kar ace wani abin sai yace gwara ta mutuwa da ita, wace ya san ya bar duniyar ne kwata kwata da ya yi wani tunanin daban
___________________________________
A hankali aka ci gaba da samun baki, aja amsar baki tare da alkhairansu
Kwonci tashi har ranar sunna ta zagayo yara suka dauki sunnan iyayensa mahaifa , ama suke masu kiranye da Ammar da amna dan kare sunnan
Taro ne aka yi na mamaki, taron da ya tara al'uma masu yawa, masu dauke da position din rayuwa kala kala
ABDUL RA'UF mai mutane ne, matasa da datijai babu wanda babu, masu hannu da shunni da mu du gamunan, taron da ya yi niyar cenza sutura sau uku irin na Uman biyu, tun ta farko da ya saka bai sake zaunawa bama bale ya cenza
Yana waje tare da jama'arsa ana shan sunna
A cikin gida kuwa tunda Risala ta bar bangaren nan sai a yau wunnin biki ta fito, shima a zuwan mahaifinta fatiha ya sameta ya yi mata wankin baban bargo da fada mata gaskiya mai dacin gaske, ya fada mata cewa idan ta yi wasa tana iya yin biyu babu, gwara ta sauke kanta ta yi zumunci da uwar gidanta su zauna lafiya
A dole ta shirya kanta cikin rantsatsiyar shada da gwala gwalai da rantsatsen mayafi ta je ta samu kujera ta kame tana dan dane danenta da dan kallon abinda ke faruwa, taron cike yake da manyan mutane jama'ar hajia da na ABDUL, wai abin arzikin da ake shigewa da shi dakin da aka ware dan kar a rikita dakin mai jego du na wannan matar ne? A dole ranta ya ci gaba da kunna na rufewar ido sai da ta yi da gaske sannan ta hanna kanta kuka tana biye da motsin kowa
Gani take yi kowa ya tsaneta
Gani take yi kowa a bayan kishiyarta yake
Gani take yi kishiyarta ta asirce mijinsu da danginsa ne
Gani take yi ba banza ba, wannan abin ba banza ba
Ba zata iya amincewa cewa matar da aka yi auren hadi da itane take da wannan taron a kanta da soyayar dangin miji, ita matar da aka auro dan soyaya an maida ita gefe ace kuma lafia ne
Sai dai ita ba zata iya wulakanta kanta haka ba
Babu wanda zata lashi kafarsa dan ta samu fada walahi
Kuma bata san kofar boka ba
Haka kuma.malami ba zai ci kudinta dan a karya ba
Ita kam ta bari da Allah kawai!, A ci gaba da nuna mata fifikota bari da Allah kawai!
Alhamdulilah taro ya ci lafiya ya tashi lafiya, jama'a na nesa da na kusa kowa ya kama gabansa an bar ma'aikata da gyaran gidansu,
Tun karfe bakwai yau Amina ta kwonta
Yaren kansu bata tsaya nemansu ba , sunna wajen Baba lauratu da ta dora ruwan zafi zata gasa masu jiki, idan sun gama tace su goya su, kanta tarwatsewa zai yi tsabar gajiya da ciwo
A hankali ta kwonta saman lalausar shinfidarta tana jan abin rufarta ta maida shi gefe ta kurawa waje daya ido ta afka a duniyar tunani
A yau ta ga abubuwan da bata taba tunanin zata iya gani ba a rayuwa na arziki da kauna da kwonciyar hankali
Kuma duka sun tarun mata ne dan ABDUL DINTA!,
Dan murmushi ta yi tana juyowa da dan karfi dan ta gyara kwoncintsa, sai dai me? Ido hudun da suka yi da shi ya sakata dan zarro ido tana dan mikewa tana kallonsa ta ce"
Abdul ya furzar da iskar dake bakinsa da dacin harshe ya ce" Ta shigo ne, sai irin ta tarar da Risala......to yau din ba lokacin Risalar bane, sai dai abin ya bata mata rai, ta yi fushinta sosai harma irin dai ta ce sai na saketan nan, Baba damuwata ban ganta ba, bata dakinta, bata bayi, bata ko'ina "
Baba ya dafe gaban goshinsa, a sanyaye ya ce" sai da na fada maka, horon nan da kake yi mata ya isa hakanan, sai da na sanar maka ya dace ka dubeta, ka yi mata uzuri, abinda nake son fahimta a kanta na fahimta, Abdul matarka na sonka , ba bata sonka ba, ama ka ki ka bude idannuwanka ka yi hakuri ka bta kulawar da ta dace da ita, ko dan abinda ke tare da ita......, Shin idan ba'a hakuri da mata za'a zauna da su ne? Kuma ita ai na ga da saukima ko?, To yanzu da ka fito ina kake tunanin ta tafi ne?"
Abdul ya dafe goshinsa shima , jikinsa du ya dauki ja abinka da farin mutun, ya ce" Nima ban sani ba, na yi tunanin ko wajenka zata zo?"
Hajia ta idasa saukowa har tana hade kafafuwanta ta Karaso da sauri tana fadin" Macen da lokacin haihuwarta bai cika ba kace tana nakuda ABDUL hankali ka daga mata har ya kaita da fara nakuda ko menene haka?"
ABDUL ya lumshe idannuwansa ya rasa amsar da zai basu,da ace zasu iya gane hallin da yake ciki, da sun hanzarta sun gabatar masa da ita a gabansa
Hajia ta ringa kai kawo tana ji Alkali na maganar ko gidan Baba Lauratu ta nufa? Ko gidansu? Ina zata je da daren nan ga ciki ga bacin rai?
Hijabinta ta gyara a jikinta tana nufar kofa ta ce" Ba inda zata je, nakuda ai ba abin wasa bace, tana cikin gidanta"
Kusan a tare suka mike sunna mara mata baya, kowane da abinda ke bakinsa suka shige mota daya baki dayansu Muhammat ya ja su suka sake komawa gidan
Cirko cirko suka same su ana ta maganar babu wanda ya fita da waya tsakanin Muhammat din da Sir din bale a yi kiransu a fada masu an ganta