← Book details Ni Zan Ladabi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 63 OF 83

Sashe 63

Ni Zan Ladabi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Amina ta ce" Why?, Ka san kuwa shi ya rufa mana asiri ni da y'ayana da kanwata har muka kawo yanzu?"

A hankali ya dakata yana kallonta ya ce" Yanzu kuwa ba gani ba, sai na zamto rufin asirinmu baki daya in sha Allah"

"Na dan lokaci?, Na kayadadan lokaci? ABDUL na dan lokaci? Yaya kake tunanin zan yi sake da barci bayan na san ni mai nemo shinkafa ce?, Ba zan kuma yarda Fido ta fada hannun wani azalumin ba in sha Allah, haka kuma ba zan iya amincewa ka korar min wa'inda nake yiwa gyara a yanzu ba, idan ka barni kuma na koma ina nema ana kin kulla ni, tun ba yau ba sana'ata ce, haka kuma inada burin habaka karatuna ABDUL " Amina ta fada tana rage amon muryarta domin ya juyo gaba dayansa yana kallonta ne har ta dire aya

A hankali ya ce" Waye ya ce maki zan barki?"

Amina ta tsatsareshi da ido
Gabanta na wani irin dokawa
Muryarta tana kin fitowa da kyau ta ce" Me, me kake nufi ne?"

ABDUL ya juyar da kansa gefe yana basar da maganat, sannan ya sake juyowa yana kallonta ya ce" Manta "

Amina ta sake matsowa tana kallonsa ta ce" Na manta me ABDUL? Me zan manta?, Ka min magana a kan bayanin nan, ni fa bana son magana a rufe!"

"Ki ringa tausasa lafuzanki mana Aunty, mu tafi kin ji?" Ya sake fada a tausashe

Amina ta sake neman tuburewa tana kallonsa, irin ai itace baba ita ya dace ta ringa masa irin haka ba wani shi ba

Tana kallonsa ta ce" Ka ga , ba wani maganar tausasawa babe ko rashinsa, magana ce ta gaskiya, dama Baba tace na bari matarka ta tare, ta tare ai har na ga aikin tarewa kun aikata kau? Yanzu ni sai ka salameni na je na ji da rayuwata, na je na ji da ta y'ayana da ta kanwata, bana so Biyu su ci gaba da shagalta da abinda ba dindindin ba, ni kawai ka..............."

Da wata irin murya ,a mugun kausashe, ya sake matsowa yana dora dan yatsarsa daya a saman lebenta ya ce" Cewa na yi, Ki tausasa harshenki, sannan ku tauna kalamanki, bana son aiki irin na yarinta da shirme a nan"

Amina ta zarro idannuwanta ta bude bakinta zata sake yin magana ta ga ya watsa mata wani mahaukacin kallo mai dauke da namijin hatsari, mai firgice da yaren zane,
Sannan ya saka yan yatsotsinsa biyu rak ya rike lebenta da su ya ce" SHUIIIIIIIIIIIIIIIIITTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTT!"

TAKAICI, MAMAKI, BACIN RAI, TASHIN HANKALI suka hadun mata, suka hannata barkata komai,yawo idannuwanta ke yi a saman fuskarsa, hadewar fuskarsa ya girmami tunaninta,

Hannunta ta saka ta janye lebenta da kyar , ta sake zubawa fuskarsa ido, sannan ta juya da wani irin gudu gudu,sauri sauri ta koma hanyar da suka biyoita da shi tana rufe bakinta da hanna kanta kuka a gaban yaro!

Da ido Masu gadi sukabita, harda Muhammat dake shirin tafia nasa gidan

Murmushi ya yi da ya tuno furucin ABDUL na dazu yana tabatar da gaskiyarsa ashe, maman twins ba dai rigima ba

Tana bude falonta ta shiga suka yi ido hudu da Hindatu tana sake saka turaren wuta

Huci take yi na wanda ke son fashewa da kuka tana kallon Hindatun ta ce"
ABDUL ya sake cije lebensa da bacin rai ya ce" Yana nan da ransa , ka gane abin ya wuce tunanin mutum, ya zamto talaka bashida wani gata sai na Allah, wa'inda suka isa su tsawata sun nade hannu kowa na tsoron tofawa, mahaifiyar yaron kanta a ha'ula'i take, ai ba maganar aure cewa ya yi idan na fito da ita ya mata saki uku, ni kuwa na fito da itan a summe"

"Saki?, Uku? Hasbunnalah, wannan wani irin marat imani ne? Wani irin rashin godiyar Allah ne? Ni ina nan haihuwar nake nema ido rufe Allah bai kawo ba ka gaan sameta a wani wajen ana wukakantawa? Dan Adam bashida godiyar Allah, wanin baya jin tsoron Allah sam"

ABDUL ya sake daukan file dinta ya bude yana komawa ya zauna ya ce" Allah zai yi maganinsu, kwana nawa ka daukan mana ne?"

Mansur ya ce" Na daukar mata kwana uku ne, idan komai ya tafi daidia jinninta ya daidaita in sha Allah zan salameta"

ABDUL ya gyada kansa yana duba duka kaf magungunnan da aka rubuta mata harda na kafe ruwan nono dan kar su dameta da suba da zogi

Sosai ya gamsu da komai ya ajiye yana sake zama yana ta cicira tunanin dake zuciyarsa, sai dai ba zai fadawa kowa yanzu ba, zai bari ne har ya tabatar sannan ya san abin yi, shin yaya zasu rayu bayan bata son rayuwa da shi? Idan kuwa har furen dake tare da ita ya yi tsiro har ya yabanya wace irin gagarumar rigima ke gabansaM

"Hum" yace har sai da Mansur ya dube shi yana ajiye masa jus yana fadin" Man kayanka sun baci gashi an kusa shiga masalaci, ya dace ka je ka kimtsa"

Ajiyar zuciya ya sauke ya mike yana masa salama da nufin sai sun hadu da yama idan ya dawo daukan Uman biyu

Tafiyarsa ya yi ya bar Baba da biyu dan ya san sa wuce masalacin tare , shi kuma ya koma gida

A cikin dakin kuwa Baba ke yiwa Amina nasiha kasa kasa, Firdausi kuwa ta samu barcin wahala tunda ta saka hannunta cikin na yayarta sai da barcin ya kwashetama Amina ta janye a hankali ta zauna aa gefenta tana kallonta

Kasa kasa Baba ya ce" Haka nata salon kadarar yake, kuma kin sam cewa Allah baya dorawa bawa abinda ya fi karfinsa, ki daina kuka ki bata kwaron gwuiwa, ta haka sai ta shanye dukkan wahalar har ki ga ta mike kamar ba ita ba kin ji Uman biyu?"

Amina ta gyada kanta tana sake share hawayen nata, idannuwanta har sun kumburo dan kuka, bata taba jin maraici har cikin kirjintaba irin na yau, kafin Abdul ya fito da Firdausi babu irin abinda bata tuna ba a duniyarta, ta yi kuka da boda kamar zata fasa motar

Shigowar Baba tana rike da bokici da yan kayayakin dake ciki , Husaini na yi mata surutu ya saka Baba sakin murmushi yana kallon Hasan ya ce" Yau sam ba fara'a a fuskar mai tsuntsaye, Allah dai ya sanyaya fushinsa"

Baba ta yi murmushi itama tana sake gyaraa matashin kan Firdausi ta zauna tana kyatu ta kama Hassan ta zaunar ta ce" Allah ubangiji yaa sa karshen wahalar kennan"

Da amen suka amsa, du suka ci gaba da zama har karfe goma sha biyu ta yi suka fice tare da Muhammat da ya dawo daukansu dan kaisu masalaci

Da yama da kyar Uman biyu ta fito , har zuwa lokacin Firdausi bata farka ba, kuma ance idan ta farka ba za'a bata abinci ba , sai dai ta sha jus

Ji take abin nan sam bai dace ba ace za'a rabata da kanwarta, shi dai a bayan motar a zaune waya yake amsawa , yau sam bai leka nema ba, gashi da zafin nema, suka nufi gidan Baba domin yau bai je ba, rabonsa da Hajia kwana biyar ciffffffffff

A asibiti

Tsaye suke a kanta, docter da Mansur sunna bata baki a kan kin amsar koda bakin ruwa ne ta sha, ta nuna Alhamdulilah bata jin cin komai

Docter ta janyo kujera ta zauna tana kallonta ta ringa yi mata nasiha da bada baki da nuna mata mahinmancin lafiyarta
Ama Firdausi sam ta nuna bata jin yinwa ne

Da kula Docter ta dubi Docter Mansur ta ce" Likita, inaga sai an tabo makusancinta, ka san ba zai yiwu ta ki shan jus din nan ba, shi zai taimaka mata samun karfin jikinta kafin ta samu iska ta fara cin dan salak da dai wani abin marar nauyi ko?"

Kai MANSUR ya gyada, cike da tausayi yana kallonta ya ce" Na gode sosai Docter da kika zo, zan dubata....."

Docter ta amsa ta mike ta tafi,

Mansur ya amshi jus din dake hannun Nurse din da ta shiyata da komai , itama ta fita , ya maida dubanta kan Fido da kanta ke sade tana kallon waje daya

Aa sanyaye ya ce"baki dangana ba Firdausi?"

Fido ta dago a hankali ta yi masa kallo daya ta sake sada kanta, muryarta a sanyaye ta ce" Dangana da me likita?"

Mansur ya ce" Da rashin da muka samu, ko kuma aban yaren ne mai baban laifin?"

Sake dagowa ta yi tana kallonsa, ta sake soke kaanta

Mansur ya sauke ajiyar zuciya ya ce" Akoy ciwo Firdausi, akoy ciwo matuka, ama ya dace ki yi duba da jama'ar dake zagaye da ke masu zubar da hawayensu dominki, a kan laifin daya tak, kar ki hukunta kanki da hukuncin da zai damu masoyanki, kin ga wace zata fara jigata yayarki ce, a gangaro kan biyunki, mu da kanmu sai hankakinmu yaa tashi Firdausi, karma ki saka damuwar wani a ranki ki kasa nutsuwa kin ji?"

Firdausi ta sauke numfashi yinwar fa na cinta, a sanyaye ta ce" Docter, dama wata sharaar ai sai a kiyama......., Luuuu luuuuuuuuuu
Nake gani kar aje nima mutuwar zan yi na shagalta da kurbar juss, shi yasa nake ta Adu'a a zuciyata......ka ga kuma biyu ba nawa bane ba fa, na uman biyu ne"

Tausayinta, madaukakin tausayinta, shi ya fi komai rinjayarsa,
Da dabaru irin na likitoci ya samu ta amshi juss din har ta yi masa sha na mamaki

Tana gama sha ta koma barci domin akoy allurorin barci a lamarin dole sai da hutu
Huci take yi na wanda ke daf da fashewa da kuka tana kallon Hindatu ta ce" Hindatu, halo turaran wutar ne? Nace maku juwa yake sakani Hindatu kin cika masa muski hawar mun kai yake yi Hindatu, wayo Allahna Hindatu". Sai kawai Amina ta fashe da kuka tana zama a kasa kamar wata yar baby

Ido Hindatun ta zarro tana yin waje da turaran ta hanyar kicin da gudu sannan ta dawo hankali tashe sai fadi take"Na shiga uku na lalace, Hajia,dan Allah ki yi hakuri ban san bakya sonsa ba HAJIA, dan Allah ki yi hakuri ki daina kukan na shiga ukuna"
Chapter 63 · 0% Book details