Sashe 78
Ni Zan Ladabi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ido Abdul ya lumshe yana jinginar da bayansa a jikin motar yana hangen kakaninsa da suka nufi dakinta kowane na saurin da Allah ya bashi ikon yi
Gaba dayansu a rikice suke a kusa da ita
A fitarsu har Fido ta yi kiran baba Lauratu dan ta ji ko gidanta ta tafi? Babar ta zo itama hankali tashe suka sake komawa dakinta a nan suka sameta a labe bayan sif jikinta na bari hankalinta du ba a jikinta ba, furucin bakinta shine ya sawake mata, ba zata iya ba, kasheta yake so ya yi ne? Ta gaji da wulakancinsa, ta gaji da komai da yake mata na wulakanci a rayuwa, ya barta ta tafi inda za'a san darajarta, tunda ba sonta yake yi ba, yana kiranta da AUnty!
Hankali tashe Hajia ta karasa tana duban Baba dake gurfane tana sake dafata ta ce" Wai a kan gwuiwa take ne?"
Baba ta gyada kai tana fadin" Haka muka sameta a kan gwuiwa take, inaga an sanar mata cewa an kashe yar gidan babansu ne a dakin saurayinta, kuma gongonsu da ta ga gawar itama ta rasu, shine kuma ya hadu da wani rikicin na Uman mallan"
Baba ya ringa kama sunnan Allah yana salatin Annabi Muhammadu Rasulullah salalahu alaihi wa salam yana gannin abin ya lafa mata tana sauke numfashi ya ce" Ni kam abin nan ya fara damuna, Uman biyu sannu kin ji? Allah ya raba lafiya, an zarce wata takwas abu ya isa haihuwa kam bale haihuwar fari, kin ga mijin fa da ya rikice har hatsari ya samu "
A gigice ta dago fuskarta jin abinda Baba ya ce
Hajia kuwa ta kalli Baba bayan ta cire hijabinta tana kiran docter ta ce" Haba alkali ya yaka kuma?"
Amina kuwa daga zaunen sai gata ta ciciba ta mike tsaye , Fido da baba na tareta ama faman sumewa take yi
Tana kallon Firdausi muryarta na rawa, daidai Abdul ya shigo a hankali dan kar ya yi hayaniya aje bata son ganninsa ya karra rikitata ta ce" Firdausi, Ab Ab Aban biyu ne ya yi hatsarin? Fido yana ina? Innalilahi wa inna ilaihi rajune..........."
Ta idasa fadi tana daf da idasa zubewa dan gaba daya kafarta ta nemi gaza daukanta
Da fido da Baba sun saka iya karfinsu dan talabeta, Haka hajia dake amsa kiran Docter tana fada mata sosai abin ya matso itama ta karaso ta talaba....uwa uba mai gaya mai tafiar shi ya fi kowa talabota a jikinsa a hankali ya zauna da ita a jikinsa yana ci gaba da shafa bayanta a hankali yana kallon yadda du ta rikice ya kama hijabinta ya ja ya cire mata shi domin du ya jika da zufa haka kuma ya janye ribom din dake kanta ya kasance gashin kanta ya saku ko zata ji saukin zafin nan, ya kai dubansa kan Fido da suka sakjar masa kuma suka kawar da dubansu yana fadin" Karra mana ACn cen Fido, kuma ki bude min dakin cen na ga idan zata iya zaman mota mu wuce asibiti ,......Hajia kirayi numbar Mansur plz ki sanar masa" ya idasa yana kallon Hajiar dake ta kai kawo kamar wace ke shirrin kwasawa da gudu, du ta rikice abinta kamar itace mai nakudar
Da sauri ta shiga lalubar number Mansur din tana buga masa kira
Baba kuwa kofi ya zuba ruwa masu dan dumi kadan ya zauna yana tofa Adu'a
A hankali ta kwontar da kanta saman kirjinsa dan hakan shine baban abinda ta ji tana bukata a zuciyarta
A hankali ya ci gaba fa shafa bayanta yana shafawa a hankali ya ce" Amina? Zaki taimaka min mu shiga cikin dakin cen na duba ki? Plz zaki iya?"
Amina dake galabaice tana sauke ajiyar zuciya a hankali ta dago idannuwanta tana kallon fuskarsa
Muryarta a raunane ta ce" ABDUL, wai nice auntyn ko?"
ABDUL ya zunawa fuskarta ido, shi kam idan za'a nada sarakan rikici na duniya zai fara bada sunnan Mina, bashida tantama ita zata ci walahi
A hankali ya girgiza kansa, dan bai san eh ko aa zai ce ba, hasalima bai san fadin sunnan take so ko kar a fadi ba
Numfashi ta ja tana sake maida kanta saman kirjinsa a sanyaye ta ce" Haka kake ce min aunty mana, kai ga mai yar yarinya mana, Abdul baba yace ka yi hatsari? Ka ji ciwo ne?"
Wata irin bugwa da zuciyarsa ke yi, da Amina ta sani, da ta bi shi a hankali kar ta halaka shi
A hankali ya mike ya samu ya dagota da taimakon Hajia sannan suka kaita dakin
Daga kofa hajia ta koma ta tsaya tana ta zufa, ita kam ta fi kowa rikicewa, kuma a yanzu kam haushin Honorable take ji, me yasa shi ba zai yi hakuri ba ko me ta masa ne sai ya ringa nemanta da rigima ne? Haba dan Allah
Da kyar ya lalabata ta yarda ya dubata,
Ai kam nakuda take yi sosai da sosai, ama idan suka maida hankali zata haihu a asibiti
Cikin gagawa yake bada umarnin maza a hada kayan haihuwa, maza a yi kaza a yi kaza, sannan suka kamata suka sakata a mota Muhammat ya ja suka nufi asibiti a lokacin dare ya tsala sosai aka bar Bab lauratu da tsaron Biyu, domin Fido kasa zama ta yi ta shige motar su Baba mai Shanu
A asibitinma gwagwarmayar ake sha, fama take baiwar Allah, nakuda sai sake nuna take ga likitoci a zagaye da ita
A hankali bakin rikicin da mita ya mutu , ta dawo sai ido sai adu'ar da take yi a cikin zuciyarta
Bata taba gannin namiji a hausa, a dakin haihuwar mace ba sai a kanta,
Mijinta na zaune rike da hannunta a lokacin da ta zo kan gaba haihuwarta ta salamo gabanin asubahi, domin haihuwar sai da asubahi ta sanyi kai sannan ta samu ta sulube ƴaƴanta kwaya biyu, mace da namiji
Yayan ake gogewa dan dora mata su a saman cikinta kamar yadda aka saba, ita kuma tana sake rintse ido da maida numfashin jin kamar an cire mata kaya zafin radafin na tafia yana barinta
Jikin ABDUL gaba daya rawa yake, ya rasa yayan zai kalla, ko ita dake damke da hannunsa bata saki ba?
A hankali ya rankwafo saman kanta yana shinshinar dukkan inda hancinsa ya kai, bama kamar wajen idannuwanta, da su hancinta, da sauransu, sai sinsina yake hannayenta cikin nasa a hankali yana kama sunnanta har ta bude idannuwanta tana kallonsa , shima yana kallonta
A hankali ya sauke numfashi mai sanyi a saman fuskarta yana kallonta, muryarsa a bayane ya furta" I love you, I love u so much Minah, i love u, i love u meenah"
Idannuwanta ta lumshe kirjinta na dokawa a hankali tana sauraron yadda yake lashe lebunnanta da suka bushe mata kayau kafin ya kame harshenta a hankali ya ringa tsotsa a yadda yake a rankwafen nan ta saman gadon tamkar zai cinyeta danya
...........
Ido Docter ta zarro tana juyawa daria na kubce mata ta ce" Docter ka bari ta sauka daga saman gadon mana mu kimtsata ka ga mun mika yaren , Hajia kuma so take ta shigo ta ga yannayin jikinta"
Da kyar ya iya barinta yana son jin amsa daga gareta, fuskarta yake kallo yadda idannuwanta ke lumshe
A hankali ya ce" Ba zaki ce min kema kina so na ba?"
Amina ta sake lumshe idannuwanta wani irin abu na ratsa ilahirin jikinta
"Kai yau na ga abu, ABDUL me kake yi haka ne wai? Ka matsa a idasa fitar mata da gudan jinni mana a gani idan da dinki a yi a kimtsata jama'a, wannan haihuwa mai wahala ka tare mata numfashi idan ta summa fa?" Hajia ta fada tana karasowa , a yau harta da rawar nan ta tsofafin da ake janyowaa kiiiii sai da ta yi, kuka kuwa risris ta rusa shi ana bata hakuri, ƴaƴan nan da kyar ta ba alkali da Firdausi, ta rasa ina zata tsoma kanta dan farin ciki, ta rasa me zata ce me zata yi? Ashe Amina itace uwar ƴaƴan jikanta? Biyu? Namiji da mace? Haihuwa da ta masu karanci a familly dinsu? Ai su lamari yana da zafin gaske a zuciyarsu, a yanzu bata san me zata yi na nuna farin cikinta ga yarinyar nan ba, to ita arzikin ya'yan nan ai ya ninka maganar hawa kujerar gwamnati sau million a wajenta
Haka ya saki hannunta ba dan ya so ba ya mike da kyar, domin a rankwafen nan a kadan ya dauki awa biyu, ita na nakuda ne shi yana nishi, kuma sai a yanzu ya ji kamar idan an jima jikinsa tsami zai yi har ya fadawa yan garinsu
Murmushi ya yi bayan ya sake juyowa ya ga yadda Hajia tta shiga taimakawa Docter da nurse din dake kan Amina dan gyarata
Hannunsa ya kai daidai zuciyarsa a hankali ya furta" Allah ka bani ikon haukatata a so na, domin idan abin ya kasance na zuciya daya ne tak, dayar bata ra'ayi, kwarai zan cutu"
Yana fitowa ya ga wani shagalin, Fido na rike da Yar, Maansur na rike da yaron, Ita fido yar take ta karra budewa cikin lulubinta hakoranta a waje tamkar gonar auduga
Shi kuwa yana rungume da ɗan a kirjinsa yana binta du inda ta yi, kuma yana kallonta kamar zai dauke idannuwansa ya lika mata
Baba kuwa ya tafi masalaci domin hawaye ya ringa yi kamar ba baba ba, ya tafi yace ya tafi ya hantse a masalaci ya godewa wanda ya basu,
Tsayawa ya yi yana kure Mansur da kallo, irin kallon nan na kankance idannuwa da dage gira guda ya ce" Kai ya haka?"
Sai da Mansur ya zabura, dan bai san ana kallonsa ba, ya juyo yana rike dan da kyau ya ce" Man ka fito?"
ABDUL ya karra kankamce ido ya karaso yana fadin" Ka ga bani na ga magajin ya ganni, kuma ka dan dawo daga nan bana so ana matsewa y'ayana waje haka, yaya yarinya na kwana kana binta?"
Ido da baki Mansur ya saki yana kallonsa, irin yadda ya sha murr kuwa kai kace baban na Fido ne sak
Fido ta karaso ta kawo masa macenma ya hade yana kallonsu
Gaba dayansu a rikice suke a kusa da ita
A fitarsu har Fido ta yi kiran baba Lauratu dan ta ji ko gidanta ta tafi? Babar ta zo itama hankali tashe suka sake komawa dakinta a nan suka sameta a labe bayan sif jikinta na bari hankalinta du ba a jikinta ba, furucin bakinta shine ya sawake mata, ba zata iya ba, kasheta yake so ya yi ne? Ta gaji da wulakancinsa, ta gaji da komai da yake mata na wulakanci a rayuwa, ya barta ta tafi inda za'a san darajarta, tunda ba sonta yake yi ba, yana kiranta da AUnty!
Hankali tashe Hajia ta karasa tana duban Baba dake gurfane tana sake dafata ta ce" Wai a kan gwuiwa take ne?"
Baba ta gyada kai tana fadin" Haka muka sameta a kan gwuiwa take, inaga an sanar mata cewa an kashe yar gidan babansu ne a dakin saurayinta, kuma gongonsu da ta ga gawar itama ta rasu, shine kuma ya hadu da wani rikicin na Uman mallan"
Baba ya ringa kama sunnan Allah yana salatin Annabi Muhammadu Rasulullah salalahu alaihi wa salam yana gannin abin ya lafa mata tana sauke numfashi ya ce" Ni kam abin nan ya fara damuna, Uman biyu sannu kin ji? Allah ya raba lafiya, an zarce wata takwas abu ya isa haihuwa kam bale haihuwar fari, kin ga mijin fa da ya rikice har hatsari ya samu "
A gigice ta dago fuskarta jin abinda Baba ya ce
Hajia kuwa ta kalli Baba bayan ta cire hijabinta tana kiran docter ta ce" Haba alkali ya yaka kuma?"
Amina kuwa daga zaunen sai gata ta ciciba ta mike tsaye , Fido da baba na tareta ama faman sumewa take yi
Tana kallon Firdausi muryarta na rawa, daidai Abdul ya shigo a hankali dan kar ya yi hayaniya aje bata son ganninsa ya karra rikitata ta ce" Firdausi, Ab Ab Aban biyu ne ya yi hatsarin? Fido yana ina? Innalilahi wa inna ilaihi rajune..........."
Ta idasa fadi tana daf da idasa zubewa dan gaba daya kafarta ta nemi gaza daukanta
Da fido da Baba sun saka iya karfinsu dan talabeta, Haka hajia dake amsa kiran Docter tana fada mata sosai abin ya matso itama ta karaso ta talaba....uwa uba mai gaya mai tafiar shi ya fi kowa talabota a jikinsa a hankali ya zauna da ita a jikinsa yana ci gaba da shafa bayanta a hankali yana kallon yadda du ta rikice ya kama hijabinta ya ja ya cire mata shi domin du ya jika da zufa haka kuma ya janye ribom din dake kanta ya kasance gashin kanta ya saku ko zata ji saukin zafin nan, ya kai dubansa kan Fido da suka sakjar masa kuma suka kawar da dubansu yana fadin" Karra mana ACn cen Fido, kuma ki bude min dakin cen na ga idan zata iya zaman mota mu wuce asibiti ,......Hajia kirayi numbar Mansur plz ki sanar masa" ya idasa yana kallon Hajiar dake ta kai kawo kamar wace ke shirrin kwasawa da gudu, du ta rikice abinta kamar itace mai nakudar
Da sauri ta shiga lalubar number Mansur din tana buga masa kira
Baba kuwa kofi ya zuba ruwa masu dan dumi kadan ya zauna yana tofa Adu'a
A hankali ta kwontar da kanta saman kirjinsa dan hakan shine baban abinda ta ji tana bukata a zuciyarta
A hankali ya ci gaba fa shafa bayanta yana shafawa a hankali ya ce" Amina? Zaki taimaka min mu shiga cikin dakin cen na duba ki? Plz zaki iya?"
Amina dake galabaice tana sauke ajiyar zuciya a hankali ta dago idannuwanta tana kallon fuskarsa
Muryarta a raunane ta ce" ABDUL, wai nice auntyn ko?"
ABDUL ya zunawa fuskarta ido, shi kam idan za'a nada sarakan rikici na duniya zai fara bada sunnan Mina, bashida tantama ita zata ci walahi
A hankali ya girgiza kansa, dan bai san eh ko aa zai ce ba, hasalima bai san fadin sunnan take so ko kar a fadi ba
Numfashi ta ja tana sake maida kanta saman kirjinsa a sanyaye ta ce" Haka kake ce min aunty mana, kai ga mai yar yarinya mana, Abdul baba yace ka yi hatsari? Ka ji ciwo ne?"
Wata irin bugwa da zuciyarsa ke yi, da Amina ta sani, da ta bi shi a hankali kar ta halaka shi
A hankali ya mike ya samu ya dagota da taimakon Hajia sannan suka kaita dakin
Daga kofa hajia ta koma ta tsaya tana ta zufa, ita kam ta fi kowa rikicewa, kuma a yanzu kam haushin Honorable take ji, me yasa shi ba zai yi hakuri ba ko me ta masa ne sai ya ringa nemanta da rigima ne? Haba dan Allah
Da kyar ya lalabata ta yarda ya dubata,
Ai kam nakuda take yi sosai da sosai, ama idan suka maida hankali zata haihu a asibiti
Cikin gagawa yake bada umarnin maza a hada kayan haihuwa, maza a yi kaza a yi kaza, sannan suka kamata suka sakata a mota Muhammat ya ja suka nufi asibiti a lokacin dare ya tsala sosai aka bar Bab lauratu da tsaron Biyu, domin Fido kasa zama ta yi ta shige motar su Baba mai Shanu
A asibitinma gwagwarmayar ake sha, fama take baiwar Allah, nakuda sai sake nuna take ga likitoci a zagaye da ita
A hankali bakin rikicin da mita ya mutu , ta dawo sai ido sai adu'ar da take yi a cikin zuciyarta
Bata taba gannin namiji a hausa, a dakin haihuwar mace ba sai a kanta,
Mijinta na zaune rike da hannunta a lokacin da ta zo kan gaba haihuwarta ta salamo gabanin asubahi, domin haihuwar sai da asubahi ta sanyi kai sannan ta samu ta sulube ƴaƴanta kwaya biyu, mace da namiji
Yayan ake gogewa dan dora mata su a saman cikinta kamar yadda aka saba, ita kuma tana sake rintse ido da maida numfashin jin kamar an cire mata kaya zafin radafin na tafia yana barinta
Jikin ABDUL gaba daya rawa yake, ya rasa yayan zai kalla, ko ita dake damke da hannunsa bata saki ba?
A hankali ya rankwafo saman kanta yana shinshinar dukkan inda hancinsa ya kai, bama kamar wajen idannuwanta, da su hancinta, da sauransu, sai sinsina yake hannayenta cikin nasa a hankali yana kama sunnanta har ta bude idannuwanta tana kallonsa , shima yana kallonta
A hankali ya sauke numfashi mai sanyi a saman fuskarta yana kallonta, muryarsa a bayane ya furta" I love you, I love u so much Minah, i love u, i love u meenah"
Idannuwanta ta lumshe kirjinta na dokawa a hankali tana sauraron yadda yake lashe lebunnanta da suka bushe mata kayau kafin ya kame harshenta a hankali ya ringa tsotsa a yadda yake a rankwafen nan ta saman gadon tamkar zai cinyeta danya
...........
Ido Docter ta zarro tana juyawa daria na kubce mata ta ce" Docter ka bari ta sauka daga saman gadon mana mu kimtsata ka ga mun mika yaren , Hajia kuma so take ta shigo ta ga yannayin jikinta"
Da kyar ya iya barinta yana son jin amsa daga gareta, fuskarta yake kallo yadda idannuwanta ke lumshe
A hankali ya ce" Ba zaki ce min kema kina so na ba?"
Amina ta sake lumshe idannuwanta wani irin abu na ratsa ilahirin jikinta
"Kai yau na ga abu, ABDUL me kake yi haka ne wai? Ka matsa a idasa fitar mata da gudan jinni mana a gani idan da dinki a yi a kimtsata jama'a, wannan haihuwa mai wahala ka tare mata numfashi idan ta summa fa?" Hajia ta fada tana karasowa , a yau harta da rawar nan ta tsofafin da ake janyowaa kiiiii sai da ta yi, kuka kuwa risris ta rusa shi ana bata hakuri, ƴaƴan nan da kyar ta ba alkali da Firdausi, ta rasa ina zata tsoma kanta dan farin ciki, ta rasa me zata ce me zata yi? Ashe Amina itace uwar ƴaƴan jikanta? Biyu? Namiji da mace? Haihuwa da ta masu karanci a familly dinsu? Ai su lamari yana da zafin gaske a zuciyarsu, a yanzu bata san me zata yi na nuna farin cikinta ga yarinyar nan ba, to ita arzikin ya'yan nan ai ya ninka maganar hawa kujerar gwamnati sau million a wajenta
Haka ya saki hannunta ba dan ya so ba ya mike da kyar, domin a rankwafen nan a kadan ya dauki awa biyu, ita na nakuda ne shi yana nishi, kuma sai a yanzu ya ji kamar idan an jima jikinsa tsami zai yi har ya fadawa yan garinsu
Murmushi ya yi bayan ya sake juyowa ya ga yadda Hajia tta shiga taimakawa Docter da nurse din dake kan Amina dan gyarata
Hannunsa ya kai daidai zuciyarsa a hankali ya furta" Allah ka bani ikon haukatata a so na, domin idan abin ya kasance na zuciya daya ne tak, dayar bata ra'ayi, kwarai zan cutu"
Yana fitowa ya ga wani shagalin, Fido na rike da Yar, Maansur na rike da yaron, Ita fido yar take ta karra budewa cikin lulubinta hakoranta a waje tamkar gonar auduga
Shi kuwa yana rungume da ɗan a kirjinsa yana binta du inda ta yi, kuma yana kallonta kamar zai dauke idannuwansa ya lika mata
Baba kuwa ya tafi masalaci domin hawaye ya ringa yi kamar ba baba ba, ya tafi yace ya tafi ya hantse a masalaci ya godewa wanda ya basu,
Tsayawa ya yi yana kure Mansur da kallo, irin kallon nan na kankance idannuwa da dage gira guda ya ce" Kai ya haka?"
Sai da Mansur ya zabura, dan bai san ana kallonsa ba, ya juyo yana rike dan da kyau ya ce" Man ka fito?"
ABDUL ya karra kankamce ido ya karaso yana fadin" Ka ga bani na ga magajin ya ganni, kuma ka dan dawo daga nan bana so ana matsewa y'ayana waje haka, yaya yarinya na kwana kana binta?"
Ido da baki Mansur ya saki yana kallonsa, irin yadda ya sha murr kuwa kai kace baban na Fido ne sak
Fido ta karaso ta kawo masa macenma ya hade yana kallonsu