Sashe 45
Ni Zan Ladabi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Baba ya sake tsayawa yana kallonta da fahimtar duka shirunta abinda yake nufi, watau jira take yi ya yi ya gama ta fita ko?
Murmushi ya yi ya ce" Ki sani idan kika fito daga dakin nan sai dai dan ki je ki taimakawa matar jikanki , idan dan ki wulakantata ne Hauwau rigima zata kulu da ni da ke koda ita zata yi sanadiyar da ba zaki yi min takaba ba idan na rigayeki zuwa gidan gaskiya!"
A zabure ta dago daga shashareshin da take tana jira ya gama yayaba mata maganar ta je ta nuna masa ta isa da jikanta ta zuba masa idannuwa da jin furucinsa na karshe wanda shi ya fi komai neman dakatar da bugawar zuciyarta
Ikon Allah, ashe zata wayi gari ta ga halaya irin ta da namiji?
Ashe zata bude ido ta ga wulakanci irin wanda karema ba zai ci ba daga mijinta abin kaunarta Alkalinta a kan wata cen? Ashe zata ga ranar nan ita Hauwau?
Daga haka BABA mai shanu ya sake mikewa ya juya ya fitowarsa ya kama hanyar dakinsa, domin ko menene ya san a yanzu kam zata samu sasaucin farmakin da ake kai mata, domin maganarsa ta nuna masa cewa ya daga mata kafa ne,
Murmushi ya yi yana ayanawa' rikicinma ya zi da sauki masha Allah, Allah kara tausasa halayar Hauwau'
Shigewa ya yi ya rufe abinsa ya sake daukan Alkur'aninsa ya ci gaba daga inda ya tsaya , dan ya zame masa sabo idan bai yi karatun Alkur'ani ba du dare baya iya rintsa idannuwansa da dadi
Jin shirun ya yi yawa ya sakashi cire kansa daga jikin kofar da ya kifa yana sauraron kalaman kakarsa
Abubuwa ne goma da gomiyatara suka taru suka yi masa yawa a cen kasan zuciyarsa
A hankali ya juyo da nufin sake kallon inda ya ajiyeta bayan ya talafeta ya sakata a ruwan zafin da ya farkar da ita daga yar kankannuwar summar da ta yi ta dora kukanta daga inda ta tsaya da tarin Allah ya isan da tana yi yaba nema mata yafiya a wajen Allah , tunda shi dai ya san ba abin a masa Allah ya isa ya yi ba, koda an yi masa ba kamashi zata yi ba tunda ai ba zuwa ya yi ya dage bujenta ya afka ba, sai da aka daura masa ita ai kau?
kukanta ya dauke tsit tunda ta ji muryar Hajia da tsoron kar hajiar ta shigo dakin ta sameta a irin wannan yannayi ta yi tsuru tsuru tana jira ta ga abinda zai sake samunta sanadiyar wannan bawan Allahn da ya shigo mata rayuwa da garaje yake son Kaita kabarinta da ranta ba tare da rai ya bar gangar jikinta ba
Walahi, wata mahaukaciyar faduwar gaba da ta sameta da ta ga ya juyo sai da ta rintse idannuwanta da karfi tana dantse lebenta da korar shedan a duniyarta, dan ta san ba komai zai sakaka jin tsoron kanninka ba irin aikin shedan a duniya
Kallonta yake yi daga tsayen da yake, tarin tambayoyi ne dankam a cikin zuciyarsa, sannin cewa bashida amsosinsu a dole ya dan kara takowa wajen da take a giciye, wani irin kwonciya ita ba a kwonce ba, ita ba a ringeshe ba ta cakumi abin rufa ta cumuimuye jikinta da shi sai kikifta idannuwa take yi kamar an jijiga bera a kwano
Tsoratar da ya ga ta yi a lokacin da ya nufota ya sakashi sake dan dakatawa yana kallonta, ajiyar zuciya take saukewa ta dauke kanta a kansa bakin fitsarar a cune tana kallon gefe hakan ya saka shi sakin dan murmushi sannan ya karasa ya dauki shadar zuwa diner dinsa a hannu ya kabe ya sake juyowa ya yi mata kallon da shi kadai ya san tarin tambayoyin dake cikinsa sannan ya juya bai ce mata komai ba ya fice a dakin
Amina na kallon gefe sai da ta ji rufewar kofar ta maido dubanta a kan kofar
A hankali idannuwanta suka sake cikawa da kwallah ta fashe da wani kukan da sam batada karfin yinsa da karfi
A hankali ta shiga fadin" Innalilahi wa inna ilaihi rajune, wayo Allahna na shiga ukuna, innalilahi wa inna ilaihi rajune ina zan kai wannan abin kunyar? Wayo Allahna ni Amina da girmana da darajata yaro karami ya min wannan wulakancin a kan abinda nake yiwa datijo tanadi? Allah ne zai saka min zalina da ka ci!, Me na yi maka da zafi haka da zaka rabani da prde dina bayan ka san na san aurenmu na yan dakiku ne?, Idan ka saba kaida kake da sabuwar amarya yarinya irinka ka je ka yi shirmenka a cen mana? Yanzu da wani ido zan kalli duniya ta kalle ni? ( Ah to, a dai san a yadda za'ayi ido hudu da jama'ar gidan Ni zan ladabi, inaga harda wace ta dora katuwar tukunyar gashi)
Sosai Amina ta ci kukanta mai ratsa zuciya, kuka na takaici, domin bata taba kawowa a ranta cewa haka zai faru da ita Amina ba , duda ta san an daura mata aure da shi a tunaninta ai baba sai baba , yaro kuwa sai yaro bata taba tunanin cewa yaron nan zai saka hannu daya ya rike mata nata hannayen ya keketata uwa zannin atampa ba sai yau, mema ta taba yi masa? Me na arziki ya taba shiga tsakaninta da shi? A tunaninsa ga banza ya samu ko? Ga yar talakawa marar galihu shine zai wulakantata? In sha Allah ya yi daukan fari ba zai kuma dauka ba koda adashi ne ya zuba!, In sha Allah furucin kakarsa sai dai ya kare a kansa da wace take so ba dai ita ba, zata tsaya tsayin daka ya bata takardarta domin itama bataga ado a yiwa yaro kannin bayanta *Biyaya ba*, me zata ce a gaban mutane ? Yaro dan kannnin bayanta ya sauka a kan ruwan cikinta? Wannan shi ya fi kona mata zuciyarta ya fi sakata kuka, a dole take fashewa da kukan nan ba dan tana so ba
Da kyar ta iya jan jikinta ta sake mayar da kanta bayi
Ruwan da ya cireta a ciki ta zubar ta tara wani mai zafin gaske ama hannunta na iya zama a ciki
Sosai ta jure ta rintse ido ta shiga ta zauna tana ambaton Allah a cen kasan zuciyarta, ta sani ta ji ciwo, domin tana gannin jini jinin dake fita daga gabanta
Tsuru ta yi tana kallon ruwan yana dada dafa mata wajen har ya huce sannan ta fito da jan kafa ta koma ta sake dosanuwa a bakin gadon da ya yiwa wata irin jirkitaciyar shinfida tamkar makaho ne ya shinfida
Sauka ta yi kasa dan kasa zaman gadon ta yi
A ranta ta yi tsaki tana ayana' Ko me Hajia take tunani ne a kaina?, Nima ba shine nawa zabin ba, bani da wani hurumi a cikin lamarin, *wata kokowar* ba tawa bace, *neman na kaina* shi na fi hangowa a gabana, ni da na so na auri mutun tamkar dutse bashi da gaba bale baya?, Dan kawai *alkalamin kadarata* ya ajiyeni a nan ai bai gama zannani ba tunda ba raina ya fita daga gangar jikina ba, kasancewata *BAK'A* kuwa ba dan Allah ya tsaneni ya haliceni haka ba, inma ba mutun da raina mutun ba ai kowa nada tasa baiwa kamar yadda nake da *BAIWATA* ko?, Ba zan taka rawa a wannan *BADAKALAR* ba, idan ya bani takardata na bace sai na zamto tamkar zanen rubutu a saman farin allo a wajenki bi'izinillah'
Radadin dake tsikararta ya saka dole barcin rabi da rabi ne ke surarta, har lokacin sallar asubahi ta zo ta yi iya yinta dan ta mike ta koma bayin ta dauro alwallah aman ta kasa hakan, daga kwoncen da take kafafuwanta a hade take matsar kwallah tana astagfari a zuciyarta, idannuwanta kuwa sun karra yi mata luhu luhu tana tunanin ita kam wa zai agajeta? Wa zai dubeta? Wa zai talafeta? Amare na kwonciya su tashi da miji koda ba mai kula bane yakan dan nuna kularsa a wannan dare, danginka kan kawo maka ziyara a taimakeka, ama ita gashi safiya ta waye bata da gaba bata da baya, tana jin zanninta da danshin da take tsoron ko jinni ne ama ta kasa motsin gyara kanta, kardai ace wannan yaro ya farketa ne ya sakata a uku? Lalle da saidai ta zauna a haka dan babu wani mahalukin da zata yarda ya san abinda take ciki ta tonawa kanta asiri da kanta
Karfe bakwai ta gota, a lokacin ta fara jigatuwa da dukkan wani launi na azabar dake iya saka bawa fadawa a rashin lafiya irin su yinwa, kishirwa, ciwon jiki da kuma uban garin wanda du wata cikakiyar budurwar da ta kai mutuncinta zata iya haduwa da zazabin nan , bale idan akai mata irin hakar da aka yiwa wace ake tunanin ta fitar da biyu daga kasanta a lokaci daya
Kwonkwasawar da ake yi a hankali ana dan saurarawa ya sakata bude lumsasun idannuwanta ta kai dubanta kan kofar sannan ta bude bakinta cen ciki duda ta san da wahala a jita tana amsawa da cewa a shigo
Budewa Baba Lauratu ta yi ta shigo tana salama hadi da wara idannuwanta cikin dakin tana kiran " UMAN biyu? Ina kike ne?"
Ido Amina ta rintse ta kasa amsawa
*NZL PAGE2️⃣8️⃣*
"Amina ki karasa ki zauna mana wai me yake damunki ne yau?" Baba Lauratu ta fada tana tsatsareta da ido, domin gana daya Aminar sai wani abinda bata santa da ita ba take yima mutane a yau , kamar wata mai tashin balagar rashin kunya
Amina ta sada kanta, kunya na neman hadiyeta baki daya
A hankali ta sake dagowa a lokacin da ta ji Mansur ya yi dan gyaran murya ya shigo gaba dayansa ya dubi wajen Hajia da docter ya ce" Baba, ba saman kujera zara zauna ba, ta wuce ciki kawai, Docter ki shiga ciki ki dubata ba zai yiwu ta zauna a falo ba domin ba'a san tashinta daga nan din ba"
Murmushi ya yi ya ce" Ki sani idan kika fito daga dakin nan sai dai dan ki je ki taimakawa matar jikanki , idan dan ki wulakantata ne Hauwau rigima zata kulu da ni da ke koda ita zata yi sanadiyar da ba zaki yi min takaba ba idan na rigayeki zuwa gidan gaskiya!"
A zabure ta dago daga shashareshin da take tana jira ya gama yayaba mata maganar ta je ta nuna masa ta isa da jikanta ta zuba masa idannuwa da jin furucinsa na karshe wanda shi ya fi komai neman dakatar da bugawar zuciyarta
Ikon Allah, ashe zata wayi gari ta ga halaya irin ta da namiji?
Ashe zata bude ido ta ga wulakanci irin wanda karema ba zai ci ba daga mijinta abin kaunarta Alkalinta a kan wata cen? Ashe zata ga ranar nan ita Hauwau?
Daga haka BABA mai shanu ya sake mikewa ya juya ya fitowarsa ya kama hanyar dakinsa, domin ko menene ya san a yanzu kam zata samu sasaucin farmakin da ake kai mata, domin maganarsa ta nuna masa cewa ya daga mata kafa ne,
Murmushi ya yi yana ayanawa' rikicinma ya zi da sauki masha Allah, Allah kara tausasa halayar Hauwau'
Shigewa ya yi ya rufe abinsa ya sake daukan Alkur'aninsa ya ci gaba daga inda ya tsaya , dan ya zame masa sabo idan bai yi karatun Alkur'ani ba du dare baya iya rintsa idannuwansa da dadi
Jin shirun ya yi yawa ya sakashi cire kansa daga jikin kofar da ya kifa yana sauraron kalaman kakarsa
Abubuwa ne goma da gomiyatara suka taru suka yi masa yawa a cen kasan zuciyarsa
A hankali ya juyo da nufin sake kallon inda ya ajiyeta bayan ya talafeta ya sakata a ruwan zafin da ya farkar da ita daga yar kankannuwar summar da ta yi ta dora kukanta daga inda ta tsaya da tarin Allah ya isan da tana yi yaba nema mata yafiya a wajen Allah , tunda shi dai ya san ba abin a masa Allah ya isa ya yi ba, koda an yi masa ba kamashi zata yi ba tunda ai ba zuwa ya yi ya dage bujenta ya afka ba, sai da aka daura masa ita ai kau?
kukanta ya dauke tsit tunda ta ji muryar Hajia da tsoron kar hajiar ta shigo dakin ta sameta a irin wannan yannayi ta yi tsuru tsuru tana jira ta ga abinda zai sake samunta sanadiyar wannan bawan Allahn da ya shigo mata rayuwa da garaje yake son Kaita kabarinta da ranta ba tare da rai ya bar gangar jikinta ba
Walahi, wata mahaukaciyar faduwar gaba da ta sameta da ta ga ya juyo sai da ta rintse idannuwanta da karfi tana dantse lebenta da korar shedan a duniyarta, dan ta san ba komai zai sakaka jin tsoron kanninka ba irin aikin shedan a duniya
Kallonta yake yi daga tsayen da yake, tarin tambayoyi ne dankam a cikin zuciyarsa, sannin cewa bashida amsosinsu a dole ya dan kara takowa wajen da take a giciye, wani irin kwonciya ita ba a kwonce ba, ita ba a ringeshe ba ta cakumi abin rufa ta cumuimuye jikinta da shi sai kikifta idannuwa take yi kamar an jijiga bera a kwano
Tsoratar da ya ga ta yi a lokacin da ya nufota ya sakashi sake dan dakatawa yana kallonta, ajiyar zuciya take saukewa ta dauke kanta a kansa bakin fitsarar a cune tana kallon gefe hakan ya saka shi sakin dan murmushi sannan ya karasa ya dauki shadar zuwa diner dinsa a hannu ya kabe ya sake juyowa ya yi mata kallon da shi kadai ya san tarin tambayoyin dake cikinsa sannan ya juya bai ce mata komai ba ya fice a dakin
Amina na kallon gefe sai da ta ji rufewar kofar ta maido dubanta a kan kofar
A hankali idannuwanta suka sake cikawa da kwallah ta fashe da wani kukan da sam batada karfin yinsa da karfi
A hankali ta shiga fadin" Innalilahi wa inna ilaihi rajune, wayo Allahna na shiga ukuna, innalilahi wa inna ilaihi rajune ina zan kai wannan abin kunyar? Wayo Allahna ni Amina da girmana da darajata yaro karami ya min wannan wulakancin a kan abinda nake yiwa datijo tanadi? Allah ne zai saka min zalina da ka ci!, Me na yi maka da zafi haka da zaka rabani da prde dina bayan ka san na san aurenmu na yan dakiku ne?, Idan ka saba kaida kake da sabuwar amarya yarinya irinka ka je ka yi shirmenka a cen mana? Yanzu da wani ido zan kalli duniya ta kalle ni? ( Ah to, a dai san a yadda za'ayi ido hudu da jama'ar gidan Ni zan ladabi, inaga harda wace ta dora katuwar tukunyar gashi)
Sosai Amina ta ci kukanta mai ratsa zuciya, kuka na takaici, domin bata taba kawowa a ranta cewa haka zai faru da ita Amina ba , duda ta san an daura mata aure da shi a tunaninta ai baba sai baba , yaro kuwa sai yaro bata taba tunanin cewa yaron nan zai saka hannu daya ya rike mata nata hannayen ya keketata uwa zannin atampa ba sai yau, mema ta taba yi masa? Me na arziki ya taba shiga tsakaninta da shi? A tunaninsa ga banza ya samu ko? Ga yar talakawa marar galihu shine zai wulakantata? In sha Allah ya yi daukan fari ba zai kuma dauka ba koda adashi ne ya zuba!, In sha Allah furucin kakarsa sai dai ya kare a kansa da wace take so ba dai ita ba, zata tsaya tsayin daka ya bata takardarta domin itama bataga ado a yiwa yaro kannin bayanta *Biyaya ba*, me zata ce a gaban mutane ? Yaro dan kannnin bayanta ya sauka a kan ruwan cikinta? Wannan shi ya fi kona mata zuciyarta ya fi sakata kuka, a dole take fashewa da kukan nan ba dan tana so ba
Da kyar ta iya jan jikinta ta sake mayar da kanta bayi
Ruwan da ya cireta a ciki ta zubar ta tara wani mai zafin gaske ama hannunta na iya zama a ciki
Sosai ta jure ta rintse ido ta shiga ta zauna tana ambaton Allah a cen kasan zuciyarta, ta sani ta ji ciwo, domin tana gannin jini jinin dake fita daga gabanta
Tsuru ta yi tana kallon ruwan yana dada dafa mata wajen har ya huce sannan ta fito da jan kafa ta koma ta sake dosanuwa a bakin gadon da ya yiwa wata irin jirkitaciyar shinfida tamkar makaho ne ya shinfida
Sauka ta yi kasa dan kasa zaman gadon ta yi
A ranta ta yi tsaki tana ayana' Ko me Hajia take tunani ne a kaina?, Nima ba shine nawa zabin ba, bani da wani hurumi a cikin lamarin, *wata kokowar* ba tawa bace, *neman na kaina* shi na fi hangowa a gabana, ni da na so na auri mutun tamkar dutse bashi da gaba bale baya?, Dan kawai *alkalamin kadarata* ya ajiyeni a nan ai bai gama zannani ba tunda ba raina ya fita daga gangar jikina ba, kasancewata *BAK'A* kuwa ba dan Allah ya tsaneni ya haliceni haka ba, inma ba mutun da raina mutun ba ai kowa nada tasa baiwa kamar yadda nake da *BAIWATA* ko?, Ba zan taka rawa a wannan *BADAKALAR* ba, idan ya bani takardata na bace sai na zamto tamkar zanen rubutu a saman farin allo a wajenki bi'izinillah'
Radadin dake tsikararta ya saka dole barcin rabi da rabi ne ke surarta, har lokacin sallar asubahi ta zo ta yi iya yinta dan ta mike ta koma bayin ta dauro alwallah aman ta kasa hakan, daga kwoncen da take kafafuwanta a hade take matsar kwallah tana astagfari a zuciyarta, idannuwanta kuwa sun karra yi mata luhu luhu tana tunanin ita kam wa zai agajeta? Wa zai dubeta? Wa zai talafeta? Amare na kwonciya su tashi da miji koda ba mai kula bane yakan dan nuna kularsa a wannan dare, danginka kan kawo maka ziyara a taimakeka, ama ita gashi safiya ta waye bata da gaba bata da baya, tana jin zanninta da danshin da take tsoron ko jinni ne ama ta kasa motsin gyara kanta, kardai ace wannan yaro ya farketa ne ya sakata a uku? Lalle da saidai ta zauna a haka dan babu wani mahalukin da zata yarda ya san abinda take ciki ta tonawa kanta asiri da kanta
Karfe bakwai ta gota, a lokacin ta fara jigatuwa da dukkan wani launi na azabar dake iya saka bawa fadawa a rashin lafiya irin su yinwa, kishirwa, ciwon jiki da kuma uban garin wanda du wata cikakiyar budurwar da ta kai mutuncinta zata iya haduwa da zazabin nan , bale idan akai mata irin hakar da aka yiwa wace ake tunanin ta fitar da biyu daga kasanta a lokaci daya
Kwonkwasawar da ake yi a hankali ana dan saurarawa ya sakata bude lumsasun idannuwanta ta kai dubanta kan kofar sannan ta bude bakinta cen ciki duda ta san da wahala a jita tana amsawa da cewa a shigo
Budewa Baba Lauratu ta yi ta shigo tana salama hadi da wara idannuwanta cikin dakin tana kiran " UMAN biyu? Ina kike ne?"
Ido Amina ta rintse ta kasa amsawa
*NZL PAGE2️⃣8️⃣*
"Amina ki karasa ki zauna mana wai me yake damunki ne yau?" Baba Lauratu ta fada tana tsatsareta da ido, domin gana daya Aminar sai wani abinda bata santa da ita ba take yima mutane a yau , kamar wata mai tashin balagar rashin kunya
Amina ta sada kanta, kunya na neman hadiyeta baki daya
A hankali ta sake dagowa a lokacin da ta ji Mansur ya yi dan gyaran murya ya shigo gaba dayansa ya dubi wajen Hajia da docter ya ce" Baba, ba saman kujera zara zauna ba, ta wuce ciki kawai, Docter ki shiga ciki ki dubata ba zai yiwu ta zauna a falo ba domin ba'a san tashinta daga nan din ba"