← Book details Ni Zan Ladabi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 46 OF 83

Sashe 46

Ni Zan Ladabi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

'innalilahi' Amina ta ayana a zuciyarta tana cire dubanta a kansa ta maida kasa
Rasa abinda zata yi cikin kin zuwa din ko zuwan ya sakata sake damkar zannin gadon dake rabe da jikinta ta juya jiki a mace ta nufi dakin da ya nuna din, domin idan akoy abinda ta yarda da shi a lokacin nan daya ne tak, shine ba zata iya hada ido da mutumen nan da tsoron kar aje ya san abinda ya faru da ita ya cika mata ciki

Du yadda ta so tafia da sauri a dole ta tafi a hankali ta shige dakin tana tafe a hankali

Muryar doctern a nutse da ta nuna mata bed din dake kasace da wata niimtaciyar shinfida tana fadin" Madame, a nan zaki kwonta dan kasa ba zai maki dadi ba" domin ta kula kamar Aminar nema take ta yada zango a saman cafet din dakin shi yasa ta katse mata hanzari

Amina ta ka numfashi ta karasa ta zauna a ringeshe tana rintse idannuwanta

Zama likitar ta yi ta fuskanceta sosai , a nutse ta ce" Madame?"

Amina ta kalleta sannan ta sake sada kanta hawayen da ya cika gurbin idannuwanta ya ringa hayewa jikin gashin idannuwan nata

Yannayinta ya saka matar sake fahimtar abinda docter Mansur ya dan kwatanta mata a gajarce

Murmushi ta yi a nutse ta ce" Kin ga, tun kafin na dubaki yannayin tafiyarki ya sheda min kina cikin halin bukatar taimakon gagawa, kin san shi wannan waje waje ne mai hatsarin gaske, babu wajen da ya kaishi bukatar taka tsantsan da samun isashen kula a duniya, kin ga idan ido ya makance zaki iya rayuwa normal, ama idan shi ya rube ba zaki anfanu ba da dadi a rayuwa, koda kin rayun tofa a cikin wahalar rayuwa ne, karshema kina iya yinta rayuwar ke daya a kauye daya dan gujewa wulakancin mutun, ina so ki yi aiki da iliminki, ki bani dama na dubaki a yi maki dukkan abinda ya dace a maki, Ni likita ce, Gynécologue ce ni, na jima a saman aiki a kadan na shekara goma sha daya, ina duba Hajia ne kawai a familly dinku sai yanzu kika shiga layi bisa umarnin SIR, zan so ki yi anfani da iliminki mu taimakeki ki ji saukin jikinki, ina fata kin fahimta?"

Kan Amina a sadden take tunani kala kala a cen cikin zuciyarta

Muryarta a sanyaye ta ce" Aunty, wanene SIR?"

Docter ta yi murmushi itama da kula tace" SIR ABDUL RA'UF sister"

Amina ta dago idannuwanta a hankali tana kallon matar
Eh lalle matar nan ta fada mata gaskiya, idan ta yi wasa da jikinta da lafiyarta itace a ciki, yau idan ta lalace a kwonce wa zai kular mata da biyu?, Kuma matar ai ba yarinya bace dimin ko a haka da take wanke jikinta ya nuna ta bata wasu shekaru goma ko sama

A hankali tace" Aunty na cire kayana ne?"

Docter ta sake yin murmushi da kula sosai ta ce" Aa ba duka kayanki ba, iya zanninku ne mu duba wajen"

Karshe dai tabas Amina ta samu kari, kuma a lokacin Docter ta hada allurar dinki ta yi mata shi, wanda saida Amina ta ringa hawaye tamkar zata summa dan azaba, domin wajen ya kwana ya sake rinewa da wahala, ana yi mata tana tunanin anya akoy wahalar da ta kai wace ta sha daga jiya zuwa yau? Sosai ta karra daukan zafi da yaron a zuciyarta, dinki? Kamar wace ta haifo kan dan mutun daga jikinta? Wannan wani irin cin zali ne?

Docter na gama yi mata tana mata sannu ta bata magungunna na zazavi da kuma na samun sasaucin radadin, cikin nutsuwa bayan Aminar ta rage jin radadin harma ta taimaka mata ta cenza wata riga yar yololuwa dan ta samu hutun mai dadi sannan ta sake bata shawrwarin yadda zata kula da kanta, ta fada mata cewa karta einga gasa kanta yanzu, ta bari zuwa jibi dinkin ya fara neman hanyar warkewa sai ta fara gasa kanta

Amina ta gyada kanta barci na fuzgarta dan ba wani isashen barci ta samu bafa a hankali ta ce" Aunty, dan Allah karki fadawa kowa cewa har kari na samu sanadiyar wannan, sanadiyar sa"

Docter ta zuba mata ido na dan dakikai, sanadiyar wannan din da ta hadiye ya dan so ya sakata a tunanin wannan me? Sai kuma ta ture tana murmushi tace" Karki damu, in sha Allah wanda ya dace ya sani kawai zai sani, ba zan sanarwa wani hakan ba"

Amina ta gyafa kanta tanai mata godiya sannan ta rakata da ido har ta fice a dakin

A hankali dan sanyin Acn na dan ratsata har barci yayi awon gaba da ita a saman lalausar shinfidar gadon , barci mai nauyi da kuma ragewar radadin wajen, hakan ya sa ta lula a barcinta har tana sauke ajiyar zuciya

Sosai Docter ta sake yiwa Baba lauratu bayanin abinda ya dace a yanzu ta ringa ci dan jikinta ya samu wadatacen kulawar da zai yi gagawar warkewa, ta sake jadada mata kar a ringa shiga ruwan yanzu, ta kuma yi nata maganar zama da hade kafafuwa da kula sosai domin kofa ba da kanta ta haihu ba idan zafin dinki ya sa a yanzu ta ringa zaman da iska ke iya shigarta sai ta shigeta ta zo tana fama da tusar gaba

Sosai Baba ta mata godiya ta rakata sannan ta dawo itama ta ringesa tana yiwa Allah godiya da sake duban falon nan, sai ta saka harshen hijabinta ta share hawayenta a fili ta furta" Mahakurci mawadaci kennan, ashe mijinki na nan rantsatse Innar marigayiya? Kinga yyau harda yan aiki ne da ke , Allah dai ya maba maganin sabon halin da ya sameki uman biyu, ki yi hakuri ki yiwa mijinki *LADABIH*"

Tunda suka fito suke dan tafe haka a hankali tana yi masa bayanin matsalar da kuma solution din da ta dauka , sosai ya gamsu da komai harda maganin da ta bata,
Har bakun motarta ya rakata yana sake yi mata godiya domin a aiki ita din gaba take da shi, kuma irin yadda rake mutuntashi da sauran ma'aikatan dake karkashinta ya sa summa suke mutuntata a rayuwa

Yana tsaye har Motarta ta fita a gidan sannan ya juyo wajen da ya hange shi tunda suka fito ya daga kansa

Yana tsayen kuwa hannunsa daya a harde a bayansa, dayan kuwa ya dafe abin madubin shima yana kallonsa

Murmushi ya yi ya tunkari part din nasa ya bude ya shiga falon ya ratsa ya shiga hawa matatakalar

A gajiye ya idasa hawa ya tsaya ya bubuga sannan ya murda ya shiga

Dafe da bayansa ya shiga yana kallon ABDUL dake zaune saman wata lalausar yar madaidaiciyar kujerar da ta yi masa kadan yana fadin" Kaikaikai, wannan idan na yarda na yi hawa goma a wata guda tabas zaunewa zan yi, wai ku yan gayun nan me kuke ji a gidan sama ne? Du ku bi ku mutu shekarunku basu kai mutuwar ba?"

ABDUL ya yi murmushi yana dauke kansa a kan Mansur ya ce" Idan ka ga ka mutun dama a rube kake man , ba laifin Upstairs bane"

Shima dariya ya yi dan yadda ya yin wai irin ya tsokale shin nan

Zaune ya kai kusa da shi kadan yana bashi hannu ya ce" Yaya kake? Ya jikinka?"

Abdul ya amshi hannun suka gaisa sosai a hankali yace" Mansur bani da lafiya ne?"

Mansur ya dage kafadarsa yace" na sani, na ga ka zama na daki kamar wani sabon ango........"

Abdul ya ce" Uhum" sannan ya yi shiru yana sake zubawa waje daya ido

Yan sekwani sun ratsa tsakani a hankali ABDUL ya ce" Wa ya dubata ne?"

Da gangan Mansur ya ce" Wace?"

ABDUL ya zuba masa ido, sai kuma ya tabe bakinsa yana kawar da kansa ya yi shiru

Yanzunma sun sake daukan lokaci Mansur ya ce" Da gangan ka yi, ko a rashin sani ka yi? "

ABDUL ya sake kallonsa, ya kuma cire kansa bai bashi amsa ba

Mansur ya yi murmushi ya ce" Ban taba tunanin zaka yi irin aikin nan ba, domin kanada ilimi"

"Ka daina magana kamar wanda kaima baka cikin mamakinta, abinda nake son sani a lamarin nan shine....mata ana yi masu halitar virginity biyu a rayuwa ne ko.......ko TWINS ba, ba ita ta haife su ba?" ABDUL ya fada a dake yana murza gaban goshinsa kadan

MANSUR ya ce" Sai dai idan Twins ba ita ta haife su ba, ama babu macen da aka halita da budurci biyu a duniya, fannin likitan mata ka karanta, kasuwanci ya kamaka ne, ya zame maka dole ne, ko kana so ka cemin akoy abinda ke iya rudaka ka shiga tunanin anya abinda ka gani haka ne ko ba haka ba?"

Da ido ya tsatsare Mansur, sai ya ga kamar wani wanda ke jiransa ya kwonkwonce masa nagangannu, to a ganninsa menene na sin titsiye shi? Me yake son fadi a maganarsa na cewa akoy abinda zai rikitashi a kan wannan lamarin ne?

A hade ya ce" Me kake nufi da na rikice na kasa fahimta?, Emotion mai karfi irin na MACEN DA AKE YIWA gagarumar soyaya, ko karfin kauna irin ta iyaye?"

Mansur ya yi murmushi a zuciyarsa, a bayane kuwa ya ce" tambaya na yi"

"Amsarka itace ba dayan biyu" ABDUL ya maida masa yana sake dauke kansa

Mansur ya dake yin murmushi yana ta kallon ABDUL, he can't believe it, ABDUL abokinsa , amininsa ne ya wayi gari da wannan farin cikin da yake dannewa karfi da yaji, ya kasa fahimtar alkiblarsa a yanzu, idan ya yi kamar ya tsani lamarinta, sai kuma ya tare mata wani abin

Mikewa ya yi yana murmushi yace" Ya dace ka dauki magani kuma ka yi sleep, ND.. .......nd ........." Ya dakatar da maganar yana kallonsa kamar tadda shima yake kallonsa

Mansur ya ce" Nd kana da tarbiya, u'r a gentle Man, ya dace ka kwatanta kula a gareta............, Kamar yadda ka fada ne, tanada shekaru kadan a saman kanta.... but tamkar baby haka take....she need ur care "
Chapter 46 · 0% Book details