Sashe 71
Ni Zan Ladabi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Husaini dake rike da hannunta jin yannayin muryarta ya dago dubansa yana kallonta ya ce" Mama bakida lafiya ne?"
Amina ta girgiza kanta ta ce" Mura nake Fadeel, nace a makaranta ya cire ku?"
Hasan ya ce" Eh mana mama an jima ai, an sakamu a wata baba mun je da uncle ya biya komai kuma Dady ya je ya gani yace ta masa, sai ake yi mana lesson akace sai mun yi lesson na wata guda kafin mu shige aji da sauran yaren Ko Husaini?"
A hankali ta dakata tana fadin" My boys, ku tafi ku buga ball din mana"
Kai Husaini ya gayada ya tafi da gudu, Hasan kuwa ya sake zuba mata ido kadan, sai kuma ya saki hannun nata ya juya a sanyaye damuwar yannayinta na kama shi
Sai da ta ga sun fara buga ball din ta idasa karasawa bangarenta ta kama abin budewar ta bude ta shiga falonta
Sai da ta ga sun shiga buga ball din sannan ta karasa bangaren nata ta kama abin budewar ta bude ta shiga tana jin tunaninta na sake harhade mata
Daga kicin take jin dan motsi, bata nufa ba dan ta tabata ba zai wuce Fido ke girki ba , ya zama hajiar girke girke na gargajiya tana ta dura mata bata san abinda ke tare da ita ba, du sunna tunanin cenjin yannayi ne , basu san abinda ta kumsa ba
Dakinta ta shige ta rufe ta karasa bakin madubi a hankali tana cire hijabinta
Rigar dake jikinta ta lesh ta ja zif dinta kasa a hankali tana kallon kanta a madubin
Jikinta ta zubawa ido, kan cikinta
Shafewarsa ke son karyata maganar da ba likita bane ya tabatar mata
A hankali ta dora hannunta tana kallo , tunani na yi mata yawa a ranta
A hankali ta idasa tubewa ta kwashe ta kai wajen shanya ta shanya su sannan ta wuce bayi dan yin wanka
Bayan ta fito harda alwalarta ta dauro ta dawo ta zauna ta sake daukan carbi tana ja hadi da zama ta hade jikinta waje daya
A ciki ta yi sallar magariba, bayan ta gama a dole ta fito dan Firdausi sai bugawa take yi , suka ci abinci tare da yaren da Firdausin dake ta faman tambayarta maman biyu shin menene? Bakida lafiya ne? Hakama twins sai tambayarta suke yi shin lafiyarta? Batada lafiya ne? Ama amsar daya ce barci take ji
Sai da suka gama ta mike tana duban Fido ta ce" Fido, dan Allah ki tabatar yarana sun yi wanka ku masu addu'a kafin su yi barci kin ji? Ni yau barci ke damuna"
Firdausi da ta fahimci bayan barcinma akoy wata damuwar a tatare da yayarta, sai dai ba zata matsa mata da son ji a yanzu ba dan bata san me hakan zai haifar ba a hankali tana murmushi ta ce" Aunty, keda kin san ko sun yi barci Abansu sai ya kuma dubawa idan an masu komai yadda ya dace? Ke dai jeki ki yi sallah ki kwonta, Allah ya tashemu lafiya"
Amina ta dan kura mata ido, sai take tunanin du kamar da gangan suke yawan sako maganar mutumen da take so ta kawar da maganarsa a ranta dan ta manta da shi kwata kwata
Baki ta tabe ta juya ta nufi dakinta bata ce komai ba
Firdausi ta bita da kallo tana sauke ajiyar zuciya, a koda yaushe ta dora kanta saman abin sallah adu'arta itace, Allah ya sa yayarta ta sauko dubanta gabanta ta gane me ke tare da ura na alkhairi, ta sani sarai yayarta ba dai son girma ba, tunda abu ya kasance haka kuwa sai a hankali, ama baban dana sannin da ba zata so ya tabata a garesu ba baki daya shine yayarta ta ki mijinta
Mijinta shine mijin da kowace mace zata yi burin samu a rayuwa
Wanda ya cancaleka, ya cancali ahalinka? Wanda ya mayar da naka nasa da zuciya daya? Bata taba tunanin akoy namiji irin wannan a duniya ba, ta zata masu kirkin basa tsayin kwana suke tafia su bar matan, lalatatun sunne cika gari, gashi dai jibi zata zubar da wankan haihuwar da ta yi da kuma rabonta da gidan ukuba, ita kam ta san ba ita ba aure, ba zata kuma ba, ba zata yarda ta kuma ba koda wasa, mijinta da ya zo babu wanda ya kaishi adini da nuna talaucinsu baya damunsa, ya kasance yakan talafesu da nasiha da yin uzuri, ama tana shiga gidansa ta zama tamkar makiyiyarsa, basa shan innuwa guda, a kulun kuma abin sake lalacewa yake yi.....bata yarda da bashida imani da tausayi ba sai a nakudarta, ba kowa ya kashe mata ƴaƴanta ba sai ubansu, wannan kalma tana fatan maimaitata a gaban mahalincinta da Mudi!
__________________________________
Tunda ta shiga dakin nata ta yi shirin kwonciya barci ta kwonta da carbinta a hannunta bayan ta gama yin sallah tana saurare
Kunnayenta ke sauraron falo har karfe goma na dare ya yi ta ji shiru ba ihun yara ba hayaniya ba komai
A hankali ta tashi zaune tana duban agogon dakin da wani tunani na daban a cikin zuciyarta
Sai da ta ga batada mai bata amsa ta koma a sanyaye ta kwonta ta sake yin addu'a ta lumshe idannuwanta
Da kyar barci ya dauketa , barcinta mai nauyi
A cikin barcinta kiraye kirayen sallar asuba ya farkar da ita , ta mike jikinta da nauyi na abin barci ta nufi bayi ta dauro alwallah bayan ta watsa ruwa dan ta saku, sannan ta fito ta gabatar da sallah still kunnayenta a waje,sai dai yanzunma babu hayaniyar komai, shiruya fi yawa
Barci ta koma dan shi ya fi cin karfinta, har sai da kusan takwas na safe ta tashi a gigice sakamakon yinwar dake kwakular hanjinta
A gagauce ta kimtsa kanta ta shafa turare sosai sannan ta fito falon
Murmushi ta yi gannin Baba da Firsausi zaune sunna cin abinci
Karasawa ta yi ta zauna kusa da su ta shiga hannu Baka , hannu kwarya tana gaishe da Babar lokaci guda
Baba ta yi murmushi ta ce" Amina ki ci a hankali mana"
Amina ta gyada kanta tana tausawa har ta hadiye sannan ta ce" Baba, wannan cenjin yannayi da saka cin abinci yake , bakiji cikina ba, jikina har rawa yake yi fa"
Baba ta ce" Aya, hakane kin san sai a hankali dama , yanzu daga yannayinki ya saba shikenan, sai ki ga kin daina"
Kai ta gyada a ranta tana ayana' Ba zan fada maku komai ba in sha Allah bale ku min wani kallon '
Sai da cikinta ya dauka sannan ta iya samun nutsuwa tana share zufa ta gyara zamanta tana kallon Baba dake yi mata bayani a kan maganar kwana arba'in din da Fido zata yi da haihuwa, waina da ake toyawa a yi sadaka koda abun ba rai, bale za'a hade da ta arba'in din yaren dai da sauransu
Amina ta gyada kanta ta ce" To Baba , in wannan ne nima sai na bada kudin hatsin ai da kudi a wajena fa, ba sai na fada masa ba inaga"
Baba ta dubeta da kyau ta ce" Aa Amina, ai dole ki fada masa, kin ga yanada hakin sannin hakan, bayan wannanma ai Uba ne baban wa uba ne Amina"
Amina ta tsare Bakin Baba dake taunar goro yana kira mata ABDUL uba ne a wajenta
Baki ta tabe ta kawar da kanta ciki ciki ta ce" Zan sanar masa"
Baba ta kureta da kallo, Hakama Firsausi
Baba ta gyada kanta ta ce" Allah shi kyauta, ni yau banma ganshi ba ai da ban tsaya shiriritar baki sako ba, na san ya fita tunda safe ko? Abdallah kennan sarkin nema"
Firsausi ta ce" Nima jiya har na yi barci dai bai shigo ba, ama na san ba zai ki shigowa gannin ƴaƴan ba komai dare in dai ba tafia ya yi ba?, Uman biyu ko ya yi tafia ne?"
Amina ta ciciba ta mike ciki ciki ta ce" Je ki gani mana dilla sai tambaya"
A ranta kuwa ayanawa take ' Yaya za'a yi ya zo? Bai zo ba ai, dama ni ba wani son zuwan naka nake ba, kar ka zo din ma mana!'
Baba ta cire kanta daga rakiyar Amina da ido ta maido dubanta kan Firdausi ta ce" wannan ya dai Allah ya tarota yarinyar nan"
Fido ta talabe haba ta ce" Amen Baba, haka jiya bata tsaya ta kula kowa ba, tun nan na gane ba lafiya, shi yasa na ki kwonci sai da ya shigo gidan nan, wai ace Aunty ta bude baki a gabansa da gaban hajia ta ce baya sonsa?"
A zabure Baba ta dafe kirji ta ce" Na ga annabi idan na yi hali na gari, ita Aminar? Kice ta lalatamu ta sa an saketa?"
Firdausi ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Ya ki fada min komai, wannanma da kyar ya fito daga fatar bakinsa, shi dai damuwarsa ta yi hakuri ta kula da cikin nan, daga nan ya shiga dakin nata ya dan jima ya fito ya shiga na biyu ya fito yace min kar na nuna ya zo kwata kwata "
Baba ta sake talabe kumatunta, tunaninta faya ne har ga Allah kar aje Amina na fama da aljannu masu taurin kai basu sani ba? Aa ita kam zata fara nemo taimako na rubutu da dan turare na aljanu ta fara yi mata ko a dace
Nan suka wuni tare, kowa na walwala banda Amina dake cicin magani, abubuwan dake ranta gani take ya fi na kowa muni, shi yasa da ta ga su basuda wata damuwa ta saka hijabinta ta fice ta ringa kale kalen tsuntsaye da yannayin ginnin gidan ABDUL, tamkar ba za'a mutu ba, an yi gini kamar ba a duniya ba jama'a kuma mamalakin abin ya sheka a shekashi kabari daga shi sai likafani ko matashin kai babu
A haka ta karasa wajen ginnin da akai mata
Tun daga yannayin wajen take ta kallon tsaruwar ginnin da irin zannen da aka yi na gyare gyare kala kala, zane ne aka yi a jikin ginnin ba hoto bane aka lika
Amina ta girgiza kanta ta ce" Mura nake Fadeel, nace a makaranta ya cire ku?"
Hasan ya ce" Eh mana mama an jima ai, an sakamu a wata baba mun je da uncle ya biya komai kuma Dady ya je ya gani yace ta masa, sai ake yi mana lesson akace sai mun yi lesson na wata guda kafin mu shige aji da sauran yaren Ko Husaini?"
A hankali ta dakata tana fadin" My boys, ku tafi ku buga ball din mana"
Kai Husaini ya gayada ya tafi da gudu, Hasan kuwa ya sake zuba mata ido kadan, sai kuma ya saki hannun nata ya juya a sanyaye damuwar yannayinta na kama shi
Sai da ta ga sun fara buga ball din ta idasa karasawa bangarenta ta kama abin budewar ta bude ta shiga falonta
Sai da ta ga sun shiga buga ball din sannan ta karasa bangaren nata ta kama abin budewar ta bude ta shiga tana jin tunaninta na sake harhade mata
Daga kicin take jin dan motsi, bata nufa ba dan ta tabata ba zai wuce Fido ke girki ba , ya zama hajiar girke girke na gargajiya tana ta dura mata bata san abinda ke tare da ita ba, du sunna tunanin cenjin yannayi ne , basu san abinda ta kumsa ba
Dakinta ta shige ta rufe ta karasa bakin madubi a hankali tana cire hijabinta
Rigar dake jikinta ta lesh ta ja zif dinta kasa a hankali tana kallon kanta a madubin
Jikinta ta zubawa ido, kan cikinta
Shafewarsa ke son karyata maganar da ba likita bane ya tabatar mata
A hankali ta dora hannunta tana kallo , tunani na yi mata yawa a ranta
A hankali ta idasa tubewa ta kwashe ta kai wajen shanya ta shanya su sannan ta wuce bayi dan yin wanka
Bayan ta fito harda alwalarta ta dauro ta dawo ta zauna ta sake daukan carbi tana ja hadi da zama ta hade jikinta waje daya
A ciki ta yi sallar magariba, bayan ta gama a dole ta fito dan Firdausi sai bugawa take yi , suka ci abinci tare da yaren da Firdausin dake ta faman tambayarta maman biyu shin menene? Bakida lafiya ne? Hakama twins sai tambayarta suke yi shin lafiyarta? Batada lafiya ne? Ama amsar daya ce barci take ji
Sai da suka gama ta mike tana duban Fido ta ce" Fido, dan Allah ki tabatar yarana sun yi wanka ku masu addu'a kafin su yi barci kin ji? Ni yau barci ke damuna"
Firdausi da ta fahimci bayan barcinma akoy wata damuwar a tatare da yayarta, sai dai ba zata matsa mata da son ji a yanzu ba dan bata san me hakan zai haifar ba a hankali tana murmushi ta ce" Aunty, keda kin san ko sun yi barci Abansu sai ya kuma dubawa idan an masu komai yadda ya dace? Ke dai jeki ki yi sallah ki kwonta, Allah ya tashemu lafiya"
Amina ta dan kura mata ido, sai take tunanin du kamar da gangan suke yawan sako maganar mutumen da take so ta kawar da maganarsa a ranta dan ta manta da shi kwata kwata
Baki ta tabe ta juya ta nufi dakinta bata ce komai ba
Firdausi ta bita da kallo tana sauke ajiyar zuciya, a koda yaushe ta dora kanta saman abin sallah adu'arta itace, Allah ya sa yayarta ta sauko dubanta gabanta ta gane me ke tare da ura na alkhairi, ta sani sarai yayarta ba dai son girma ba, tunda abu ya kasance haka kuwa sai a hankali, ama baban dana sannin da ba zata so ya tabata a garesu ba baki daya shine yayarta ta ki mijinta
Mijinta shine mijin da kowace mace zata yi burin samu a rayuwa
Wanda ya cancaleka, ya cancali ahalinka? Wanda ya mayar da naka nasa da zuciya daya? Bata taba tunanin akoy namiji irin wannan a duniya ba, ta zata masu kirkin basa tsayin kwana suke tafia su bar matan, lalatatun sunne cika gari, gashi dai jibi zata zubar da wankan haihuwar da ta yi da kuma rabonta da gidan ukuba, ita kam ta san ba ita ba aure, ba zata kuma ba, ba zata yarda ta kuma ba koda wasa, mijinta da ya zo babu wanda ya kaishi adini da nuna talaucinsu baya damunsa, ya kasance yakan talafesu da nasiha da yin uzuri, ama tana shiga gidansa ta zama tamkar makiyiyarsa, basa shan innuwa guda, a kulun kuma abin sake lalacewa yake yi.....bata yarda da bashida imani da tausayi ba sai a nakudarta, ba kowa ya kashe mata ƴaƴanta ba sai ubansu, wannan kalma tana fatan maimaitata a gaban mahalincinta da Mudi!
__________________________________
Tunda ta shiga dakin nata ta yi shirin kwonciya barci ta kwonta da carbinta a hannunta bayan ta gama yin sallah tana saurare
Kunnayenta ke sauraron falo har karfe goma na dare ya yi ta ji shiru ba ihun yara ba hayaniya ba komai
A hankali ta tashi zaune tana duban agogon dakin da wani tunani na daban a cikin zuciyarta
Sai da ta ga batada mai bata amsa ta koma a sanyaye ta kwonta ta sake yin addu'a ta lumshe idannuwanta
Da kyar barci ya dauketa , barcinta mai nauyi
A cikin barcinta kiraye kirayen sallar asuba ya farkar da ita , ta mike jikinta da nauyi na abin barci ta nufi bayi ta dauro alwallah bayan ta watsa ruwa dan ta saku, sannan ta fito ta gabatar da sallah still kunnayenta a waje,sai dai yanzunma babu hayaniyar komai, shiruya fi yawa
Barci ta koma dan shi ya fi cin karfinta, har sai da kusan takwas na safe ta tashi a gigice sakamakon yinwar dake kwakular hanjinta
A gagauce ta kimtsa kanta ta shafa turare sosai sannan ta fito falon
Murmushi ta yi gannin Baba da Firsausi zaune sunna cin abinci
Karasawa ta yi ta zauna kusa da su ta shiga hannu Baka , hannu kwarya tana gaishe da Babar lokaci guda
Baba ta yi murmushi ta ce" Amina ki ci a hankali mana"
Amina ta gyada kanta tana tausawa har ta hadiye sannan ta ce" Baba, wannan cenjin yannayi da saka cin abinci yake , bakiji cikina ba, jikina har rawa yake yi fa"
Baba ta ce" Aya, hakane kin san sai a hankali dama , yanzu daga yannayinki ya saba shikenan, sai ki ga kin daina"
Kai ta gyada a ranta tana ayana' Ba zan fada maku komai ba in sha Allah bale ku min wani kallon '
Sai da cikinta ya dauka sannan ta iya samun nutsuwa tana share zufa ta gyara zamanta tana kallon Baba dake yi mata bayani a kan maganar kwana arba'in din da Fido zata yi da haihuwa, waina da ake toyawa a yi sadaka koda abun ba rai, bale za'a hade da ta arba'in din yaren dai da sauransu
Amina ta gyada kanta ta ce" To Baba , in wannan ne nima sai na bada kudin hatsin ai da kudi a wajena fa, ba sai na fada masa ba inaga"
Baba ta dubeta da kyau ta ce" Aa Amina, ai dole ki fada masa, kin ga yanada hakin sannin hakan, bayan wannanma ai Uba ne baban wa uba ne Amina"
Amina ta tsare Bakin Baba dake taunar goro yana kira mata ABDUL uba ne a wajenta
Baki ta tabe ta kawar da kanta ciki ciki ta ce" Zan sanar masa"
Baba ta kureta da kallo, Hakama Firsausi
Baba ta gyada kanta ta ce" Allah shi kyauta, ni yau banma ganshi ba ai da ban tsaya shiriritar baki sako ba, na san ya fita tunda safe ko? Abdallah kennan sarkin nema"
Firsausi ta ce" Nima jiya har na yi barci dai bai shigo ba, ama na san ba zai ki shigowa gannin ƴaƴan ba komai dare in dai ba tafia ya yi ba?, Uman biyu ko ya yi tafia ne?"
Amina ta ciciba ta mike ciki ciki ta ce" Je ki gani mana dilla sai tambaya"
A ranta kuwa ayanawa take ' Yaya za'a yi ya zo? Bai zo ba ai, dama ni ba wani son zuwan naka nake ba, kar ka zo din ma mana!'
Baba ta cire kanta daga rakiyar Amina da ido ta maido dubanta kan Firdausi ta ce" wannan ya dai Allah ya tarota yarinyar nan"
Fido ta talabe haba ta ce" Amen Baba, haka jiya bata tsaya ta kula kowa ba, tun nan na gane ba lafiya, shi yasa na ki kwonci sai da ya shigo gidan nan, wai ace Aunty ta bude baki a gabansa da gaban hajia ta ce baya sonsa?"
A zabure Baba ta dafe kirji ta ce" Na ga annabi idan na yi hali na gari, ita Aminar? Kice ta lalatamu ta sa an saketa?"
Firdausi ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Ya ki fada min komai, wannanma da kyar ya fito daga fatar bakinsa, shi dai damuwarsa ta yi hakuri ta kula da cikin nan, daga nan ya shiga dakin nata ya dan jima ya fito ya shiga na biyu ya fito yace min kar na nuna ya zo kwata kwata "
Baba ta sake talabe kumatunta, tunaninta faya ne har ga Allah kar aje Amina na fama da aljannu masu taurin kai basu sani ba? Aa ita kam zata fara nemo taimako na rubutu da dan turare na aljanu ta fara yi mata ko a dace
Nan suka wuni tare, kowa na walwala banda Amina dake cicin magani, abubuwan dake ranta gani take ya fi na kowa muni, shi yasa da ta ga su basuda wata damuwa ta saka hijabinta ta fice ta ringa kale kalen tsuntsaye da yannayin ginnin gidan ABDUL, tamkar ba za'a mutu ba, an yi gini kamar ba a duniya ba jama'a kuma mamalakin abin ya sheka a shekashi kabari daga shi sai likafani ko matashin kai babu
A haka ta karasa wajen ginnin da akai mata
Tun daga yannayin wajen take ta kallon tsaruwar ginnin da irin zannen da aka yi na gyare gyare kala kala, zane ne aka yi a jikin ginnin ba hoto bane aka lika