Sashe 67
Ni Zan Ladabi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai gashi ta zannata a mutunce, a kamilance, a hakimce a bayan motar da Muhammat ya ja bayan ABDUL ya yi mata adu'ar Allah ya tsare ya bada Sa'a
Suka je ta shige aji ta zanna ta fito ta samu Muhammat na jiranta, harda abin karin da ta sha mamakin yadda aka yi ya san yinwa take ji, har mamakin kanta take yi kafin ta fito fa sai da ta karya tare da Fido da ta yi dan wake tun da asusuba, ta ci dan waken nan kamar ba gobe, kuma sai gashi tun kafin a fito wata yinwar na yi mata wawushe da kayan ciki, kuma yinwar nan fa idan tana ji bata jin kunyar cin abinci a gaban kowa
Bata san tana ci hannu baka hannu kwarya ba a cikin motar sai da ta cinye tana lumshe ido tana kora ruwa mai sanyi ta dubi wajen Muhammat ta ce" Ama muhammat wannan dambu ya yi dadi, a ina ka siyo shi?"
Muhammat ya yi murmushi yana kadda kai, watau abinda ya faru ogansa ne yace da shi a ina za'a samo abincin gargajiya, dangin abinci dai na gargajiya, idanma da hali harda dadawa
Shine ya je ya samu Matarsa ita kuwa ta kaishi gidan da ake yin dambun nan suka siyo
Yana kai masa yace aa ya je daukan Uman biyu da shi zata so samunsa a wannan lokacin
Har yana mamakin dambu kuma uman biyun?, Sai gashi ta cinye tsaf
Muhammat ya ce" Mom twins ai a gidan wata kawar madame na siyo shi"
Amina ta gyada kai tana fadin" Muhammat ta iya dambu, man kulin nan da ta saka ya yi dadi sosai, mu je mu karro in ajiye da yama na ci, sai na ji ko kulun shi zan ringa ci ba zan gajiya ba, ama ka san wannan dambun ba na gaz bane ko Muhammat?"
Muhammad da ya dauke wuta tunda tace su je su siyo yana tunanin ai bama zai tarki zuwa da ita ba Sir ya nadi hancinsa ya ce" ai da itace take yi, ko man da itace take soyawa, ai bakiga ba tsaftarta, ama yanzun gida zan kaiki sai na koma na gani idan akoy na karro maki"
"Aa Muhammat, ba gida zaka kaini ba gaskiya, zuwa zamu yi na siyowa baba, na tabata idan ya taba dambun nan gobema sai ya sa an siyo masa, mu he mu sayi da yawa a kai masa nasa nima na tafi da nawa gida" Amina ta fada tana buda yar jakarta dan ta ga tanadin jakar, kar aje ba nauyi tana ta maganar aje ta sayi dambu
Waje ya samu ya parker yana fadin" to bara na amsa kira na dawo mu tafi
Daga motar ya fita ya koma gefe ya danna kiran ABDUL da fatan Allah ya sa ya daga da wuri, duda ya san da wahala ya ki dagawar , ama kuma idan aiki ya masa yawa yakan ki dagawarma
Koro masa bayani ya yi dala dala, wanda hakan ya saka ABDUL neman excus ya fito daga dakin meeting din da suke yi da bakinsa yana sake fadin" Wai kai wa ya aikeka fada mata ga inda ka siyo? Muhammat bakinka ba dai magana ba, yanzu idan babu fa?"
Muhammat ya ce" Nima abinda nake ta tunani kennan, kar dai ta yi wannan kuka nata na shiga uku"
ABDUL ya dafe gaban goshinsa ya ce" Kana ji, ka fara kiran matarka, ta je ta yi jiranka a zuba a daure, ka yi ta yawo da ita kafin ku karasa a tabatar an daure komai , kawai a miko maku , ku je wajen baban daga cen sai ka maida ita gida"
Muhammat ya ce" In sha Allah sir"
Har zai katse ya ce" Kana ji?"
Mummamat ya amsa da "eh sir ina ji"
"Muhammat kar ka yi tukin ganganci da ita ka ji?" ABDUL ya fada a hankali yana duban agogon hannunsa.
Muhammat na murmushi ya sake fadin" Bi'izinillah Sir"
Ai ko gidan suka wuce, Muhammat ya fita daga motar ya jira kaɗan matarsa ta miƙo masa dambun sannan suka wuce gidan Baba mai Shanu.
Tunda suka shiga bayan sun gaisa, bata nemi hawa wajen hajia ba, domin ba haka tsakaninsu, idanma ta je zata dauki wulakanci a hannunta ne na gori kala kala,
Da zumudi ta masa tayin shin ta zuba masa dambu zai ci?
Baba ya kalleta da mamaki yace "Uman biyu yau kuma dambu aka yi?"
Da fara'a a fuskarta tace "A'a Baba, ai a hanya ne na sa Muhammat ya tsaya muka siyo, wallahi Baba baka ji dambun ba? Na zuba maka ka ci za ka ji daɗ..."
Yar sauran harafin daya rage ne ya makale dan ita wallahi kallon da Baban yake mata kamar wanda ya ga wani abu a jikinta, irin kallon mamakin nan ne da kuma son gano wani abu........, Dan kallon jikinta ta yi , kar aje ko abincin ta zuzuba a jikinta bata sani ba?
Murmushin da ya saki tare da girgiza kanshi gefe daya ya sake tabbatar mata da lallai fa Baban wani abu yake tunani a kan ta.
Amma tunda ba tambayarshi za ta yi ba sai kawai ba ta ce komai ba aka bar zancen, amma kam yannayin nasa kamar wasu lokuta yaron nan dake sakata a duhu kuma ya barta da duhun kai yake mata shi ma.
Dake kwanan Risala ne yau kuma ba wani damuwa take da shiga harkar yarinyar ba, har fridge din falon ta zo dan daukar kakkaurar madarar da suka rage dazu ita da Fido, dan wallahi idan tana sha ji take kamar za ta tsinka harshenta
Tafiya take tana jan kafafunta dake sanye da silifas masu laushi na daki tana susar bayanta da yar yatsarta, kuma a ganinta darene ai kowa yayi bacci, shiyasa ta fito da riga da wondonta na cotton da suka dan saketa har jikinta na rawa a ciki, iya hula ce a kanta wacce ta tsaya a rabin kanta kamar za ta fadi.
Har ta buda fridge din ta dauko farin bidon ta kalli madarar mai kaurin gaske da sanyi, rufewa tayi ta juya da niyyar komawa dakinta. Hada ido sukayi da Abdul da ya fito daga dakin Biyu zai koma makwancinsa, domin Risala har yanzu bai idasa sake mata ba, dan tunda ta dawo ya kan je dakin ne ya ga lafiyarta, amma yana so ya barta tayi hankali kafin ya sake nuna ita ma matarsa ce, dan ba zai iya da wannan kwaroroton tereren tara masa dangi ba daga abinda bai kai bai kawo ba.........sirrinsa abin boyewa ne da karfin gaske ba abin watsawa bane!
Kyaɓe baki ta fara yi tana lullumshe idanu, sai kuma ta ɓoye madarar a bayanta ta zura hannunta cikin bayan rigar ita a dole kar ya ga me ta zo yi, a nutse ta shiga takawa ba ta sake kallon inda yake ba sai ma gunguni da take kasa kasa a kan me bai yi bacci ba shi din?
Shi dai yana tsaye bai ce mata kala ba har ta shige dakin ta maida kofar ta rufe, wani tattausan murmushi ya saki yana girgiza kai a ranshi ya ayanna 'Uman biyu kennan'
*Bayan kwana biyu* dukansu gidan Baba Rabi'u suka je bikin jikar tasa, duk da ba wani shaƙuwa ce tsakaninsu ba amma dai tare suka tafi bisa bukatar Baba da shi ABDUL din , harma suka kwashe awannin nan tare, ama kowa da inda ya fi karkata, domin Hajia na cen wajen tsofafin wajen sunna nasu shagali na iyaye,Amina na wajen amaren sunna nasu shagali , Risala na nata eriyar tana nata shagalin har lokacin dawowarsu gida yayi
Abdul da kanshi ne yake tuƙasu
Hajia na gaba tare da shi sai ita da Risala a baya, inda Muhamat ke tuƙa Baba da biyu, ya zamto motar sunna bibiyar junna ne, watau daya a gaba daya a baya
Motar shiru da fari ba mai wani magana, sai kuma Hajia da Risala da suka fara yar hirarsu da Abdul ma shi tsakani da Allah yana jin me suke fada amma baya gane gaban zancen, gyara zama Hajia ta sake yi ta buɗa jakarta ta lalubo dabinonta irin na kwalin nan ta fara ci, dan bata ci abincin bikin ba, sam lamarin matar Rabi'u ba classs, yaushe zata barawa mutanen gida su yi girkin abincin auren jikarta? Ga kampani na ma'aikata dake girki kala daban daban maimakun su je su dauko a yi girki a tsare da kiyayewa ...aaa, sai ta bari yan gida suka jamalmala, shi yasa ta kasa ci gaskiya, dan a matsayinta ba zata wanke goma ta durmiya biyar a cikin abincin vilagggssss ba!
Ɗan kallonta Amina tayi daga baya, dan a barin da ABDUL yake ta zauna, tana iya gannin hajiar da abinda take yi
har zata ɗauke idanunta sai kuma ta sake kallon dabinon, irin yanda ya jeru raras a gidanshi yayi ja mai kyau da alamar masifaffen zaƙi, sai kawai ta ji yawunta na wucewa ba tare da ta ankara ba
alamar dai so take yi sosai
Ba ta ankara ba, ba ta kula da ta kasa dauke idanunta akan dabinon ba har saida Hajia ta ci mai isarta ta maida sauran a jaka tana korawa da ruwan roba.
Abdul da tun fara kallonta ga dabinon ya kula, da fari ita yake ɗan satar kallo ta madubi, da ya ga ba ta ko kyabtawa sai ya maida hankali kan abinda take kallo, hakan yasa shi kallon hannun Hajia ya sake kallon idanun Aminatu ta madubi.
Yanzu kuma da Hajia ta maida abunta sai ya kula da yadda ta dauke kanta da yanayin rashin jin dadi tare da dan turo bakinta gaba ta jinginar da kanta sosai irin na yaro dai idan yana son abu aka hanna masa, murmushi kawai ya saki yana ci gaba da tukinsa
A ƙofar gidan Baba Mai Shanun aka tsaya dan sauke Hajiar da motar su Baba dake bayansu, Hajia na buɗewa za ta fita Amina ta rigata fita tare da bude bakinta ta kwaranyo aman da ya tuƙota yanzun nan ba tare da sanin dalilinsa ba
Suka je ta shige aji ta zanna ta fito ta samu Muhammat na jiranta, harda abin karin da ta sha mamakin yadda aka yi ya san yinwa take ji, har mamakin kanta take yi kafin ta fito fa sai da ta karya tare da Fido da ta yi dan wake tun da asusuba, ta ci dan waken nan kamar ba gobe, kuma sai gashi tun kafin a fito wata yinwar na yi mata wawushe da kayan ciki, kuma yinwar nan fa idan tana ji bata jin kunyar cin abinci a gaban kowa
Bata san tana ci hannu baka hannu kwarya ba a cikin motar sai da ta cinye tana lumshe ido tana kora ruwa mai sanyi ta dubi wajen Muhammat ta ce" Ama muhammat wannan dambu ya yi dadi, a ina ka siyo shi?"
Muhammat ya yi murmushi yana kadda kai, watau abinda ya faru ogansa ne yace da shi a ina za'a samo abincin gargajiya, dangin abinci dai na gargajiya, idanma da hali harda dadawa
Shine ya je ya samu Matarsa ita kuwa ta kaishi gidan da ake yin dambun nan suka siyo
Yana kai masa yace aa ya je daukan Uman biyu da shi zata so samunsa a wannan lokacin
Har yana mamakin dambu kuma uman biyun?, Sai gashi ta cinye tsaf
Muhammat ya ce" Mom twins ai a gidan wata kawar madame na siyo shi"
Amina ta gyada kai tana fadin" Muhammat ta iya dambu, man kulin nan da ta saka ya yi dadi sosai, mu je mu karro in ajiye da yama na ci, sai na ji ko kulun shi zan ringa ci ba zan gajiya ba, ama ka san wannan dambun ba na gaz bane ko Muhammat?"
Muhammad da ya dauke wuta tunda tace su je su siyo yana tunanin ai bama zai tarki zuwa da ita ba Sir ya nadi hancinsa ya ce" ai da itace take yi, ko man da itace take soyawa, ai bakiga ba tsaftarta, ama yanzun gida zan kaiki sai na koma na gani idan akoy na karro maki"
"Aa Muhammat, ba gida zaka kaini ba gaskiya, zuwa zamu yi na siyowa baba, na tabata idan ya taba dambun nan gobema sai ya sa an siyo masa, mu he mu sayi da yawa a kai masa nasa nima na tafi da nawa gida" Amina ta fada tana buda yar jakarta dan ta ga tanadin jakar, kar aje ba nauyi tana ta maganar aje ta sayi dambu
Waje ya samu ya parker yana fadin" to bara na amsa kira na dawo mu tafi
Daga motar ya fita ya koma gefe ya danna kiran ABDUL da fatan Allah ya sa ya daga da wuri, duda ya san da wahala ya ki dagawar , ama kuma idan aiki ya masa yawa yakan ki dagawarma
Koro masa bayani ya yi dala dala, wanda hakan ya saka ABDUL neman excus ya fito daga dakin meeting din da suke yi da bakinsa yana sake fadin" Wai kai wa ya aikeka fada mata ga inda ka siyo? Muhammat bakinka ba dai magana ba, yanzu idan babu fa?"
Muhammat ya ce" Nima abinda nake ta tunani kennan, kar dai ta yi wannan kuka nata na shiga uku"
ABDUL ya dafe gaban goshinsa ya ce" Kana ji, ka fara kiran matarka, ta je ta yi jiranka a zuba a daure, ka yi ta yawo da ita kafin ku karasa a tabatar an daure komai , kawai a miko maku , ku je wajen baban daga cen sai ka maida ita gida"
Muhammat ya ce" In sha Allah sir"
Har zai katse ya ce" Kana ji?"
Mummamat ya amsa da "eh sir ina ji"
"Muhammat kar ka yi tukin ganganci da ita ka ji?" ABDUL ya fada a hankali yana duban agogon hannunsa.
Muhammat na murmushi ya sake fadin" Bi'izinillah Sir"
Ai ko gidan suka wuce, Muhammat ya fita daga motar ya jira kaɗan matarsa ta miƙo masa dambun sannan suka wuce gidan Baba mai Shanu.
Tunda suka shiga bayan sun gaisa, bata nemi hawa wajen hajia ba, domin ba haka tsakaninsu, idanma ta je zata dauki wulakanci a hannunta ne na gori kala kala,
Da zumudi ta masa tayin shin ta zuba masa dambu zai ci?
Baba ya kalleta da mamaki yace "Uman biyu yau kuma dambu aka yi?"
Da fara'a a fuskarta tace "A'a Baba, ai a hanya ne na sa Muhammat ya tsaya muka siyo, wallahi Baba baka ji dambun ba? Na zuba maka ka ci za ka ji daɗ..."
Yar sauran harafin daya rage ne ya makale dan ita wallahi kallon da Baban yake mata kamar wanda ya ga wani abu a jikinta, irin kallon mamakin nan ne da kuma son gano wani abu........, Dan kallon jikinta ta yi , kar aje ko abincin ta zuzuba a jikinta bata sani ba?
Murmushin da ya saki tare da girgiza kanshi gefe daya ya sake tabbatar mata da lallai fa Baban wani abu yake tunani a kan ta.
Amma tunda ba tambayarshi za ta yi ba sai kawai ba ta ce komai ba aka bar zancen, amma kam yannayin nasa kamar wasu lokuta yaron nan dake sakata a duhu kuma ya barta da duhun kai yake mata shi ma.
Dake kwanan Risala ne yau kuma ba wani damuwa take da shiga harkar yarinyar ba, har fridge din falon ta zo dan daukar kakkaurar madarar da suka rage dazu ita da Fido, dan wallahi idan tana sha ji take kamar za ta tsinka harshenta
Tafiya take tana jan kafafunta dake sanye da silifas masu laushi na daki tana susar bayanta da yar yatsarta, kuma a ganinta darene ai kowa yayi bacci, shiyasa ta fito da riga da wondonta na cotton da suka dan saketa har jikinta na rawa a ciki, iya hula ce a kanta wacce ta tsaya a rabin kanta kamar za ta fadi.
Har ta buda fridge din ta dauko farin bidon ta kalli madarar mai kaurin gaske da sanyi, rufewa tayi ta juya da niyyar komawa dakinta. Hada ido sukayi da Abdul da ya fito daga dakin Biyu zai koma makwancinsa, domin Risala har yanzu bai idasa sake mata ba, dan tunda ta dawo ya kan je dakin ne ya ga lafiyarta, amma yana so ya barta tayi hankali kafin ya sake nuna ita ma matarsa ce, dan ba zai iya da wannan kwaroroton tereren tara masa dangi ba daga abinda bai kai bai kawo ba.........sirrinsa abin boyewa ne da karfin gaske ba abin watsawa bane!
Kyaɓe baki ta fara yi tana lullumshe idanu, sai kuma ta ɓoye madarar a bayanta ta zura hannunta cikin bayan rigar ita a dole kar ya ga me ta zo yi, a nutse ta shiga takawa ba ta sake kallon inda yake ba sai ma gunguni da take kasa kasa a kan me bai yi bacci ba shi din?
Shi dai yana tsaye bai ce mata kala ba har ta shige dakin ta maida kofar ta rufe, wani tattausan murmushi ya saki yana girgiza kai a ranshi ya ayanna 'Uman biyu kennan'
*Bayan kwana biyu* dukansu gidan Baba Rabi'u suka je bikin jikar tasa, duk da ba wani shaƙuwa ce tsakaninsu ba amma dai tare suka tafi bisa bukatar Baba da shi ABDUL din , harma suka kwashe awannin nan tare, ama kowa da inda ya fi karkata, domin Hajia na cen wajen tsofafin wajen sunna nasu shagali na iyaye,Amina na wajen amaren sunna nasu shagali , Risala na nata eriyar tana nata shagalin har lokacin dawowarsu gida yayi
Abdul da kanshi ne yake tuƙasu
Hajia na gaba tare da shi sai ita da Risala a baya, inda Muhamat ke tuƙa Baba da biyu, ya zamto motar sunna bibiyar junna ne, watau daya a gaba daya a baya
Motar shiru da fari ba mai wani magana, sai kuma Hajia da Risala da suka fara yar hirarsu da Abdul ma shi tsakani da Allah yana jin me suke fada amma baya gane gaban zancen, gyara zama Hajia ta sake yi ta buɗa jakarta ta lalubo dabinonta irin na kwalin nan ta fara ci, dan bata ci abincin bikin ba, sam lamarin matar Rabi'u ba classs, yaushe zata barawa mutanen gida su yi girkin abincin auren jikarta? Ga kampani na ma'aikata dake girki kala daban daban maimakun su je su dauko a yi girki a tsare da kiyayewa ...aaa, sai ta bari yan gida suka jamalmala, shi yasa ta kasa ci gaskiya, dan a matsayinta ba zata wanke goma ta durmiya biyar a cikin abincin vilagggssss ba!
Ɗan kallonta Amina tayi daga baya, dan a barin da ABDUL yake ta zauna, tana iya gannin hajiar da abinda take yi
har zata ɗauke idanunta sai kuma ta sake kallon dabinon, irin yanda ya jeru raras a gidanshi yayi ja mai kyau da alamar masifaffen zaƙi, sai kawai ta ji yawunta na wucewa ba tare da ta ankara ba
alamar dai so take yi sosai
Ba ta ankara ba, ba ta kula da ta kasa dauke idanunta akan dabinon ba har saida Hajia ta ci mai isarta ta maida sauran a jaka tana korawa da ruwan roba.
Abdul da tun fara kallonta ga dabinon ya kula, da fari ita yake ɗan satar kallo ta madubi, da ya ga ba ta ko kyabtawa sai ya maida hankali kan abinda take kallo, hakan yasa shi kallon hannun Hajia ya sake kallon idanun Aminatu ta madubi.
Yanzu kuma da Hajia ta maida abunta sai ya kula da yadda ta dauke kanta da yanayin rashin jin dadi tare da dan turo bakinta gaba ta jinginar da kanta sosai irin na yaro dai idan yana son abu aka hanna masa, murmushi kawai ya saki yana ci gaba da tukinsa
A ƙofar gidan Baba Mai Shanun aka tsaya dan sauke Hajiar da motar su Baba dake bayansu, Hajia na buɗewa za ta fita Amina ta rigata fita tare da bude bakinta ta kwaranyo aman da ya tuƙota yanzun nan ba tare da sanin dalilinsa ba