Sashe 76
Ni Zan Ladabi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Karasawa ta yi tana kallon Risala ta ce" Ke tun jiya kina ina har mu na waje muka shigo muka raka yar uwarki haihuwa bakya wajen? Sannan har aka sakomu yau sai yanzu zaki zo?"
Risala ta sosa gaban goshinta da uwar makup din da ta sha tana inda inda ta ce" Hajia sai yanzu na ji ne"
Hajia ta gyada kanta tana yin kwafa ta dubi mahaifiyar Risala dake dan jujuyar da kai irin an takurawa y'arta fa ta ce" Hajia fahimtar da ni Hajia"
Maman Risala ta ce" Gani na yi yaushe kuma kuka shirya da yarinyar cen ne da har zaki dauki y'arta a hannunki kina koya mata shayarwa?"
Ido hajia ta zarro, wani irin mamaki na neman kasheta
Ta juya ta kalli wajen yan matan da kuma ABDUL da ya ciro waya ya koma ya gyara zamansa yana daukanta hotuna a dabarance yana murmushi
Hajia ta ce" Hajia kin kuwa san me kika ce? Na shirya da yarinya har na dauki danta? Ai ni dama ban yi fada da yarinya ba ra'ayina na fada na kuma ja mijina ya ja, a yanzu da na ga har karuwa ta samu kuma na sakar ko a kaina aka fara nuna kiyaya wa matar Da ne kuma daga baya a sota? Ko kina so ki fitar min da wata irin magana irin ta wadda baya gane abinda yake fada cewa ni Hajia Hauwau Alkali me ya hadani da daukan gudan jinnin ABDUL RA'UF Umar Faruk Aliyu?"
Da sauri yayarta ta ce" Hajia, du fa ba cen ta nufa ba, ai ita bata san kin sauko daga kiyayar da kike yiwa matar jikan naki ba shi yasa ta yi mamaki har ta furta, kin san ita batada munafurci ko cem, takan fadi abinda take tunani komai muninsa ne sai dai ka yi hakuri idan ya maka ciwo"
Hajia ta gyada kanta ta ce" Hakane, ba mamaki, halaya ne ai na mahaukata, gashi ita kuma cikin kyakyawar shiga"
"Hajia nice kike zagi da mahaukaciya kuma yau?, Hajia nice mahaukaciya? Walahi ni ba mahaukaciya bace, ai ba karya aka yi maki ba, da baki nuna mata kiyayar ba ai da ba zan zo na fada ba, ko kin ga na maki kage a nan ne? Maman risala da itama ta harzuka ta fada har tana cire hannun yar uwarta dake mayar da ita baya dan bata so ko kadan Maman risalar ta zubar da mutuncinta a idannuwan sirikinta, duda aikin gama ya gama sunne basu sani ba, a hausa ai ba'a haka, bahaushe da kunya da kara aka sanshi ba shirme ba
Rai bace ta ce" Dan Allah adda ki daina turani haba dan Allah, ita komai ya tashi sai ta wani nemi ta wulakanta mutane , ai nima ba yar talaka bace bale a zageni da arziki, ita yarinyar da kika tsana din ai dan yar mai datin hula ce, ko karya aka yi? Kema da bakinki kin ce jikanki ba zai zauna da mai tuyar waina tana bi kwararo kwararo da ƴaƴan shegu a hannunta ba, shine yanzu zaki wani hade kai da ita a cutar min ya? Ba zai yiwu ba tunda aka fara haka Risalar ba zata ga da kyau a wajenki ba, Risala kuwa yar gata ce gaba da baya ba zan bari a wulakanta min yata ina ji ina gani ba, koda banida da shi ba zan yarda abinda kika yiwa wancen ki yiwa yata ba walahi!, Ke risala wuce mu tagi gida wuce min!" Sama sama take maganar danma du wanda bai ji ba ya ji, gaba daya zagin da ta juyewa su Amina da wulakanci tasss kowa ya ji haka kuma sirikinta dake murmushi gaba daya murmushin ya dauke a fatar bakinsa
A nutse ya mike cikin shigar dakakiyar shadarsa ya karaso yana kallonsu
Aa hankali ya ce" am, ku yi hakuri ku koma waje, yanzu ta fito daga asibiti hayaniyar nan ba zata haifar mata da abin alkhairi ba................"
Maman Risala ta tabe baki, bata sake wata muguwar maganar ba dan ko HAJIAR gaba daya bakinta a mace tana kallonsu ne
Maman Risala ta sake lekowa ta ce" Ke wai ba da ke nake ba dan kutumar ubanki?"
Risala ta juyo ifannuwanta sun cika da kwallah ta fara taku daya biyu ta tsinkayi muryarsa a dakensa ya ce" Idan kika fita daga get din gidana a yau ba tare da izinina ba na yanke igiyoyin aurena dake kanki"
A haukace ta ci birki tana juyowa ta kalle shi idannuwanta na firfitowa waje
Haka mahaifiyarta da yar uwarta, haka hajia ta juyo tana kallonsa zuciyarta na karra tsintsinkewa
Bakinta na rawa ta ringa nuna kanta, da shi tana son furta wani abin ama ta rasa mene
Mahaifiyarta ta sake shaka ta saka hannunta ta fardota tana fadin" Sai me, ai mai kyai baya tsawa , wuce mu je Alhamdulilah ba ciki bs goyo bale abin duniya ya isheni, menene a auren da ya wuce cusa bakin ciki da kaskantar da mutun da darajarsa da komai? Wuce mu je zaki samu sama da shi a komai, ai ba shi bane autan maza a duniya!"
Janyo hannun yar take yi , yar na tirjewa
Da karfi ta sake juyo da ita dan ta fuskanci kamar bata jinta, sai dai abinda y'ar ta yi ya sakata zuba mata ido, domin hannunta ne ta janye a hankali hawaye na zubowa yana neman bata kwaliyar da idan biya ne zasu yi a yi mata zasu iya kwararar dubu hamsin
A hankali ta ce" Risa, mu tafi mana kar rana ta yi zafi ta taba maki fata kin ji?"
A hankali Risala ta langwabar da kanta tana kallon Mamanta
ABDUL kuwa ya kama hannun Hajia da ta zama tamkar gunki ya shige ciki da ita, direct dakin Fido domin ya kula tana da bukatar dan kadaicewa ko yayane
A hankali Maman Risala, dan kar su Amina su jiyota ta ce " Me kike nufi da dakatawa a nan bayan kina gannin wulakancin da ake mana , ni uwarki da ke din kanki?"
Risala ta fashe da kukan da take rikewa ta kasa yin magana
Mamanta ta zarro idannuwanta tana nuna kanta ta ce" Risa, risa namiji zaki zaba a kaina?"
Da sauri ta girgiza kanta tana kallon mamanta ta ce" Aa mama, ba maganar na zabeshi bane mama, mama a shekara ashirin da takwas na same shi, na so shi, ya so ni, mun yi aure, yanzu na kai ashirin da tara a duniya, idan har ba zanen kadara ta fitar da ni ba zaki so na dawo na sake maki wani zaman? Mama banida matsala da shi, ban rasa komai ba, kema kin san a aurena zuwa yanzu na tara abinda ban tara ba kafin auren nawa......., Mama kakarsa ce, itace mamansa, itace duniyarsa, idan tana fada s kansa bana gannin laifinta, kamar kece da mu fa.........
, Mama, babar matsalarma ina son shi, mama ina son mijina, idan na biki muka tafi na dawo ina neman saka kanmu a uku baki dayanmu fa? Dan na tabata wata rana sai na tarda ABDUL, idan yau ya koreni, gobe ya koreni, jibi ya koreni, wata rana ina iya samun galaba a kansa, ina iya sakashi a uku, uwa uba na saka kaina...Mama ribar me zaki ci?....."
Dau mahaifiyarta ta dauketa da wani mahaukacin Mari tna nunata da yatsarta ta ce" Ni zaki watsawa kasa a ido a kan Kato?"
Risala da ta duke tana kuka tana girgiza kai, yayar mahaifiyarta na rike mahaifiyar tata har suka janyeta suka fita da ita a falon Amina sannan ta mike da gudu itama ta fita ta nufi bangarenta tana cire abubuwan kwaliyar da aka bata lokaci ana mata dan ta yi kira ta sanar kishiyarta ta haihu , mahaifiyarta ta zabo mata leshen dake da kyau da tsafa aka caka mata dauri, ama abin ya kare a haka? Yanzu yau ita da mahaifiyarta ne wannan abu ya faru? Ina zata shiga da ranta? Shin ABDUL da mamanta wane zata zaba? Idan ta yarda ta zabi Abdul din ya wulakantata da gaske fa? Shin yaya zata yi da rayuwarta?
Wayarta ta dauka ta ringa kiran mahaifinta, sai dai ya fada mata yana cikin aiki, da zarar ya zauna zasu yi magana, a dole ta kashe ta ci gaba da kukanta, domin an saba mata tana samun damuwa takan yi kiran mamanta ne ta zo inda take, ama a yau da maman nata ne damuwar a dole ta rasa inda zata saka kanta
____________________&__
A cikin daki,
Tunda ya zaunar da ita ya fice ya je ya samo mata ruwa mai dan sanyi sannan ya dawo ta wajen su Firdausi dake zaune jigum jigum yana dan murmushi ya ce" Sorry an mata mun shiga dakin cen dan lokaci?"
Fido ta yi murmushi tana fadin" Dady mu da muke nan muna dan hirarmuma"
Shima ya yi murmushin ya kalli Amina kkasa kasa ya ce" Sun sha?"
Manyan idannuwanta ta dago ta dora saman fuskarsa, a hankali ta dan masu kasa kasa sai kuma ta mayyar bakin hanyar da Fido ta bi dan basu waje
Murmushi ya yi ya sake fadin" kins da kyau, jan ajin kuma ya amsheki Hajiar ABDUL"
Yanzuma baki ta dan tabe bata ce masa komai ba har yaa mike ya nufi ciki yana jin dan damuwa na rashin kulashin da take yi
A hankali ya zubawa HAJIA bayan ya bude ya mika mata sannan shima ya zauna a gefenta ya yi shiru yana sauraron hucin dake fita daga bakinta
A hankali Hajia ta sauke numfashi tana girgiza kanta ta ce" Ka san a duniya, babu wulakantace sai wanda ya wulakanta kansa ta hanyar daukan duniyar nan a wani abu mai dorewa, bayan tunda aka haifeka kake gannin jariri, yaro, saurayi, mai aure, uba, tsoho, mace ko namiji na mutuwa sunna zuwa wajen da ba'a katse rayuwar sai dai ka yi ta girban abinda ka shuka na dindindin, ama a haka muke manta komai muna aikata abubuwan da suka fi karfin kawunnanmua........"
ABDUL ya sake dubanta a hankali ya ce" Daj Adam din kennan, alkhairinsa ya kasance mai rokon gafarar ubangijinsa sannan ya tuba da gaskiya da daukar niyar ba zai kuma maimaita laifin da ya aikata ba"
Risala ta sosa gaban goshinta da uwar makup din da ta sha tana inda inda ta ce" Hajia sai yanzu na ji ne"
Hajia ta gyada kanta tana yin kwafa ta dubi mahaifiyar Risala dake dan jujuyar da kai irin an takurawa y'arta fa ta ce" Hajia fahimtar da ni Hajia"
Maman Risala ta ce" Gani na yi yaushe kuma kuka shirya da yarinyar cen ne da har zaki dauki y'arta a hannunki kina koya mata shayarwa?"
Ido hajia ta zarro, wani irin mamaki na neman kasheta
Ta juya ta kalli wajen yan matan da kuma ABDUL da ya ciro waya ya koma ya gyara zamansa yana daukanta hotuna a dabarance yana murmushi
Hajia ta ce" Hajia kin kuwa san me kika ce? Na shirya da yarinya har na dauki danta? Ai ni dama ban yi fada da yarinya ba ra'ayina na fada na kuma ja mijina ya ja, a yanzu da na ga har karuwa ta samu kuma na sakar ko a kaina aka fara nuna kiyaya wa matar Da ne kuma daga baya a sota? Ko kina so ki fitar min da wata irin magana irin ta wadda baya gane abinda yake fada cewa ni Hajia Hauwau Alkali me ya hadani da daukan gudan jinnin ABDUL RA'UF Umar Faruk Aliyu?"
Da sauri yayarta ta ce" Hajia, du fa ba cen ta nufa ba, ai ita bata san kin sauko daga kiyayar da kike yiwa matar jikan naki ba shi yasa ta yi mamaki har ta furta, kin san ita batada munafurci ko cem, takan fadi abinda take tunani komai muninsa ne sai dai ka yi hakuri idan ya maka ciwo"
Hajia ta gyada kanta ta ce" Hakane, ba mamaki, halaya ne ai na mahaukata, gashi ita kuma cikin kyakyawar shiga"
"Hajia nice kike zagi da mahaukaciya kuma yau?, Hajia nice mahaukaciya? Walahi ni ba mahaukaciya bace, ai ba karya aka yi maki ba, da baki nuna mata kiyayar ba ai da ba zan zo na fada ba, ko kin ga na maki kage a nan ne? Maman risala da itama ta harzuka ta fada har tana cire hannun yar uwarta dake mayar da ita baya dan bata so ko kadan Maman risalar ta zubar da mutuncinta a idannuwan sirikinta, duda aikin gama ya gama sunne basu sani ba, a hausa ai ba'a haka, bahaushe da kunya da kara aka sanshi ba shirme ba
Rai bace ta ce" Dan Allah adda ki daina turani haba dan Allah, ita komai ya tashi sai ta wani nemi ta wulakanta mutane , ai nima ba yar talaka bace bale a zageni da arziki, ita yarinyar da kika tsana din ai dan yar mai datin hula ce, ko karya aka yi? Kema da bakinki kin ce jikanki ba zai zauna da mai tuyar waina tana bi kwararo kwararo da ƴaƴan shegu a hannunta ba, shine yanzu zaki wani hade kai da ita a cutar min ya? Ba zai yiwu ba tunda aka fara haka Risalar ba zata ga da kyau a wajenki ba, Risala kuwa yar gata ce gaba da baya ba zan bari a wulakanta min yata ina ji ina gani ba, koda banida da shi ba zan yarda abinda kika yiwa wancen ki yiwa yata ba walahi!, Ke risala wuce mu tagi gida wuce min!" Sama sama take maganar danma du wanda bai ji ba ya ji, gaba daya zagin da ta juyewa su Amina da wulakanci tasss kowa ya ji haka kuma sirikinta dake murmushi gaba daya murmushin ya dauke a fatar bakinsa
A nutse ya mike cikin shigar dakakiyar shadarsa ya karaso yana kallonsu
Aa hankali ya ce" am, ku yi hakuri ku koma waje, yanzu ta fito daga asibiti hayaniyar nan ba zata haifar mata da abin alkhairi ba................"
Maman Risala ta tabe baki, bata sake wata muguwar maganar ba dan ko HAJIAR gaba daya bakinta a mace tana kallonsu ne
Maman Risala ta sake lekowa ta ce" Ke wai ba da ke nake ba dan kutumar ubanki?"
Risala ta juyo ifannuwanta sun cika da kwallah ta fara taku daya biyu ta tsinkayi muryarsa a dakensa ya ce" Idan kika fita daga get din gidana a yau ba tare da izinina ba na yanke igiyoyin aurena dake kanki"
A haukace ta ci birki tana juyowa ta kalle shi idannuwanta na firfitowa waje
Haka mahaifiyarta da yar uwarta, haka hajia ta juyo tana kallonsa zuciyarta na karra tsintsinkewa
Bakinta na rawa ta ringa nuna kanta, da shi tana son furta wani abin ama ta rasa mene
Mahaifiyarta ta sake shaka ta saka hannunta ta fardota tana fadin" Sai me, ai mai kyai baya tsawa , wuce mu je Alhamdulilah ba ciki bs goyo bale abin duniya ya isheni, menene a auren da ya wuce cusa bakin ciki da kaskantar da mutun da darajarsa da komai? Wuce mu je zaki samu sama da shi a komai, ai ba shi bane autan maza a duniya!"
Janyo hannun yar take yi , yar na tirjewa
Da karfi ta sake juyo da ita dan ta fuskanci kamar bata jinta, sai dai abinda y'ar ta yi ya sakata zuba mata ido, domin hannunta ne ta janye a hankali hawaye na zubowa yana neman bata kwaliyar da idan biya ne zasu yi a yi mata zasu iya kwararar dubu hamsin
A hankali ta ce" Risa, mu tafi mana kar rana ta yi zafi ta taba maki fata kin ji?"
A hankali Risala ta langwabar da kanta tana kallon Mamanta
ABDUL kuwa ya kama hannun Hajia da ta zama tamkar gunki ya shige ciki da ita, direct dakin Fido domin ya kula tana da bukatar dan kadaicewa ko yayane
A hankali Maman Risala, dan kar su Amina su jiyota ta ce " Me kike nufi da dakatawa a nan bayan kina gannin wulakancin da ake mana , ni uwarki da ke din kanki?"
Risala ta fashe da kukan da take rikewa ta kasa yin magana
Mamanta ta zarro idannuwanta tana nuna kanta ta ce" Risa, risa namiji zaki zaba a kaina?"
Da sauri ta girgiza kanta tana kallon mamanta ta ce" Aa mama, ba maganar na zabeshi bane mama, mama a shekara ashirin da takwas na same shi, na so shi, ya so ni, mun yi aure, yanzu na kai ashirin da tara a duniya, idan har ba zanen kadara ta fitar da ni ba zaki so na dawo na sake maki wani zaman? Mama banida matsala da shi, ban rasa komai ba, kema kin san a aurena zuwa yanzu na tara abinda ban tara ba kafin auren nawa......., Mama kakarsa ce, itace mamansa, itace duniyarsa, idan tana fada s kansa bana gannin laifinta, kamar kece da mu fa.........
, Mama, babar matsalarma ina son shi, mama ina son mijina, idan na biki muka tafi na dawo ina neman saka kanmu a uku baki dayanmu fa? Dan na tabata wata rana sai na tarda ABDUL, idan yau ya koreni, gobe ya koreni, jibi ya koreni, wata rana ina iya samun galaba a kansa, ina iya sakashi a uku, uwa uba na saka kaina...Mama ribar me zaki ci?....."
Dau mahaifiyarta ta dauketa da wani mahaukacin Mari tna nunata da yatsarta ta ce" Ni zaki watsawa kasa a ido a kan Kato?"
Risala da ta duke tana kuka tana girgiza kai, yayar mahaifiyarta na rike mahaifiyar tata har suka janyeta suka fita da ita a falon Amina sannan ta mike da gudu itama ta fita ta nufi bangarenta tana cire abubuwan kwaliyar da aka bata lokaci ana mata dan ta yi kira ta sanar kishiyarta ta haihu , mahaifiyarta ta zabo mata leshen dake da kyau da tsafa aka caka mata dauri, ama abin ya kare a haka? Yanzu yau ita da mahaifiyarta ne wannan abu ya faru? Ina zata shiga da ranta? Shin ABDUL da mamanta wane zata zaba? Idan ta yarda ta zabi Abdul din ya wulakantata da gaske fa? Shin yaya zata yi da rayuwarta?
Wayarta ta dauka ta ringa kiran mahaifinta, sai dai ya fada mata yana cikin aiki, da zarar ya zauna zasu yi magana, a dole ta kashe ta ci gaba da kukanta, domin an saba mata tana samun damuwa takan yi kiran mamanta ne ta zo inda take, ama a yau da maman nata ne damuwar a dole ta rasa inda zata saka kanta
____________________&__
A cikin daki,
Tunda ya zaunar da ita ya fice ya je ya samo mata ruwa mai dan sanyi sannan ya dawo ta wajen su Firdausi dake zaune jigum jigum yana dan murmushi ya ce" Sorry an mata mun shiga dakin cen dan lokaci?"
Fido ta yi murmushi tana fadin" Dady mu da muke nan muna dan hirarmuma"
Shima ya yi murmushin ya kalli Amina kkasa kasa ya ce" Sun sha?"
Manyan idannuwanta ta dago ta dora saman fuskarsa, a hankali ta dan masu kasa kasa sai kuma ta mayyar bakin hanyar da Fido ta bi dan basu waje
Murmushi ya yi ya sake fadin" kins da kyau, jan ajin kuma ya amsheki Hajiar ABDUL"
Yanzuma baki ta dan tabe bata ce masa komai ba har yaa mike ya nufi ciki yana jin dan damuwa na rashin kulashin da take yi
A hankali ya zubawa HAJIA bayan ya bude ya mika mata sannan shima ya zauna a gefenta ya yi shiru yana sauraron hucin dake fita daga bakinta
A hankali Hajia ta sauke numfashi tana girgiza kanta ta ce" Ka san a duniya, babu wulakantace sai wanda ya wulakanta kansa ta hanyar daukan duniyar nan a wani abu mai dorewa, bayan tunda aka haifeka kake gannin jariri, yaro, saurayi, mai aure, uba, tsoho, mace ko namiji na mutuwa sunna zuwa wajen da ba'a katse rayuwar sai dai ka yi ta girban abinda ka shuka na dindindin, ama a haka muke manta komai muna aikata abubuwan da suka fi karfin kawunnanmua........"
ABDUL ya sake dubanta a hankali ya ce" Daj Adam din kennan, alkhairinsa ya kasance mai rokon gafarar ubangijinsa sannan ya tuba da gaskiya da daukar niyar ba zai kuma maimaita laifin da ya aikata ba"