← Book details Ni Zan Ladabi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 83

Sashe 11

Ni Zan Ladabi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kanta na kallon kasa take tunanin amsar da ta dace ta bashi, ita ko daya ba maganar talaka ko mai kudi ke gabanta ba, ita burinta ta samu datijo ko yayane wanda zai juri zama da ita da ƴaƴanta, idan ta auri Mutari ina zata kai biyu? Mutari kansa nada nasa ya'yan hudu da matarsa, matarsa sau biyu tana mata tataki da habaice habaice da komai, sai dai ita ba tsoront take ji ba, ba kuma wannan zai sa ta bar Mutari ba idan har ta yi niyar aurensa, matsalar daya ce zuwa biyu, wace ta fi karfi ƴaƴanta, sai kuma shi din kansa, mutari ba wani baba bane in ya yi nisa ya bata shekara hudu, irin saurin auren nan ne na mutanenmu na gida har ya tara ya'ya hudu, ita yanzu ta auri wanda ya bata shekara hudu ai ta auri yaro, salon su kama gardama a gida ya wanka mata mari ko? Ko ya kamata da kokowa? Bata tunanin hakurin da ta ji da shekara ashirin da tara zata cike talatin a duniya zata zo kuma ta dsa rayuwar wahala da wani namijin, ko kamaceceniyar rayuwar kanwarta, ba ztaa iya jurar a wulakanta mata yan bayin Allan ƴaƴanta ba

A sanyaye ta ce"

Ku zo fa mu je mata💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻, barkarmuda safiyar litinin
🙇‍♀️🙇‍♀️🙇‍♀️🙇‍♀️🙇‍♀️🙇‍♀️🙇‍♀️🙇‍♀️🙇‍♀️🙇‍♀️
_*NI ZAN LADABI*_
🙇‍♀️🙇‍♀️🙇‍♀️🙇‍♀️🙇‍♀️🙇‍♀️🙇‍♀️🙇‍♀️🙇‍♀️🙇‍♀️

*NA*

*SAJIDA NIGER*

Asalamu alaikum wa rahamatullah, makaranta novel dina gani na dawo da sabon takarda, sabuwar tafia, sabon salo mai dauke da darusan rayuwa, da karfin ikon sunnah, da gwagwarmaya da kula kula, rayuwa ce irin ta talaka bawan Allah dake gannin hawa da sauka dan ya rayu da mutuncinsa, rayuwa ce ta Mace mai dauke da hatsari, sadaukarwa, Biyaya da karfi.......zai zo maku da shafuka na gyara tun daga kan fatar jiki, ppart, sirika irin na cikin kurya a gangaro kan sabulai na sana'a da kuma turaran HUMURA wace kowace mace zata iya yiwa kanta tsumamen hadin tada hankalin mai gida

Wannan Novel na kudi ne ba free bane

Yan Nigeria jama'ata ga naku : 500 Naira
account number: 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi GT Bank sai ka turo shedar biyanka ta numberta kamar haka +227 93811618 SAJIDA NIGER

Gareku wa'inda suke son turo kati ko yin POS, kunna iya turo katinku ta numberta kamar haka 93811618 idan ka turon hoton katin sai na saka ka a grup, katin MTN ne, na gode sosai

Jama'ata yan NIGER ga naku : Dala dari , 500 francs cefa ta katin AIRTEL ko SAHELCOM ka turo ta numberna kamar haka 93811618 sai na saka ka

*NA gode sosai, Allah ya saka da alkhairi, sai kun zo🥰🥰🥰*

*Page 0️⃣7️⃣*

A sanyaye amina ta ce" Ka yi hakuri Muctar, zan karasa gida bana son tsayuwa a bakin layi"

Da dan sauri ya daga kafarsa yana biye da ita dan har ta juya ta fara tafia,
Bata yarda sun jera ba, ama idan ka gansu zaka gane tare suke, a tafiyyar da suke yi kuma kasa kasa maganar ya ci gaba da yi mata har suka karasa kantinsa
Da mamaki yake tambayarta dama nan din zata zo ta ki bashi sako?

Amina ta yi murmushi kawai ta mika kudi tana zayano abubuwan da take da bukata na kayan kosan da take son farawa na safe bisa shawarar inna lauratu

Dagewa ya yi kan sai ta amshi kudinta, a dole ta fuskance shi a nutse ta ce" Muctar, ka san bana kulaka dan wannan, ka san ba yau ba ka nuna mu ringa amsar cefane na nuna maka aa, ka yi hakuri ba zan iya amsar kayan sana'arka ba, nima sana'a zan fara da wannan din, inada na jarin, ba raina maia na yi ba, na fi so na saka gumina dan na fi gane gaban nemana"

Shi kam gaba daya irin yadda take zile masa na matukar damunsa, du yadda ta ki amsar wani abin sai da ya zuba wani ba tare da ta gane ba, sai da ta isa gida ta ringa cin karro da abubuwan da ya karra mata, sosai ta ji ba dadi domin dukkan abinda zai taba mata mutuncinta ko kwonciyar hankalinta takan yi iya yinta dan kiyaye alakar da zata taba mutuncinta, shi yasa a rayuwa du tsakaninta da kai bata yarda da kyautuka irin na yau da gobe koda na saurayi da budurwa ne

Kilace komai ta yi ta gyara wakenta da nufin kaiwa markade gobe da karfe tara , domin kosan na yan gayu ne na masu karin karfe goma ne zuwa sama

Washe gari da sasafe ta gama dukkan abubuwan da suka zamo mata jiki, yau din Alhamis ce tun kusan karfe takwas har rana ta fito ta fara kwalar kawunnan mutane, Su Amina na daya daga cikin wa'inda ranar ke kwala a bakin titi daf da kwata sunna jiran dan adaidaitan da suke wahala yau

Husaini kan buda ruwansa ya didika ya rufe ya maida a jakar makarantar, yau fa basa yin karatu ama mamansu ta ki yarda tace ita jiya ba'a fada mata ba yau ba makaranta, shi kam gaba ta kaishi domin an saka masa bota a boredinsa ga kuma naira ashirin dinsa a jaka, kwanakin nan gidansu dadinsu kawai suke ci, sunne taliya, sunne shinkafa da miya ta gwamnati mai dadin hadiya, sunne biredi da bota, jiya harda alewar tsinke yar goma goma mamansu ta siyo masu, sun zama yan gayu , cin dadi suke yi ba kama hannun yaro, shi yasa shi kam fara'arsa har kamar zata yi yawa , baya fada da kowa baya jin haushin kowa, Hasan ne hali baya barinsa, du dadin nan ya ga damar ya tashi yana fushi ya ki kula kowa a gidan

Ajiyar zuciya Amina ke saukewa lokaci zuwa lokaci tana sake hangen titin a zuciyarta tana karra ayana' ikon Allah, yau kamar an yi ruwa an kafe ? Basu da yawa yan adaidaitar kuma du a cike? Gashi har lokaci zai shige na makaranta gashi ban kai markadan ba, Allah la turo mana dan sahu na mika su na dawo'

Gali mai ruwa ne ya karyo kwana da kurar ruwansa shake yana turi, Gali kan kaiwa Amina ruwa lokaci zuwa lokaci, bama kamar in zata fara sana'a domin ruwan pampo ne yake siyarwa sosai an yarda da tsaftarsa ga kuma sauki, Gali dai saurayi ne mai zuciyar nema, yana zaune ne a gidan mahaifiyarsa tare da mahaifiyar tasa da kannensa uku yan mata, gali shine komai nasu, jajircewarsa ta sa basa zama da yinwa, mutane da yawa na mamakin irin yadda Gali ke samun kudi, sandar ruwan dai gaba daya naira ashirin da biyar ce duka duka, a cikin kurar gali bai fi sanda goma ba, kuma a wuni in ya yi zagaye mai yawa ya yi zagaye hudu, domin harka ce ta ruwa kusan mutane da yawa nada rijiya a gidajensu, yawanci masu sana'ar shayi ne da kuma masu halin siyan na pampo dan sha a gidajensu yake kaiwa ruwan, ama yanzu haka wayar da Gali ke anfani da ita a kadan zata doshi dubu hamsin, kaf anguwar nan an san gali da gayu da ba naira kashi, abinda ba'a sani ba shine shin a ina Gali yake samun kudade zafafa haka? Da yawa abokansa sun fada sana'ar siyar da ruwan suma, harma sukan yi fita fiye da tashi a wuni, ama abinda aka fi karfi cimar kaiwa baka ce, bayanta du wata rigimar da kudi zai warware sai dai a yi kamo nan kama cen a yi wace idan ba'a yi ba ana iya mutuwa ko a jigatu, sukan kalli Gali a matsayin wanda ya iya sana'a fiye da su, basu san wanene Gali ba!

Tunda ya shanyo kwanar ya tsaya dan kusa da su kadan yana dariya ya ce" Hajia Amina ikon Allah, yan matan jiya yan matan yau, kun ci zamaninku kun haye na kannenku har kun fi su kyan kamani"

Amina ta sale tamke fuskarta, a duniya ta ki jinnin dukkan wani furuci ko lamari da zai saka yan ƴaƴanta dago kai su yi mata kallon Mama ke da kanki? irin kallon nan dai na mamaki da wasu lokuta zaka ga danka ya nuna a kan wani lamari da ya ga ya faru da kai ko a gabanka baka dauki mataki ba,
Bata san dalilin da yasa Gali idan zai yi mata magana yakan saki jikinsa ya ringa yi mata tsokanar da ta wuce misali, ita dai sa'arsa bace, ita ba wani wasa take yi da maza ba irin da zaka ga budurwa tana shigewa maza da son yin wasan banza da su ba, hasalima samarin anguwar nan na mutuntata ta hanyar kuranta da aunty, ko wani ka ga zai mata ba daidai ba to fa bako ne kuma idan wani ya ji zai masa magana, kare mutuncinta da girmamasu da take yi ya sa suke girmamata itama, ama bata san shi me yasa yake yi mata irin haka ba, sam bata jin dadin irin wasan nan

Bata bashi amsa ba, ama bai karyar masa da gwuiwa ba yana kare mata kallo yauma dai cikin hijab, ita dai kulun a hijab ya ce" Makaranta ba za'a kai biyu? Hajia Amina ai yanzu malan Muktar ke fada min yau fa akoy kosai, na ajiye jarka biyu ta ruwa a wajensa ya biya kudin, shine nace ko dai da yayan namu za'a shige daga cikin ne?"

Da takaici ta juyo zata yi masa magana sai ji ta yi shaaaaaa ruwan dake kwonce na jikin kwatar nan an maka masu shi daga ita din har biyun, da Galin gaba daya

A haukace du suka bi bayan motar da ta aikata haka, walahi bata san lokacin da ta saka ihu ihu ta daga hannunta da ya wawuro dutse ta daga kafarta daa dan gudu ta cila dutsen nan da dukan karfinta da karfi kuma ta ce" Allah ya isa mugu ko muguwar dake cikin la'annaniyar bak'ar mota! Allah ya isa rainin hankalin banza da woffffffffffi dan ba'a dan zafin haihuwa ba ina tsaye da y'ayana za'a watsan ru.......................!"
Chapter 11 · 0% Book details