Sashe 79
Ni Zan Ladabi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Murmushi ya dago yana yi zai yi magana ya sake gannin Mansur Fido yake kallo,
Fuska ya sha ya ce" Kai ba nace ka daina kallon yar ba?"
Mansur ya dube shi yana fadin" Dan Allah wai meye haka? Ba za'a yita ta kare ba?"
Firdausi ta yi gaba da dan sauri, dan bata kaunar abinda ke fitowa daga bakin Docter mai kirki
Sam bata so, bata tunanin idan har tana ra'ayin haka a kurkusan nan
Mansur yaa kai zaune yana fadin" Me ka yi kennan? Haba Man, yaya ba zaka kama min ba bayan ina so?"
ABDUL ya tabe baki ya ce" Yaren nan ka tabata basa bukatar kwalba?"
Da haushi haushi Mansur ya ce" Kai dan Allah ka rufa min asiri, kwalbar me yayan masha Allah babu na kasa da kilo 3?, Ina maka magana ta a bani na raya sunna kana kawar min da zancen?"
ABDUL ya yi murmushi ya ce" Man, sai ka bita a hankali.....idan kace zaka takura ba zaka samu abinda kake so ba.....ka ga tanada tabo na maza a rayuwarta, sai ta gamsu da kai a aikace ba a furucin bakinka ba........so kawai ka yi ta kanka, domin nima ta kaina zan yi da rigimamiyata"
Mansur ya yi murmushi yan saka yaran a irin gadon nan na turawa ya lulube su ya mika masa hannu yana yi masa congratulations
A nan dai suka hantse aka kimtsa Amina sosai aka kaita dakin hutu bayan ta sha dinki aka barta tana hutawa, domin awa shida zata yi a saketa, ta haihu lafiya bata samu matsalolin haihuwa ba sai na kari kadai
Ana dawowa daga masalaci aka mayar da baba gida, ama HAJIA tace aa sai sun je ta daidaita masu harkar Ac da sauransu dan kar a yi wasa a kama masu mura, yaran ta masu hoto fiye da a irga, hawaye kuwa daukewa take yi tana karrawa
ABDUL ya nemi waje zai zauna da jalabiyar nan da suka sha kokowa da komai da ita, HAJIA ta nuna Aa, kawai ya wuce gida gasunnan, ai zuwa karfe goma za'a salameta a fara shirya zuwansu gida
Har ya yi gaba ta sake kiransa ya dawo ya dan zauna yana kallonta
Fuskarta a hade ta ce" ABDUL, matarka bata san y'ar uwarta na asibiti bane?"
ABDUL ya yi dan tsai, sai kuma ya gane inda ta nufa, a nutse ya dan yi yannayi na bai sani ba
Hajia ta tabe baki tana gyada kanta ta ce"
A hankali ta dan gyara rigar barcin dake jikinta, mai hasken fari da mannewa a jiki tana dan son wara idannuwanta dake shanyewa dan kansu tamkar wace ke masu haka da gangan, muryarta a dan shake ta ce" Hi "
Idannuwansa ya lumshe, hannunsa daya a cikin aljihun wandon barcinsa irin budaden nan mai dan kauri mai ruwan blu , watau hasken sararin samaniya, sai rigar ciki singileti da kuma ta sama ta wandon wace bai balla boturan ba haka ya ratso al'uma ya taho , hannunsa daya kuwa a saman kirjinsa yana dan shafawa a hankali, yana son dauke yar damuwar dake tattare da shi wace bata wuce rikicin da suka yi daa Baba da Hajia kan maganar Amina, cewa Amina gida zata je ta yi wanka, wai gidan Baba, bayan shi yana niyyar fasa tasa tafiyar dan ya sake raya duniyarsu shi da ita da ƴaƴansu hudu? Shikenan sai a wani ce za'a tafi da ita?
Bakin nata da ta ce Hi, da amon muryarta ya nemi cenza tunaninsa
A hankali ya karasa inda take zaune, ta yi irin zaman nan da ake matsewa a cen saman gado, ta dan hade bayanta da jikin abin gadon , kafafuwanta kuwa ta dan dago su ta dora hannayenta samansu
A hankali ya haye gaba dayansa saman gadon ya yi zaune yana kallonta
Bai san a yadda zai fasarta lamarinta a tare da rayuwarsa ba
Tanada girma mai girman da girma bai isa ya kayade ba
Yana gannin mutuncinta, kimarta, da dumbin soyayarta a zuciyarsa
Bai taba tunanin zai samu wannan jarabawa a kan Amina ba
A hankali ya kamo hannunta ya sakaa cikin nasa, sannan ya shiga murzawa kadan kadan yana kallonta, muryarsa a ciki ciki ya ce" Ba zan iya barinki ki tafi ba "
Amina ta bude lumsasun idannuwanta ta zuba masa su, ba zai iya barinta ta tafi ina ba? Ina yake tunanin zata tafi? Hala a tunanin ABDUL tana kan bakanta na neman saki? Lolz lalle
Iska ya furzar daga bakinsa mai zafi ya ce" Shi wankan, a nanma ba sai ki yi ba? Idanma babu mai maki ba gani ba?"
Sai a yanzu ta dago zancen, kuma sai abin ya bata kunya
A hankali ta dan cicira idannuwanta gefe na alamun kunyar, wanda tsaf ya karanceta bar ya samu kansa da sakin murmushi, domin dama yana tunanin gannin haka daga gareta, Aminansa ba dai kunya ba
Ni tuni na ce masu ba zaki tafi ba, suka ce sai kin je, shi wancen Alkalin harda fadin da kansa zai zo ku tafi sai kin yi wankan jego a gabansa, baya ciki da cin amana.....Wifey Ni ai ba dan cin amana bane ko?"
Ya salam, gaba daya nema yake ya cenza duniyarta da dukkan wani tunaninta
A hankali ta janye hannunta taana kallonsa da lumsasun idannuwanta ta ce" Yanzu zamu tafi ko gobe?"
Shiru ya yi sshima yana kallonta, sai kuma ya budi bakinsa a hankali ya ce" Binsu zaki yi?"
Da idannuwanta ta bashi amsa tana masu luuuuuuuuuuuuuuuuuuuuuuuuuu sannan ta dage su
Jajayen lebunnansa ya dan cije yana kallonta ya ce" Tafia zaki yi ki barni ni kadai?"
A hankali ta dan sake matsawa dan matsota yake yi kasa kasa ta ce" Dama ai ba tare da ni kake ba, ko na tafi ba kai kadai bane"
"Meenart" ya fada aa hankali yana katseta
Amina ta sake bude idannuwanta aa hankali ta ce" Aban Amnahhhhhhhh"
Abinda zai fada ya samu kansa da mantawa har ya dan daburce, wannan ne karron farko da ta budi baki ta ce masa Aban Amnahhhhhh, ba ABDUL ba ko kai ka bari fa
Murmushi ya dan saki a hankali ya ce" Bakya tausaya min ko?"
Baki ta dan tabe, sai kuma ta dannawa gefe harara kasa kasa ta ce" Aban Amnah kai ka tausaya min ne?"
Ido ya zarro har yana dafe habarsa , da madaukakin mamaki ya ce" Lah hararata kika yi?"
Amina ta bude idannuwanta tarr tana kallonsa, ta turo bakinta hadi da shagwabe fuskarta ta ce" Ni aa, gefe na harara fa"
"Umum um um Uman twins da ni kike " ya fada yana sake matse mata waje
Amina ta dire kasa hakan ya bayanar da iya tsayin rigar barcin nata da kwata kwata duwawunta kadai ta dan dara
A hankali ta duka tana bashi baya ta dauki takalminta na kusan bed ba dan sai ta yi haka zata saka ba, aa , kawai hakanan ta yi hakan har tana wani irin dan girgiza ta saka takalmin sannan ta mike ta dan gantsare tana yin hammar da ba ta gaskiya ba sai kuma ta janye ribom dinta ta dan girgiza kanta kadan, hakan ya sa gashin kan nata bajewa ya dan watsu gefe da gefe sannan cikin tafiyar izgili ta nufi bayi kasa kasa tana fadin" ABAn Fadeel, bana ciki da rigima, kawai Allah ya bamu alkhairi, yo Allah na tuba yau ka fara cin amana kuwa, ka je kawai wajen dayar na san tana cen tana kyarkyara" da gangan da zata ce kyarkyarar har sai da ta kama kofar bayi ta juya duwawunta son ranta sannan ta shige ta datse kofar tana zarro ido hadi da dafe kirjinta dake dokawar tsoro ta rufe idannuwanta da hannayenta biyu wata mahaukaciyar kunya na son halakata ta rufe bakinta dan kar ta kurma ihun kunyar da ta rufeta
"Dady?, Dady?" Muryar Husaini da ya shigo yiwa mamansa sai da safe ya yi ta salama shiru ba'a amsa ba sai da ya karaso ya taba gefen hannun babansu da ya tarar a zaune tamkar matacen mutun ya kurawa kofar bayi ido ko kiftawa baya yi ya ringa ambaton sunnansa ama shiru, dan haka ya dafa shi yana sake kiran sunnan da karfi
Wani irin ajiyar zuciya ya sauke, a zabure ya kalli Husaini, sai kuma lokaci daya ya kalli jikinsa
Cikin dabara ya dora kafa daya kan daya yana kallon Husaini muryarsa a cen kurya ya ce" Son, ?"
Husaini ya sake kallonsa a hankalin sshima ya ce" Dady baka da lafiya ne?"
ABDUL ya dan fitar da idannuwansa irin bai san me yasa ya ce haka ba ya ce" Rashin lafiya? Me ya sa kace banida lafiys?"
Husaini ya shafo gaban goshinsa da zufa ke tsatsafowa ya ce" Dady kalli fa goshinka?"
ABDUL ya ringa sauke ajiyar zuciya a boye cikin dabara ya kakaro murmushi ya ce" No lafiyata kalau Boy, wai mema kake so?" Ya karashe yana dage masa gira daya
Husaini ya yi murmushi yana kallon gashin girar babn nasu kamar wanda ke gyaran gira, ga cika gaa tsari ya ce" Mama ne ni ban mata good night ba, shine na zo"
ABDUL ya yi murmushi ya shafa kansa yana fadin" Mamanka tanaa bayi, zan sanar mata ka tafi ka kwonta saboda school fa gobe"
Husaini ya gyada kansa ya juya yana masa byby
A hankali ABDUL ya yi masa by din shima sannan ya sake maido dubansa kan kofar
Mikewa ya yi ya karasa ya kama abin budewa ya murda, ama a garkame ta rufe ruf
A hankali ya dora hannunsa saman kofar ya dan shafa kofar yana sauraron ciki ko zai ji motsi, ama baya jin komai
Wata ajiyar zuciyar ya sauke kasa kasa ya ce" Na san kina jina............."
Amina dake like da kofar tana jinsa ta sake lumshe idannuwanta tana sauraronsa, domin bata iya motsawa daga jikin kofar ba tana jin maganarsa da Husaini
ABDUL ya sake sauke numfashi a hankali ya ce" I'm sorry, plz ki yafe min kin ji?"
Amina ta sake lumshe idannuwanta tana dafe gaban kirjinta dake doka mata
Fuska ya sha ya ce" Kai ba nace ka daina kallon yar ba?"
Mansur ya dube shi yana fadin" Dan Allah wai meye haka? Ba za'a yita ta kare ba?"
Firdausi ta yi gaba da dan sauri, dan bata kaunar abinda ke fitowa daga bakin Docter mai kirki
Sam bata so, bata tunanin idan har tana ra'ayin haka a kurkusan nan
Mansur yaa kai zaune yana fadin" Me ka yi kennan? Haba Man, yaya ba zaka kama min ba bayan ina so?"
ABDUL ya tabe baki ya ce" Yaren nan ka tabata basa bukatar kwalba?"
Da haushi haushi Mansur ya ce" Kai dan Allah ka rufa min asiri, kwalbar me yayan masha Allah babu na kasa da kilo 3?, Ina maka magana ta a bani na raya sunna kana kawar min da zancen?"
ABDUL ya yi murmushi ya ce" Man, sai ka bita a hankali.....idan kace zaka takura ba zaka samu abinda kake so ba.....ka ga tanada tabo na maza a rayuwarta, sai ta gamsu da kai a aikace ba a furucin bakinka ba........so kawai ka yi ta kanka, domin nima ta kaina zan yi da rigimamiyata"
Mansur ya yi murmushi yan saka yaran a irin gadon nan na turawa ya lulube su ya mika masa hannu yana yi masa congratulations
A nan dai suka hantse aka kimtsa Amina sosai aka kaita dakin hutu bayan ta sha dinki aka barta tana hutawa, domin awa shida zata yi a saketa, ta haihu lafiya bata samu matsalolin haihuwa ba sai na kari kadai
Ana dawowa daga masalaci aka mayar da baba gida, ama HAJIA tace aa sai sun je ta daidaita masu harkar Ac da sauransu dan kar a yi wasa a kama masu mura, yaran ta masu hoto fiye da a irga, hawaye kuwa daukewa take yi tana karrawa
ABDUL ya nemi waje zai zauna da jalabiyar nan da suka sha kokowa da komai da ita, HAJIA ta nuna Aa, kawai ya wuce gida gasunnan, ai zuwa karfe goma za'a salameta a fara shirya zuwansu gida
Har ya yi gaba ta sake kiransa ya dawo ya dan zauna yana kallonta
Fuskarta a hade ta ce" ABDUL, matarka bata san y'ar uwarta na asibiti bane?"
ABDUL ya yi dan tsai, sai kuma ya gane inda ta nufa, a nutse ya dan yi yannayi na bai sani ba
Hajia ta tabe baki tana gyada kanta ta ce"
A hankali ta dan gyara rigar barcin dake jikinta, mai hasken fari da mannewa a jiki tana dan son wara idannuwanta dake shanyewa dan kansu tamkar wace ke masu haka da gangan, muryarta a dan shake ta ce" Hi "
Idannuwansa ya lumshe, hannunsa daya a cikin aljihun wandon barcinsa irin budaden nan mai dan kauri mai ruwan blu , watau hasken sararin samaniya, sai rigar ciki singileti da kuma ta sama ta wandon wace bai balla boturan ba haka ya ratso al'uma ya taho , hannunsa daya kuwa a saman kirjinsa yana dan shafawa a hankali, yana son dauke yar damuwar dake tattare da shi wace bata wuce rikicin da suka yi daa Baba da Hajia kan maganar Amina, cewa Amina gida zata je ta yi wanka, wai gidan Baba, bayan shi yana niyyar fasa tasa tafiyar dan ya sake raya duniyarsu shi da ita da ƴaƴansu hudu? Shikenan sai a wani ce za'a tafi da ita?
Bakin nata da ta ce Hi, da amon muryarta ya nemi cenza tunaninsa
A hankali ya karasa inda take zaune, ta yi irin zaman nan da ake matsewa a cen saman gado, ta dan hade bayanta da jikin abin gadon , kafafuwanta kuwa ta dan dago su ta dora hannayenta samansu
A hankali ya haye gaba dayansa saman gadon ya yi zaune yana kallonta
Bai san a yadda zai fasarta lamarinta a tare da rayuwarsa ba
Tanada girma mai girman da girma bai isa ya kayade ba
Yana gannin mutuncinta, kimarta, da dumbin soyayarta a zuciyarsa
Bai taba tunanin zai samu wannan jarabawa a kan Amina ba
A hankali ya kamo hannunta ya sakaa cikin nasa, sannan ya shiga murzawa kadan kadan yana kallonta, muryarsa a ciki ciki ya ce" Ba zan iya barinki ki tafi ba "
Amina ta bude lumsasun idannuwanta ta zuba masa su, ba zai iya barinta ta tafi ina ba? Ina yake tunanin zata tafi? Hala a tunanin ABDUL tana kan bakanta na neman saki? Lolz lalle
Iska ya furzar daga bakinsa mai zafi ya ce" Shi wankan, a nanma ba sai ki yi ba? Idanma babu mai maki ba gani ba?"
Sai a yanzu ta dago zancen, kuma sai abin ya bata kunya
A hankali ta dan cicira idannuwanta gefe na alamun kunyar, wanda tsaf ya karanceta bar ya samu kansa da sakin murmushi, domin dama yana tunanin gannin haka daga gareta, Aminansa ba dai kunya ba
Ni tuni na ce masu ba zaki tafi ba, suka ce sai kin je, shi wancen Alkalin harda fadin da kansa zai zo ku tafi sai kin yi wankan jego a gabansa, baya ciki da cin amana.....Wifey Ni ai ba dan cin amana bane ko?"
Ya salam, gaba daya nema yake ya cenza duniyarta da dukkan wani tunaninta
A hankali ta janye hannunta taana kallonsa da lumsasun idannuwanta ta ce" Yanzu zamu tafi ko gobe?"
Shiru ya yi sshima yana kallonta, sai kuma ya budi bakinsa a hankali ya ce" Binsu zaki yi?"
Da idannuwanta ta bashi amsa tana masu luuuuuuuuuuuuuuuuuuuuuuuuuu sannan ta dage su
Jajayen lebunnansa ya dan cije yana kallonta ya ce" Tafia zaki yi ki barni ni kadai?"
A hankali ta dan sake matsawa dan matsota yake yi kasa kasa ta ce" Dama ai ba tare da ni kake ba, ko na tafi ba kai kadai bane"
"Meenart" ya fada aa hankali yana katseta
Amina ta sake bude idannuwanta aa hankali ta ce" Aban Amnahhhhhhhh"
Abinda zai fada ya samu kansa da mantawa har ya dan daburce, wannan ne karron farko da ta budi baki ta ce masa Aban Amnahhhhhh, ba ABDUL ba ko kai ka bari fa
Murmushi ya dan saki a hankali ya ce" Bakya tausaya min ko?"
Baki ta dan tabe, sai kuma ta dannawa gefe harara kasa kasa ta ce" Aban Amnah kai ka tausaya min ne?"
Ido ya zarro har yana dafe habarsa , da madaukakin mamaki ya ce" Lah hararata kika yi?"
Amina ta bude idannuwanta tarr tana kallonsa, ta turo bakinta hadi da shagwabe fuskarta ta ce" Ni aa, gefe na harara fa"
"Umum um um Uman twins da ni kike " ya fada yana sake matse mata waje
Amina ta dire kasa hakan ya bayanar da iya tsayin rigar barcin nata da kwata kwata duwawunta kadai ta dan dara
A hankali ta duka tana bashi baya ta dauki takalminta na kusan bed ba dan sai ta yi haka zata saka ba, aa , kawai hakanan ta yi hakan har tana wani irin dan girgiza ta saka takalmin sannan ta mike ta dan gantsare tana yin hammar da ba ta gaskiya ba sai kuma ta janye ribom dinta ta dan girgiza kanta kadan, hakan ya sa gashin kan nata bajewa ya dan watsu gefe da gefe sannan cikin tafiyar izgili ta nufi bayi kasa kasa tana fadin" ABAn Fadeel, bana ciki da rigima, kawai Allah ya bamu alkhairi, yo Allah na tuba yau ka fara cin amana kuwa, ka je kawai wajen dayar na san tana cen tana kyarkyara" da gangan da zata ce kyarkyarar har sai da ta kama kofar bayi ta juya duwawunta son ranta sannan ta shige ta datse kofar tana zarro ido hadi da dafe kirjinta dake dokawar tsoro ta rufe idannuwanta da hannayenta biyu wata mahaukaciyar kunya na son halakata ta rufe bakinta dan kar ta kurma ihun kunyar da ta rufeta
"Dady?, Dady?" Muryar Husaini da ya shigo yiwa mamansa sai da safe ya yi ta salama shiru ba'a amsa ba sai da ya karaso ya taba gefen hannun babansu da ya tarar a zaune tamkar matacen mutun ya kurawa kofar bayi ido ko kiftawa baya yi ya ringa ambaton sunnansa ama shiru, dan haka ya dafa shi yana sake kiran sunnan da karfi
Wani irin ajiyar zuciya ya sauke, a zabure ya kalli Husaini, sai kuma lokaci daya ya kalli jikinsa
Cikin dabara ya dora kafa daya kan daya yana kallon Husaini muryarsa a cen kurya ya ce" Son, ?"
Husaini ya sake kallonsa a hankalin sshima ya ce" Dady baka da lafiya ne?"
ABDUL ya dan fitar da idannuwansa irin bai san me yasa ya ce haka ba ya ce" Rashin lafiya? Me ya sa kace banida lafiys?"
Husaini ya shafo gaban goshinsa da zufa ke tsatsafowa ya ce" Dady kalli fa goshinka?"
ABDUL ya ringa sauke ajiyar zuciya a boye cikin dabara ya kakaro murmushi ya ce" No lafiyata kalau Boy, wai mema kake so?" Ya karashe yana dage masa gira daya
Husaini ya yi murmushi yana kallon gashin girar babn nasu kamar wanda ke gyaran gira, ga cika gaa tsari ya ce" Mama ne ni ban mata good night ba, shine na zo"
ABDUL ya yi murmushi ya shafa kansa yana fadin" Mamanka tanaa bayi, zan sanar mata ka tafi ka kwonta saboda school fa gobe"
Husaini ya gyada kansa ya juya yana masa byby
A hankali ABDUL ya yi masa by din shima sannan ya sake maido dubansa kan kofar
Mikewa ya yi ya karasa ya kama abin budewa ya murda, ama a garkame ta rufe ruf
A hankali ya dora hannunsa saman kofar ya dan shafa kofar yana sauraron ciki ko zai ji motsi, ama baya jin komai
Wata ajiyar zuciyar ya sauke kasa kasa ya ce" Na san kina jina............."
Amina dake like da kofar tana jinsa ta sake lumshe idannuwanta tana sauraronsa, domin bata iya motsawa daga jikin kofar ba tana jin maganarsa da Husaini
ABDUL ya sake sauke numfashi a hankali ya ce" I'm sorry, plz ki yafe min kin ji?"
Amina ta sake lumshe idannuwanta tana dafe gaban kirjinta dake doka mata