Sashe 37
Ni Zan Ladabi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da sauri Amina da hawaye suka fara wanke idannuwanta ta karaso ta janyo shi jikinta ta rungume shi sosai tana kallon Hajiar itama haka kuma tana shafa bayansa
Muryarta na bari ta ce" Hajia , na yi wani laifin ne kuma?"
Hajia ta mata shiru itama tana jin zuciyarta na dokawa da daci da bacin rai
Amina ta lumshe idannuwanta hawayenta suka gangaro sosai a hankali ta ce" Hajia, walahi walahi baya gabana, Hajia kudinsa basa gabana, Hajia asiri kuka rufa mana da kuka ajiye mu a nan, tabas asiri kuka rufa mana kuma Allah ne zai saka maku da alkhairi.......ama dan Allah ki yi hakuri ki daina yi a gaban yaron nan, ki yi hakuri Hajia ......." Sai ta fashe da kuka ta sake rungume yaronta wanda shima ya shiga nasa kukan, wanda dama ba zaka ji yana kuka ba sai idan abin ya shafeta ne
Hajia ta rintse idannuwanta, fushinta bai sauka ba, haka kuma bata ji wani tausayinsu bama sai fitsararsu da ta gani ta juya ta fice a dakin ta bar gidan gaba daya, dan ta san da wahala a kai kayan nan a kuma dauko su
Kayan aka fara shigowa da su , Baba Lauratu da sauri ta karaso tana kama Amina da mikar da ita hadi da fadin" subahanalah ke meye haka? Lafiya? Tare muke da Mai SHANU fa, menene? Lafiya?"
Amina ta fashe da kuka ta fada jikin Baba tana kukan ta ce" Ki ce a sakeni mana, walahi na iya talaucina kuma na iya rike mutuncina, ki ce a sakeni nima fa ba sonsa nake yi ba, a kan me zan zama wulakantaciya har a gaban dana, a gaban Fadeel zata ringa wulakantani? Kin fi kowa sannin kowa zai hadiye banda Hasan ko?, Ki ce ta saka a bani takardata ni bana sin kayan nan, na je ina da su? Nace ni yar waye? Na saka na doshi ina wai? Haba haba wayo Allahna ni ba zan iya wannan rikicin ba walahi!"
A hankali Baba ke kiran sunnanta dan bata so Baba ya karasa saukowa ya tarda wannan lamari, bata san me zai faru ba
Amina ta ringa jan numfashi ta ce" Baba yaya ba zan yi kuka ba, kin ga fa hankalin Hasan take son daga min, abinda ba zan jura bafa, ni fa ban ce ina son yaron nan ba"
Baba ta ja numfashi ta ce" Ya isa haka, kin ga fa da Baban muka sauko yace so yake ya zo ya ga murmushin marainiya da kansa, kina so ya ganki a haka ne hankalinsa ya tashi? Kin sani sarai fa yadfa yake daukan lamarinki da mahimmanci, ya dace ki sasauta ki yi masa adalci shima kin ji? Dan uwan mijin kuwa ki barni da shi zan rarasheshi kin ji? Maza share hawayenki ma yi maganar daga baya maza share kin ji?"
Amina ta gyada kanta tana share hawayen ta dauko hijabinta ta zurma Baba ta juya dan gannin ko baban ya sauko?
A hankali Baba ya juyar da bayansa ya dan matsa dan baya so su fahimci ya san wani abin
Bismillah ta yi masa ya biyo bayanta yana murmushi
Tunda ya shigo bai zauna ba, haka kuma bai idasa shigowa gaba dayansa ba, ya ja dai daga baki baki ya tsaya hannayensa a Harde a bayansa ya dan saci kallon Hasan da aka kwontar aka mayar da gabansa wajen bango dan basa so Baban ya fahimci ya yi kuka
Murmushi ya yi yana fadin" Uman biyu, kin ga lefenki nan, zan je falo na dan jira dukan abinda yake na da naki ki tarkato ki hadawa Lauratu ta fito da su ta kai ta ba mabukata, ciki harda wannan hijabi naki da kuma takalmin dake kofar dakinki kin ji? Ni kam kayan nan kamar na tayaki dubawa kin gansu kuwa?"
Amina ta tsatsare Baba da ido, murmushin yake ta kakaro tana sada kanta muryarta a cen ciki ta ce" Allah ya karra budi Baba, ama baba a bari a hankali idan na cire na yi wanki da komai sai na bada ko?"
A dake, kansa tsaye , yana dan kama hanyar fita ya ce" Baki gane Ba Uman biyu, ina jiran hakan yanzu, ina nufin harda saitin akwatunnan cen gaskiya basu min ba, ai wanki ba damuwa bane idan ta kama nima sai na wanke fa, ke kuwa kina amarya kuma uwar gida ran gida ai ba'a isa a saka ki wanki yanzu ba"
Da ido suka raka shi su dukansu
Amina ta kai zaune muryarta a raunane ta ce" Baba ki bi shi dan Allah ki rarashe shi kar na taba kayan nan, kin ji abinda tace fa, bana son abinda zai taban mutuncina"
Baba ta yatsina bakinta ta ce" Ke ki je ku yi maganar mana Amina, mutunci kuma ai kece mutuncin jikan da take tinkahon da shi, a dai juri zuwa rafi, watarana tulun zai fashe, tashi ki ban na je na aiwatar da abinda aka sakani, ai daidai yake da ku indai mai SHANU ne, kaya kuwa ta je ta same shi yadda suka yi sai mu ji idan ya zo ya dauke dama shi ya bada damar a kawo"
Tana ji tana gani aka kwashe tsofafin kayanta Baba lauratu ta fita da su
Baba gaba daya kayan nan ya umarci Baba da ta ware wa'inda ba'a dinka ba kala uku uku ma kanta, sauran kuwa ta je ta kai gidan Firdausi ta yiwu ta samu na anfanarwa kanta a ciki
Sosai Baba ta fita da wannan farin cikin, da ta samu Firdausi har kamar nakuda zata taso mata ta farin ciki, kuka kuwa ta sha kamar zata hadiyi zuciya, daga baya tace Babar ta je da su gidanta dan idan ta bara mata a nan ba zata anfana da su ba zai kwashe, idan Allah ya sauketa lafia sai ta ringa dauka da kadan kadan tana anfanarwa kanta
________________________________
Hajia kam na fita gidan Uma ta je ta wuni a ranar, sun yi kiran wani gagarumin malamin adini ya zo da kansa Hajia ta gabatar masa da damuwarta, ta dora da fadin" Malan, wannan lamari idan ba aikin sihiri ba me zai haifar da shi? Mijina gaba daya ya birkice min ? Dan Allah a duba lamarin nan"
Sosai Ustaz Laminu ya nazarci maganarta
A tausashe ya ringa yi masu nasiha baki dayansu sannan ya dora da fadin" Da farko shi sihiri ba abu bane da ido bude ke ganninsa, haka kuma ba'a hawansa da hasashe ko zargi, kwarai zan baki adu'o'in da zaki dage da yi da fadawa Allah, idan har alkhairi ce yarinyar nan Allah ya kwontar maki da hankalinki a kanta, idan kuwa ba alkhairi bace Allah ya raba ba tare da hankalin kowa ya tashi ba, Shi Kuwa Alkali ki ci gaba da yi masa biyaya in sha Allah ko menene Allah zai warware mana baki daya"
Sosai Malan ya basu adu'o'in da suka dace na karya sihiri, ya hada masu da na kariya kala daban daban sannan ya masu salama
Umma ta ja numfashi ta ce" Kai kawata abin nan na damuna, wannan lamari sai hauhawa yake yi fisabililahi kuma ace ba sihiri bane? Kinsan fa shi malan Laminu dama haka yake, ko bincike fa baya yi kwata kwata, ko me ka kawo masa damuwarka a haka din nan ne zai durfafi abin, bi abinda yasa nake nace masa gaskiya abu da yawa da na saka a gabana na fada masa ala tayamu da Adu'a ina gannin hasken abin, ama yanzun kam na fi gane mu samu gagarumin malamin da zai buga mana kasa ya gano mana sirrin dake boye dan mu haye abin ta inda ya dace"
Hajia Hauwa ta sauke ajiyar zuciya ta kurbi jus kadan tana kallon kawarta ta ce" Hajia Uma, kin san fa ni gaskiya ban cika son irin abubuwan nan ba, na fi so ko menene din na bi ta hanyar da ta dace, ina dalili sallar mutun ta lwana arba'in ba'a karba, idan halin mutuwa ya riskeni a haka fa? Kai ina tsoron bin bokaye wai sai ace malamai, wani malami ne zai aikata irin haka?, Ni yanzun abinda ya fi damuna kalar akwatunnan ne da muka dauka damuwata, ai ba classs a cakuden da muka yi, dan kayan dake ciki bani da darr da su, kayan nan ko uwar ta samu ai ta haye bale yar, balema ABDUL din yace zai min transfer na masu ranar da za'a kai kayan dazu da na kire shi ina kukan wani wulakancin na Alkali, ABDUL fa yanada damar ya bijirewa abin nan aman ya kyale alkali yana ta zubar masa da mutunci da sunna a kan banzar yarinyar nan mai manyan idannu!"
Uma ta girgiza kanta tana tsaki ta ce" Ni kam abin nan na dauren kai, koda yake ai shima ba zata barshi banza ba, wainar da ake kawowa alkali ba kince wani sa'in tare suke ci ba? Ke dai dan kawia baki yarda da maganar boka bane da mun nemi mai kaifin wuka ya nuna mata ita karamar kwaro ce, ama walahi idan muka ga zata zame mana dan hakin da muka raina har ta kai ga tsole mana ido ko kw baki je ba ni zan je, domin ba zan yarda a wulakanta lamarin Gwamnana ba!"
Hajia aka wani cira kai da isa an kira dan albarka da gwamna
Uma ta ce" Kuma fa Hajia ke kika damu kanki da maganar kalolin akwatunnan nan, yanzun ba haka na ga ana yi ba sai ki ga an hada su red, su blue, su black, su fari du a tafia daya dan gadara ba, ba wani damuwa fa"
Hajia ta tabe baki tace" A kalolin wannan yelow din mai kama da zawon baby ne ke ci min tuwo a kwarya, ke kika ce mu daukar mata ita kalar kalarta ce"
Hajia Uma tace" Ni fa Allah itama bata da wata matsala, ke dai ba da kudi ba? Ki barsu ai sai mun nunawa maman Yarinyar nan mu ba sa'aninta bane, transfer din za'a yi mata ranar da mazan suka kai kayan a mata shiru, ta ga kudin ba bayani ta haukace, ita karamar yar bariki!"
Hajia ta yi murmushi tana hango wulakancin yadda zai bada kala
Muryarta na bari ta ce" Hajia , na yi wani laifin ne kuma?"
Hajia ta mata shiru itama tana jin zuciyarta na dokawa da daci da bacin rai
Amina ta lumshe idannuwanta hawayenta suka gangaro sosai a hankali ta ce" Hajia, walahi walahi baya gabana, Hajia kudinsa basa gabana, Hajia asiri kuka rufa mana da kuka ajiye mu a nan, tabas asiri kuka rufa mana kuma Allah ne zai saka maku da alkhairi.......ama dan Allah ki yi hakuri ki daina yi a gaban yaron nan, ki yi hakuri Hajia ......." Sai ta fashe da kuka ta sake rungume yaronta wanda shima ya shiga nasa kukan, wanda dama ba zaka ji yana kuka ba sai idan abin ya shafeta ne
Hajia ta rintse idannuwanta, fushinta bai sauka ba, haka kuma bata ji wani tausayinsu bama sai fitsararsu da ta gani ta juya ta fice a dakin ta bar gidan gaba daya, dan ta san da wahala a kai kayan nan a kuma dauko su
Kayan aka fara shigowa da su , Baba Lauratu da sauri ta karaso tana kama Amina da mikar da ita hadi da fadin" subahanalah ke meye haka? Lafiya? Tare muke da Mai SHANU fa, menene? Lafiya?"
Amina ta fashe da kuka ta fada jikin Baba tana kukan ta ce" Ki ce a sakeni mana, walahi na iya talaucina kuma na iya rike mutuncina, ki ce a sakeni nima fa ba sonsa nake yi ba, a kan me zan zama wulakantaciya har a gaban dana, a gaban Fadeel zata ringa wulakantani? Kin fi kowa sannin kowa zai hadiye banda Hasan ko?, Ki ce ta saka a bani takardata ni bana sin kayan nan, na je ina da su? Nace ni yar waye? Na saka na doshi ina wai? Haba haba wayo Allahna ni ba zan iya wannan rikicin ba walahi!"
A hankali Baba ke kiran sunnanta dan bata so Baba ya karasa saukowa ya tarda wannan lamari, bata san me zai faru ba
Amina ta ringa jan numfashi ta ce" Baba yaya ba zan yi kuka ba, kin ga fa hankalin Hasan take son daga min, abinda ba zan jura bafa, ni fa ban ce ina son yaron nan ba"
Baba ta ja numfashi ta ce" Ya isa haka, kin ga fa da Baban muka sauko yace so yake ya zo ya ga murmushin marainiya da kansa, kina so ya ganki a haka ne hankalinsa ya tashi? Kin sani sarai fa yadfa yake daukan lamarinki da mahimmanci, ya dace ki sasauta ki yi masa adalci shima kin ji? Dan uwan mijin kuwa ki barni da shi zan rarasheshi kin ji? Maza share hawayenki ma yi maganar daga baya maza share kin ji?"
Amina ta gyada kanta tana share hawayen ta dauko hijabinta ta zurma Baba ta juya dan gannin ko baban ya sauko?
A hankali Baba ya juyar da bayansa ya dan matsa dan baya so su fahimci ya san wani abin
Bismillah ta yi masa ya biyo bayanta yana murmushi
Tunda ya shigo bai zauna ba, haka kuma bai idasa shigowa gaba dayansa ba, ya ja dai daga baki baki ya tsaya hannayensa a Harde a bayansa ya dan saci kallon Hasan da aka kwontar aka mayar da gabansa wajen bango dan basa so Baban ya fahimci ya yi kuka
Murmushi ya yi yana fadin" Uman biyu, kin ga lefenki nan, zan je falo na dan jira dukan abinda yake na da naki ki tarkato ki hadawa Lauratu ta fito da su ta kai ta ba mabukata, ciki harda wannan hijabi naki da kuma takalmin dake kofar dakinki kin ji? Ni kam kayan nan kamar na tayaki dubawa kin gansu kuwa?"
Amina ta tsatsare Baba da ido, murmushin yake ta kakaro tana sada kanta muryarta a cen ciki ta ce" Allah ya karra budi Baba, ama baba a bari a hankali idan na cire na yi wanki da komai sai na bada ko?"
A dake, kansa tsaye , yana dan kama hanyar fita ya ce" Baki gane Ba Uman biyu, ina jiran hakan yanzu, ina nufin harda saitin akwatunnan cen gaskiya basu min ba, ai wanki ba damuwa bane idan ta kama nima sai na wanke fa, ke kuwa kina amarya kuma uwar gida ran gida ai ba'a isa a saka ki wanki yanzu ba"
Da ido suka raka shi su dukansu
Amina ta kai zaune muryarta a raunane ta ce" Baba ki bi shi dan Allah ki rarashe shi kar na taba kayan nan, kin ji abinda tace fa, bana son abinda zai taban mutuncina"
Baba ta yatsina bakinta ta ce" Ke ki je ku yi maganar mana Amina, mutunci kuma ai kece mutuncin jikan da take tinkahon da shi, a dai juri zuwa rafi, watarana tulun zai fashe, tashi ki ban na je na aiwatar da abinda aka sakani, ai daidai yake da ku indai mai SHANU ne, kaya kuwa ta je ta same shi yadda suka yi sai mu ji idan ya zo ya dauke dama shi ya bada damar a kawo"
Tana ji tana gani aka kwashe tsofafin kayanta Baba lauratu ta fita da su
Baba gaba daya kayan nan ya umarci Baba da ta ware wa'inda ba'a dinka ba kala uku uku ma kanta, sauran kuwa ta je ta kai gidan Firdausi ta yiwu ta samu na anfanarwa kanta a ciki
Sosai Baba ta fita da wannan farin cikin, da ta samu Firdausi har kamar nakuda zata taso mata ta farin ciki, kuka kuwa ta sha kamar zata hadiyi zuciya, daga baya tace Babar ta je da su gidanta dan idan ta bara mata a nan ba zata anfana da su ba zai kwashe, idan Allah ya sauketa lafia sai ta ringa dauka da kadan kadan tana anfanarwa kanta
________________________________
Hajia kam na fita gidan Uma ta je ta wuni a ranar, sun yi kiran wani gagarumin malamin adini ya zo da kansa Hajia ta gabatar masa da damuwarta, ta dora da fadin" Malan, wannan lamari idan ba aikin sihiri ba me zai haifar da shi? Mijina gaba daya ya birkice min ? Dan Allah a duba lamarin nan"
Sosai Ustaz Laminu ya nazarci maganarta
A tausashe ya ringa yi masu nasiha baki dayansu sannan ya dora da fadin" Da farko shi sihiri ba abu bane da ido bude ke ganninsa, haka kuma ba'a hawansa da hasashe ko zargi, kwarai zan baki adu'o'in da zaki dage da yi da fadawa Allah, idan har alkhairi ce yarinyar nan Allah ya kwontar maki da hankalinki a kanta, idan kuwa ba alkhairi bace Allah ya raba ba tare da hankalin kowa ya tashi ba, Shi Kuwa Alkali ki ci gaba da yi masa biyaya in sha Allah ko menene Allah zai warware mana baki daya"
Sosai Malan ya basu adu'o'in da suka dace na karya sihiri, ya hada masu da na kariya kala daban daban sannan ya masu salama
Umma ta ja numfashi ta ce" Kai kawata abin nan na damuna, wannan lamari sai hauhawa yake yi fisabililahi kuma ace ba sihiri bane? Kinsan fa shi malan Laminu dama haka yake, ko bincike fa baya yi kwata kwata, ko me ka kawo masa damuwarka a haka din nan ne zai durfafi abin, bi abinda yasa nake nace masa gaskiya abu da yawa da na saka a gabana na fada masa ala tayamu da Adu'a ina gannin hasken abin, ama yanzun kam na fi gane mu samu gagarumin malamin da zai buga mana kasa ya gano mana sirrin dake boye dan mu haye abin ta inda ya dace"
Hajia Hauwa ta sauke ajiyar zuciya ta kurbi jus kadan tana kallon kawarta ta ce" Hajia Uma, kin san fa ni gaskiya ban cika son irin abubuwan nan ba, na fi so ko menene din na bi ta hanyar da ta dace, ina dalili sallar mutun ta lwana arba'in ba'a karba, idan halin mutuwa ya riskeni a haka fa? Kai ina tsoron bin bokaye wai sai ace malamai, wani malami ne zai aikata irin haka?, Ni yanzun abinda ya fi damuna kalar akwatunnan ne da muka dauka damuwata, ai ba classs a cakuden da muka yi, dan kayan dake ciki bani da darr da su, kayan nan ko uwar ta samu ai ta haye bale yar, balema ABDUL din yace zai min transfer na masu ranar da za'a kai kayan dazu da na kire shi ina kukan wani wulakancin na Alkali, ABDUL fa yanada damar ya bijirewa abin nan aman ya kyale alkali yana ta zubar masa da mutunci da sunna a kan banzar yarinyar nan mai manyan idannu!"
Uma ta girgiza kanta tana tsaki ta ce" Ni kam abin nan na dauren kai, koda yake ai shima ba zata barshi banza ba, wainar da ake kawowa alkali ba kince wani sa'in tare suke ci ba? Ke dai dan kawia baki yarda da maganar boka bane da mun nemi mai kaifin wuka ya nuna mata ita karamar kwaro ce, ama walahi idan muka ga zata zame mana dan hakin da muka raina har ta kai ga tsole mana ido ko kw baki je ba ni zan je, domin ba zan yarda a wulakanta lamarin Gwamnana ba!"
Hajia aka wani cira kai da isa an kira dan albarka da gwamna
Uma ta ce" Kuma fa Hajia ke kika damu kanki da maganar kalolin akwatunnan nan, yanzun ba haka na ga ana yi ba sai ki ga an hada su red, su blue, su black, su fari du a tafia daya dan gadara ba, ba wani damuwa fa"
Hajia ta tabe baki tace" A kalolin wannan yelow din mai kama da zawon baby ne ke ci min tuwo a kwarya, ke kika ce mu daukar mata ita kalar kalarta ce"
Hajia Uma tace" Ni fa Allah itama bata da wata matsala, ke dai ba da kudi ba? Ki barsu ai sai mun nunawa maman Yarinyar nan mu ba sa'aninta bane, transfer din za'a yi mata ranar da mazan suka kai kayan a mata shiru, ta ga kudin ba bayani ta haukace, ita karamar yar bariki!"
Hajia ta yi murmushi tana hango wulakancin yadda zai bada kala