Sashe 35
Ni Zan Ladabi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A tausashe ya ce" To ke kuwa wace irin mace ce za'a maki kishiya kike taya roko? Bakya kishi irin na mata ko kuwa Mai shanun birnin ne bakya so?"
Kunya ce ta kamata, dan walahi baba har wani kasa kasa yake maganar da wani salo na tsokana irin na jika da kakansan nan, dama sun saba irin haka tsakaninsu sukan sha hira , dan dai a da yakan yi ta tsokanar ne ita kuma kanta a kasa tana murmushi da jin kunya, ama a yanzu ita ke ta magana dan tana so a saurareta
Salamarsa a cen cikin makoshi kasa kasa da shigowar daya daga cikin masu aikinsa ya kawo kayan marmari na anfanin gonarsa da ya je kaya kaya ana ajiyewa ana sake shigo da wasu ya saka Baba kallonsa da fadin" Dan halak ya ki ambato, kai dan ka ga ina hira da amarsun ne ka wani diro kana huci? Yaro sha kuruminka ni da uman biyu mutu ka raba"
Dan satar kallon gefen da take zaune ya yi kadan, sannan ya dauke kansa ya maida wajen Hasan da ya mike yana murmushi yana kallonsa, ama bai karasa wajensa ba, jira yake yi har ya ga fuskar yin hakan, duda rabonsa da shi da dadin rai suka rabu, ama shi din ba irin yaren nan bane masu shegen zakuwa da nacin abu ba, dan uwansa kuwa tuni ya labe a jikin babarsa dan shi tsoronsa yake ji
Hannunsa na dama ya mika masa , hakan ya sa ya karaso inda yake tsaye ya saka hannunsa cikin nasa
Basu yiwa junna magana ba, ama a hankali da hannayensu dake cikin na junna ya dan matsa kadan shima ya dan matsa nasa hannun , daga haka ya wadatar
Cen gefe ya karasa ya zauna yana karra kallon sumar yaron, daidai lokacin da baba ke fadin" Lalle, hali da hali, Uman biyu wai kin ga mijinki da yaronki kuwa?"
A tare suka kalli Baban, sai kuma suka kalli junna
Wata hararar tsinin ido ta maka masa ta turo baki hadi da dauke kai, shi kuwa ya girgiza kansa a dan takaice ya dubi baban yana fadin" Na sameka lafiya?"
Baba ya ce" Gani kuwa garas muna zantawa da uman biyu, kai ka yi mata nasiha ta san ciwon kanta da kishi irin na mata, wai ace uman biyu ke min maganar kun tsayar da maganar a karo mata abokiyar zama? Ko tarewarku fa ba'a yi ba, uwa uba ta dage wai karshen watan nan dan sun shirya dangin amaryar? Jama'a ni kam ka bani sirrin nan na aikatawa Hajia ko za'a dace, dan inaga da na gwada aure nan da shekara ashirin da hudu ta kusan wata a asibiti!"
Sai da baba ya dire maganarsa, sannan ya sake kallon ABDUL da son gane yana sauraronsa kuwa? Kuma da son gane ainahin maganar uman biyu
A hankali ta ciciba ta mike daga zaunen da take dan karara baba ke so ta dauke fuskar yaron nan da mari ta shiga uku, yaya zai ringa abu kamar na neman rigima ne? Ina hadinta da yaron nan?
"KE DAWO NAN KI ZAUNA" ya fada a dake bayan ya mata kallo daya ya gane nufinta tafia ce zata yi bayan ta dauko maganar da shi bai san yaushe suka yi ba?
Lah ha ila ha ilalahu muhamadu Rasulullah salalahu alaihi Wasallam ku kirawo hajia ABDUL zai ballo mata ruwa jama'a 😖😖😖😖😖😖😖😖😖😖
*NZL PAGE2️⃣1️⃣*
A hankali ta juyo ta sauke dubanta a kansa, kai innalilahi walahi walahi jama'a da ita yake, subahanalah me yake yawo a kan yaron nan ne wai? Menene wannan lamarin na zubar da kima haka?
A kaikaice ta sake dauke shi da hararar da tsaf Baba ya gani, haka kuma ya saka shi boye murmushi ya gyara zamansa tsaf yana son gannin karshen wasansu, dan ya tabata sunna daf da falasa kansu a wajen nan
Juyawa ta yi da niyar sake yin tafiyarta dan ita ai ba sa'ar yara kanana bace
A nutse Baba ya ce" Uman biyu mijinki yace ki dawo ki zauna fa"
Innalilahi wa inna ilaihi rajune, inama zata iya fashewa da kuka a wajen nan? Da ta yi kuka har kamar zata haukace
Wai mijinki, wannan kalma na tsaye mata a wuyanta kamar zata kumeta ta sumar da ita
Jiki a mace ta dawo ta zauna tana sake sada kanta tana hadiye bacin ranta
"Ke baki iya gaisar da mutane bane?" Ya sake fada , dan kawai fitsarar yarinyar dariya take bashi, yauma kuwa warin nan na abin nan take yi dan gayanan a hannayenta , ko menene anfaninsa? Bai taba haduwa da ita ba bata wari, bau san menene take kwabawa jikinta ba sam!
Idannuwanta da suka cika da kwala ta dago ta zuba a saman fuskarsa, numfashi ta ja tana fitar da kyatu ta dantse lebenta na kasa dan bata so ta fashe da ihun kuka
Baba kansa dariya ke tikarsa, sosai abin ke titikarsa a ransa, gaba daya sai suka zamto wani nishadi nasa na sasafe, dan haka da kula yace "Uman biyu baki ji ba?"
Amina ta sake kallon Baba, sai kawai ga hawaye tarrr ta bude bakinta ta ce" Baba wai na gaishe fa yake cewa fa?"
Baba ya yi murmushi yana fadin" Eh haka, to ba shine gaba ba?"
Kai kawai ta soke tana hakin kukanta
Baba ya sake yin murmushi a hankali yace" Allah shi kyauta"
Hijabinta ta saka tana dan goge hawayenta a hankali dan dagowar da ta yi ta ga Hasan ya kura mata ido so yake ya gane kuka take yi ko me? Idan kuwa ya gane haka ta san shima zata daga masa hankali
Danta kuwa tuni ya yi waje, shifa mutumen nan da baya dariya ba tafiyarsu daya ba gaskiya, dan shi baya son bulala
Baba ya sake yin murmushi gannin wani sirri da ya gani gannin idannuwansa a cikin lamarin
Kai ya gyada ya ki yin lididddigar da ya yi niya
Da kula ya ce" Yaushe kuka tsayar da mijin naki za'a tura maganar auren? Sannan yaushema kika ce za'a saka ranar daurin auren?"
A hankali ta dab karra satar kallon yaron, ita baban takaicinta kar ya yi mata wata fasarar daban
Ajiyar zuciya ta sauke ta sake maimaita masa abinda Hajia ta tsara mata
Baba ya dubi ABDUL RA'UF ya ga shima shi yake kallo, so yake ya gani wai hala da gasken sai da ta roka zai yarda? Kai ama kuwa da ya sha mamakin baban, yaushe ya saka wata a wajen da yake da power ne? Lalle da an wulakanta shi shi kam!
Kai ya gyada ya ce" Allah ya nuna mana, zamu je ni da Rabi'u, sannan za'a saka yadda kuke so, maganar tarewarku ne ban ji ba"
Da dan sauri Amina na yiwa ABDUL kallon kasa kasa da turo baki ta ce" Wannan ai mun fi so idan aka daura natan sai mu tare baki daya Baba"
Shiru ya ratsa wajen, na lokaci mai dan tsayi, domin Baban kawai kallonsu yake yi
"Uhum" ya fada a cikin makoshinsa
'idan da raina ta yiwu na raba abin kunya' ya ayyana a zuciyarsa
"Allah ya doramu a kan daidai, tashi ki bashi ruwa sai ki koma ki gama tuyarki na san Lauratun na cen tana fama da rigimar gaz, gaskiya Hauwa bata kyauta min ba, ai sai ta bari a min abina a itacen kamar yadda aka saba wai kar garu su dauki bakin hayaki, in ba Hauwa ba shekarar ginnin nan nawa? Itama dake namalakiyar ginnin bata ga ta yi furfura ba balle wai garu? Gaskiya Abdallahi ka yi mata magana ni kam in dai Uman biyu na nan du juma'a a toyan wainata da itace"
Ruwan ta zuba ta kai daga cen barin dan so take ta yi masa maganar da bata so sai an jima dan gudun mantuwa ko ya bar gidanma bata sani ba
Kasa kasa sosai bayan ta ajiye ruwan ta ce" Kake wani ce min ke zo nan gaskiya bana so kar a maimaita, kuma da kaji ana wata maganar daban nima so nake na yadda kwalon mangwaro na huta da kuda, Allah ya sa baka mance hausa ba!"
Ajiye ruwan ta yi ta mike ta yi gaba
Da ido ya rakata har ta bacewa ganninsa, ya dawo da dubansa Kan Baba domin shi yana kallonta ne shi kuma Baban na kallonsa
A hankali ya ce" Tana fama da yarinta sosai yarinyar nan"
Baba ya yi dariya harda dan kama haba ya ce" Ka ji da shi Abdallah"
Shima murmushin ya yi ya karra duban kan Hasan ya ce" Inaga zamu je aski mu dawo kafin mu tafi masalaci da yaren nan"
Wani farin ciki ya lulube zuciyar Baba, ya san cewa ABDUL zai kula yaran nan ne dan sun shiga ransa ba dan wani abu da yake da burin ginawa ko kulawa da uwarsu ba, dadin da ya ji shine Halayar ABDUL din kwata kwata sun yi nisa da na sangartacen yaro da kudi, halinsa na datako na sakashi a nishadi da kwonciyar hankali, ya tabata idan har suka samu sasantawa da Uman biyu sai ya fi kowa farin cikin hakan
Sai dai tsoro kan kama shi
Ya kula Uman biyun ma fa bata son hadin nan, domin a yadda ta yi wani abin kamar wace ba zuciya a kirjinta na kishi? Kishi ai halal ne, shi da kansa ABDUL din ya kula ya yi mamakin abin
Salamarsa Abdul din ya yi suka fice, wanda Husain ya ki binsu sai da baba direba sannan ya shiga motar yana labe a jikin Baban yana hangen ABDUL da ya hade gabas da yama ya wani yi zama a hakimce cikin lalausan milk color din yadi yana wani basarwa irin na masu kudi
Shi kuwa Hasan a haka ya ga wajen zama, dan kuwa shima ya yi zaman ne ya wani dauke kai yana kallon titi kamar wanda ya jima yana shuga mota, bayan ko kwarewa da bude motar basu yi ba, to a cenma su yan yawace yawacensu da mamansu a adaidaita sahu ne, bale a yanzu
____________________________________
Dukkan yadda suka yi da Baba ta sanarwa Hajia a yanzu da ta fito tsaf cikin lalausan shirinta da nufin tafia gidan yar uwarta
Kunya ce ta kamata, dan walahi baba har wani kasa kasa yake maganar da wani salo na tsokana irin na jika da kakansan nan, dama sun saba irin haka tsakaninsu sukan sha hira , dan dai a da yakan yi ta tsokanar ne ita kuma kanta a kasa tana murmushi da jin kunya, ama a yanzu ita ke ta magana dan tana so a saurareta
Salamarsa a cen cikin makoshi kasa kasa da shigowar daya daga cikin masu aikinsa ya kawo kayan marmari na anfanin gonarsa da ya je kaya kaya ana ajiyewa ana sake shigo da wasu ya saka Baba kallonsa da fadin" Dan halak ya ki ambato, kai dan ka ga ina hira da amarsun ne ka wani diro kana huci? Yaro sha kuruminka ni da uman biyu mutu ka raba"
Dan satar kallon gefen da take zaune ya yi kadan, sannan ya dauke kansa ya maida wajen Hasan da ya mike yana murmushi yana kallonsa, ama bai karasa wajensa ba, jira yake yi har ya ga fuskar yin hakan, duda rabonsa da shi da dadin rai suka rabu, ama shi din ba irin yaren nan bane masu shegen zakuwa da nacin abu ba, dan uwansa kuwa tuni ya labe a jikin babarsa dan shi tsoronsa yake ji
Hannunsa na dama ya mika masa , hakan ya sa ya karaso inda yake tsaye ya saka hannunsa cikin nasa
Basu yiwa junna magana ba, ama a hankali da hannayensu dake cikin na junna ya dan matsa kadan shima ya dan matsa nasa hannun , daga haka ya wadatar
Cen gefe ya karasa ya zauna yana karra kallon sumar yaron, daidai lokacin da baba ke fadin" Lalle, hali da hali, Uman biyu wai kin ga mijinki da yaronki kuwa?"
A tare suka kalli Baban, sai kuma suka kalli junna
Wata hararar tsinin ido ta maka masa ta turo baki hadi da dauke kai, shi kuwa ya girgiza kansa a dan takaice ya dubi baban yana fadin" Na sameka lafiya?"
Baba ya ce" Gani kuwa garas muna zantawa da uman biyu, kai ka yi mata nasiha ta san ciwon kanta da kishi irin na mata, wai ace uman biyu ke min maganar kun tsayar da maganar a karo mata abokiyar zama? Ko tarewarku fa ba'a yi ba, uwa uba ta dage wai karshen watan nan dan sun shirya dangin amaryar? Jama'a ni kam ka bani sirrin nan na aikatawa Hajia ko za'a dace, dan inaga da na gwada aure nan da shekara ashirin da hudu ta kusan wata a asibiti!"
Sai da baba ya dire maganarsa, sannan ya sake kallon ABDUL da son gane yana sauraronsa kuwa? Kuma da son gane ainahin maganar uman biyu
A hankali ta ciciba ta mike daga zaunen da take dan karara baba ke so ta dauke fuskar yaron nan da mari ta shiga uku, yaya zai ringa abu kamar na neman rigima ne? Ina hadinta da yaron nan?
"KE DAWO NAN KI ZAUNA" ya fada a dake bayan ya mata kallo daya ya gane nufinta tafia ce zata yi bayan ta dauko maganar da shi bai san yaushe suka yi ba?
Lah ha ila ha ilalahu muhamadu Rasulullah salalahu alaihi Wasallam ku kirawo hajia ABDUL zai ballo mata ruwa jama'a 😖😖😖😖😖😖😖😖😖😖
*NZL PAGE2️⃣1️⃣*
A hankali ta juyo ta sauke dubanta a kansa, kai innalilahi walahi walahi jama'a da ita yake, subahanalah me yake yawo a kan yaron nan ne wai? Menene wannan lamarin na zubar da kima haka?
A kaikaice ta sake dauke shi da hararar da tsaf Baba ya gani, haka kuma ya saka shi boye murmushi ya gyara zamansa tsaf yana son gannin karshen wasansu, dan ya tabata sunna daf da falasa kansu a wajen nan
Juyawa ta yi da niyar sake yin tafiyarta dan ita ai ba sa'ar yara kanana bace
A nutse Baba ya ce" Uman biyu mijinki yace ki dawo ki zauna fa"
Innalilahi wa inna ilaihi rajune, inama zata iya fashewa da kuka a wajen nan? Da ta yi kuka har kamar zata haukace
Wai mijinki, wannan kalma na tsaye mata a wuyanta kamar zata kumeta ta sumar da ita
Jiki a mace ta dawo ta zauna tana sake sada kanta tana hadiye bacin ranta
"Ke baki iya gaisar da mutane bane?" Ya sake fada , dan kawai fitsarar yarinyar dariya take bashi, yauma kuwa warin nan na abin nan take yi dan gayanan a hannayenta , ko menene anfaninsa? Bai taba haduwa da ita ba bata wari, bau san menene take kwabawa jikinta ba sam!
Idannuwanta da suka cika da kwala ta dago ta zuba a saman fuskarsa, numfashi ta ja tana fitar da kyatu ta dantse lebenta na kasa dan bata so ta fashe da ihun kuka
Baba kansa dariya ke tikarsa, sosai abin ke titikarsa a ransa, gaba daya sai suka zamto wani nishadi nasa na sasafe, dan haka da kula yace "Uman biyu baki ji ba?"
Amina ta sake kallon Baba, sai kawai ga hawaye tarrr ta bude bakinta ta ce" Baba wai na gaishe fa yake cewa fa?"
Baba ya yi murmushi yana fadin" Eh haka, to ba shine gaba ba?"
Kai kawai ta soke tana hakin kukanta
Baba ya sake yin murmushi a hankali yace" Allah shi kyauta"
Hijabinta ta saka tana dan goge hawayenta a hankali dan dagowar da ta yi ta ga Hasan ya kura mata ido so yake ya gane kuka take yi ko me? Idan kuwa ya gane haka ta san shima zata daga masa hankali
Danta kuwa tuni ya yi waje, shifa mutumen nan da baya dariya ba tafiyarsu daya ba gaskiya, dan shi baya son bulala
Baba ya sake yin murmushi gannin wani sirri da ya gani gannin idannuwansa a cikin lamarin
Kai ya gyada ya ki yin lididddigar da ya yi niya
Da kula ya ce" Yaushe kuka tsayar da mijin naki za'a tura maganar auren? Sannan yaushema kika ce za'a saka ranar daurin auren?"
A hankali ta dab karra satar kallon yaron, ita baban takaicinta kar ya yi mata wata fasarar daban
Ajiyar zuciya ta sauke ta sake maimaita masa abinda Hajia ta tsara mata
Baba ya dubi ABDUL RA'UF ya ga shima shi yake kallo, so yake ya gani wai hala da gasken sai da ta roka zai yarda? Kai ama kuwa da ya sha mamakin baban, yaushe ya saka wata a wajen da yake da power ne? Lalle da an wulakanta shi shi kam!
Kai ya gyada ya ce" Allah ya nuna mana, zamu je ni da Rabi'u, sannan za'a saka yadda kuke so, maganar tarewarku ne ban ji ba"
Da dan sauri Amina na yiwa ABDUL kallon kasa kasa da turo baki ta ce" Wannan ai mun fi so idan aka daura natan sai mu tare baki daya Baba"
Shiru ya ratsa wajen, na lokaci mai dan tsayi, domin Baban kawai kallonsu yake yi
"Uhum" ya fada a cikin makoshinsa
'idan da raina ta yiwu na raba abin kunya' ya ayyana a zuciyarsa
"Allah ya doramu a kan daidai, tashi ki bashi ruwa sai ki koma ki gama tuyarki na san Lauratun na cen tana fama da rigimar gaz, gaskiya Hauwa bata kyauta min ba, ai sai ta bari a min abina a itacen kamar yadda aka saba wai kar garu su dauki bakin hayaki, in ba Hauwa ba shekarar ginnin nan nawa? Itama dake namalakiyar ginnin bata ga ta yi furfura ba balle wai garu? Gaskiya Abdallahi ka yi mata magana ni kam in dai Uman biyu na nan du juma'a a toyan wainata da itace"
Ruwan ta zuba ta kai daga cen barin dan so take ta yi masa maganar da bata so sai an jima dan gudun mantuwa ko ya bar gidanma bata sani ba
Kasa kasa sosai bayan ta ajiye ruwan ta ce" Kake wani ce min ke zo nan gaskiya bana so kar a maimaita, kuma da kaji ana wata maganar daban nima so nake na yadda kwalon mangwaro na huta da kuda, Allah ya sa baka mance hausa ba!"
Ajiye ruwan ta yi ta mike ta yi gaba
Da ido ya rakata har ta bacewa ganninsa, ya dawo da dubansa Kan Baba domin shi yana kallonta ne shi kuma Baban na kallonsa
A hankali ya ce" Tana fama da yarinta sosai yarinyar nan"
Baba ya yi dariya harda dan kama haba ya ce" Ka ji da shi Abdallah"
Shima murmushin ya yi ya karra duban kan Hasan ya ce" Inaga zamu je aski mu dawo kafin mu tafi masalaci da yaren nan"
Wani farin ciki ya lulube zuciyar Baba, ya san cewa ABDUL zai kula yaran nan ne dan sun shiga ransa ba dan wani abu da yake da burin ginawa ko kulawa da uwarsu ba, dadin da ya ji shine Halayar ABDUL din kwata kwata sun yi nisa da na sangartacen yaro da kudi, halinsa na datako na sakashi a nishadi da kwonciyar hankali, ya tabata idan har suka samu sasantawa da Uman biyu sai ya fi kowa farin cikin hakan
Sai dai tsoro kan kama shi
Ya kula Uman biyun ma fa bata son hadin nan, domin a yadda ta yi wani abin kamar wace ba zuciya a kirjinta na kishi? Kishi ai halal ne, shi da kansa ABDUL din ya kula ya yi mamakin abin
Salamarsa Abdul din ya yi suka fice, wanda Husain ya ki binsu sai da baba direba sannan ya shiga motar yana labe a jikin Baban yana hangen ABDUL da ya hade gabas da yama ya wani yi zama a hakimce cikin lalausan milk color din yadi yana wani basarwa irin na masu kudi
Shi kuwa Hasan a haka ya ga wajen zama, dan kuwa shima ya yi zaman ne ya wani dauke kai yana kallon titi kamar wanda ya jima yana shuga mota, bayan ko kwarewa da bude motar basu yi ba, to a cenma su yan yawace yawacensu da mamansu a adaidaita sahu ne, bale a yanzu
____________________________________
Dukkan yadda suka yi da Baba ta sanarwa Hajia a yanzu da ta fito tsaf cikin lalausan shirinta da nufin tafia gidan yar uwarta