Sashe 73
Ni Zan Ladabi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sunna zuwa suka tarar da Fido din zaunenta ga su jus a gabanta ama bata dauki ko daya ba, hasalima kamar a takure take a zaunen da take har suka zo ta mike suka yi masa salama suka wuce dan zuwa wajen da zata fara nata karatun da sauransu
Kwonci tashi, a hankali Amina ta ci gaba da rainon cikinta,
A fannin ci, da sha, da sutura sai dai tace abin har ya wuce tunaninta, daga gidan Baba mai shanuma ya zamto bini bini za'a turo mata da kayan kwalam da makulashe, irin abubuwan kwadayin da wasu har mamakin inda aka samo su ke kamata, haka kuma du ranar Juma'a Baban ne da kansa da Hania zasu zo gidan, duda ba maganar dake hadasu da Hajiar sai tsatsareta da ido da zatana yi da yawan fada mata ta ringa kiyayewa , ta ringa cin abu kaza ta daina cin kaza, daga hala ba wata hirar kuma a tsakaninsu, karshema takan tafi lamuran gabanta ne sai Baba ne zai baje abinsa ya wuni a gidan a sha hira tare, kuma harda Risala yake sakawa a kirawo yana tsakiya abinsa idan ya dauko wannan hirar ya tsoma su baki daya, wanin su amsa gaba dayansu, wannin kuwa wata ta yi shiru, kowace dai da kalar nata isar da kalar nata nuna kulawar da sauransu, har sai yama ta yi a mayar da shi gida abinsa, wani lokacin Biyu su bi shi, wani lokacin kuwa su kiya su nuna gobe asabar abansu na gida zasu buga game da shi
Abinda ke damunta kuwa ta gwamaci barawa kanta a zuciyarta, domin bata san me zata fasara haka ba
Kiri kiri ABDUL ya dauki kwananta ya hadewa Risala
Babu abinda ya dame shi da ita
Ba gaba yake yi mata ba, ama kuma babu irin wancen kulawar
Rabonsa da ya shiga dakinta tub ranar da aka samu matsalar nan a gidan Baba
Tun daga ranar tana tunanin ko dakin biyu ya daina shiga ya masu addu'a
Gaba daya ya yi watsi da ita
Abinda yake mata a rayuwa shine ci, sha sutura, bayan wannan idan ka ga ya mata magana ido da ido dan ya tambayeta ne yana fatan cikinsa lafiya kalau? Yana fatan tana tune da ranar awonta, awon da ya fita irgen lokacinsa, har mamaki take yi a kan haka
Risala sai tunkaho da daga kai take yi mata a cikin gida, domin ba dai an fada mata ba, da idannuwanta ta isa ta gane miji ya mayar da ita banza a cikin gida, gaba daya ta zuba masa ido ne, jira take yi ta haihu sai ta bashi gidansa ya yi yadda yake so da wadda yake so!
Yau kwanakin watan musulunci ashirin da daya, haka watanin cikinta wata bakwai ne
cikinta ya riga ya fito da kansa, ba maganar buya, domin ko tafia take yi shine a gaba, shi yasa sam bata fita in ba abu ya zama dole ba balema irin girman da ya yi ne abin a dubeta a yi mata sannu, dan ya kai girman cikin da ya isa haihuwa, shi yasa take komai a hankali da kuma lalaba lafiyarta, idan Baba ya zo nema yake sakata dole yawatawa a cikin gidan wai su je su yiwa ma'aikata ziyara, ba dan ta so ba, a dole take binsa dan bata da yadda zata yi masa
Ya zamana a yanzu ABDUL kan ajiye fitar juma'a koda bayan sallar juma'ar ne ya yi tsaye daga dakinsa yana hangensu
Yakan yi murmushi mai taushi yana kallonta n cikinta
A irgensa, nan da wata biyu da yan kwanaki abinda ke cikinta zai fito duniya , shima zai rungumi baby a hannunsa daga Aminansa
Harta da ranar da aka bata a asibiti na haihuwa ya ware sati kafin ranar, da kuma sati biyu bayan ranar, koda takan haihu kafin lokacin, ko kuma bayan lokacin in sha Allah, ba zai fita ko nan da nan ba bi'izinillah, zai zauna kusa da ita har ta sauka ........ In dai yana raye
_________________________________
Kamar yadda aka saba, sabon sati na sabon watan watani takwas din Amina da ciki
A juma'ar yau falon nata ya dauki Harda ABDUL ne, sakamakon zazabin da ta tashi da shi, wanda Firsausi kafin ta fita ta sanar masa, domin jikinta da zafi sosai, gashi ba'a so mai ciki da irin haka, dan yana gagawar ratsa babyn da ita kanta, yana haifar da matsala
Daga kicin ta fito rike da plate din da ta je ta yanyankowa su Baba fruits ba tare da sun san abinda ta shiha yi kennan ba, da Hajiar da kanta ce zata hannata, domin Hajia bata hada cikin nan da komai a duniya
A hankali ya mike ya nufeta dan amsar plat din, domin baba ne ta ciko, kuma tafiyarta kanta wata iri ce baiwar Allah, gajiya na tatare da ita a bayane ba a boye ba
A hankali ya rike Plat din hadi da hannunta, hakan ya sa ta dago manyan idannuwanta ta saka cikin nasa, dama abinda yake bukata kennan
A saman lebensa ya ce" Yaya jikin ki?"
Amina ta lumshe idannuwanta itama a saman lebenta ta ce" Ya dameka ne?"
ABDUL ya tsatsareta da ido ya ce" Ya fi damuna fiye da kowa a duniya "
Amina ta tabe bakinta, kasa kasa ta ce" Ka fafi gaskiya , ko kana tunanin Risala ke gabanka?"
Idannuwanta ya tsatsare da ido, so yake yi ya ga abinda Mansur ke fada masa dangane da ita da shi, ama shi a kulun ganu yake yi bata ra'ayinsa bata ra'ayin kasancewa kusa da shi
A hankali ya budi Baki zai yi magana Kukan Fido ya karade wajen, ta shigo da gudu hannunta saman kanta tana kuka, ta rasa ina zata nufa domin Hajia dai ta san ba wace ke ra'ayin janta a jikinta bace
Da sauri ya Rike Amina gannin zata je da sauri Wajen Fidon da ta nufi Baba da ya mike yana kiranta da salalami yana tambayarta lafiya?
Zaunar da Amina ya yi saman kujera sannan ya dubi Fido dake kukanta hankalinta tashe tana wani irin haki
ABDUL ya ce" Firdausi menene kike kuka haka, zo nan taho nan na ji?"
Firdausi ta karasa inda yake ta duka kanta a kasa, Hajia dake dadana wayarta ta dan dago ta sake duban Fido, ta sake maida kanta kan wayar tana ci gaba da dadanawa
Firdausi na shashekar kuka ta ce" Dady, wai , wai Mudi ne ya tarda ni cen wajen koyon girkina, yau muna koyawa baki ne , muna tsakiya da aikinmu ya cewa security wai shi mijina ne, aka barshi ya shigo, a cikin mutane ya ringa zazagina yana ce min wai karuwa ce ni na kashe aurena ina yawon cakuduwa da maza, na kashe masa ya'yansa har biyu ina zaune ina yawon ta zubar, Dady ana rikeshi yana fadin a barshi sai ya yi ajalina, da kyar Bintu ta fitar da ni a motarta ta kawo ni gida "
Da mamaki ABDUL da ya mantama waye wai Mudi, dan shi ba wani rike sunnan yaron ya yi ba ya ce" Mudi? Tsohon Mijinki Kennan?"
Fido ta gyada kanta tana sake tare hawayenta
Amina haka jikinta ke rawa, wata irin dunkulaliyar Ashar ke makale a wuyanta, wace a zaunen da take gwara ta saka ihu da ta yita, domin irin zaburariyar ashar din nan ce mai sakawa a maka kallon lalatace komai girmanka da darajarka, ji take tamkar ta hira ta je inda yake yau ta kwakulo idon marar kunya!
ABDUL da bacin rai ya dubi Baba dake tambayarsa wai yaron nan bashida kunya ne ko me yake nema da mutane ne kuma?
ABDUL ya dan dantse lebensa na kasa, sannan ya saki ya ce" Bashida kunya, kuma bai gane an kyale shi ne dan takardar rashin kunyarsa bata kai inda za'a yi fito na fito da shi ba, ama yanzu na amshi tayin, ina zuwa!"
Mikewar da ya yi daga zaune ya saka Hajia mayar da wayar gefe tana kallonsa a tausashe ta ce" Honorable ina zaka je?"
ABDUL ya dakata dan ya dan shine ai Honorable din dai da Hajia ke kira kulun, Aminama da ta fara murmushi tana jin inama a je da ita ta ga yadda ABDUL zai ci uban dan iskan cen dakatawar ta yi tana kallonsa ta ji ya ce" Zan je na dawo ne"
Hajia ta yi murmushi tana fadin" Koma ka zauna, kai da matarka bata da lafiya?, Wannan ai ba aikinka bane, ka ga ya kule kansa fa yaron da kansa, tunda yace zai halakata a cikin jama'a, kuma ya je har wajen da yake na gidansu ya zageta, tunda wajenka ne kai kuma Uba kake a wajenta, sannan ya yi karyace karyace da yawa.......ka barshi kawai ya kule kansa ai"
Alkali ya zuba mata ido, yadda take maganarta a nutse hankali kwonce ya san abin kansa zai karkato
Ai kuwa ta dube shi tana daukan wayarsa da sam bai cika anfani da ita ba ta mika masa ta ce" Alkali kana ji jikarka za'a kashe, ka dan yi wani abu mana"
Amina dake zaune sai da ta ji kamar numfashinta zai katse dan wani abu dake ratsa mata zuciya da jiki
Alkali kuwa murmushi ya yi yana dan rage girman idannuwansa dan ya lalubo sunna, ama ya kasa a dole ya mikawa Amina da ta fi kusa da shi ya ce" Uman biyu, lalubo min DPO Mustapha na sojojin ba polisse ba"
ABDUL ya saki murmushi yana gannin yadda Amina ke danne dariyarta, wada karars ya fahimci dariyar farin ciki take son saki ama tana hanna kanta har ta lalubo ta dannawa Baba kira sannan ta kara matsawa tana sauraron maganar da Baba da DPO
Tsaf Baban ya gama bayaninsa, amsar da DPO ya bayar da tambayar su Hajia da Honorable ya saka ABDUL sake yin murmushi, watau gaba daya makaraban Hajia Honorable suke kiransa, bayan kasa ya gama nikawa wace zai watsa masu a ido, domin shi ba dan siyasa bane, ba kuma zai tsaya a takarar neman kujerar gwamna ba, bashida ra'ayin hakan gaskiya
Kwonci tashi, a hankali Amina ta ci gaba da rainon cikinta,
A fannin ci, da sha, da sutura sai dai tace abin har ya wuce tunaninta, daga gidan Baba mai shanuma ya zamto bini bini za'a turo mata da kayan kwalam da makulashe, irin abubuwan kwadayin da wasu har mamakin inda aka samo su ke kamata, haka kuma du ranar Juma'a Baban ne da kansa da Hania zasu zo gidan, duda ba maganar dake hadasu da Hajiar sai tsatsareta da ido da zatana yi da yawan fada mata ta ringa kiyayewa , ta ringa cin abu kaza ta daina cin kaza, daga hala ba wata hirar kuma a tsakaninsu, karshema takan tafi lamuran gabanta ne sai Baba ne zai baje abinsa ya wuni a gidan a sha hira tare, kuma harda Risala yake sakawa a kirawo yana tsakiya abinsa idan ya dauko wannan hirar ya tsoma su baki daya, wanin su amsa gaba dayansu, wannin kuwa wata ta yi shiru, kowace dai da kalar nata isar da kalar nata nuna kulawar da sauransu, har sai yama ta yi a mayar da shi gida abinsa, wani lokacin Biyu su bi shi, wani lokacin kuwa su kiya su nuna gobe asabar abansu na gida zasu buga game da shi
Abinda ke damunta kuwa ta gwamaci barawa kanta a zuciyarta, domin bata san me zata fasara haka ba
Kiri kiri ABDUL ya dauki kwananta ya hadewa Risala
Babu abinda ya dame shi da ita
Ba gaba yake yi mata ba, ama kuma babu irin wancen kulawar
Rabonsa da ya shiga dakinta tub ranar da aka samu matsalar nan a gidan Baba
Tun daga ranar tana tunanin ko dakin biyu ya daina shiga ya masu addu'a
Gaba daya ya yi watsi da ita
Abinda yake mata a rayuwa shine ci, sha sutura, bayan wannan idan ka ga ya mata magana ido da ido dan ya tambayeta ne yana fatan cikinsa lafiya kalau? Yana fatan tana tune da ranar awonta, awon da ya fita irgen lokacinsa, har mamaki take yi a kan haka
Risala sai tunkaho da daga kai take yi mata a cikin gida, domin ba dai an fada mata ba, da idannuwanta ta isa ta gane miji ya mayar da ita banza a cikin gida, gaba daya ta zuba masa ido ne, jira take yi ta haihu sai ta bashi gidansa ya yi yadda yake so da wadda yake so!
Yau kwanakin watan musulunci ashirin da daya, haka watanin cikinta wata bakwai ne
cikinta ya riga ya fito da kansa, ba maganar buya, domin ko tafia take yi shine a gaba, shi yasa sam bata fita in ba abu ya zama dole ba balema irin girman da ya yi ne abin a dubeta a yi mata sannu, dan ya kai girman cikin da ya isa haihuwa, shi yasa take komai a hankali da kuma lalaba lafiyarta, idan Baba ya zo nema yake sakata dole yawatawa a cikin gidan wai su je su yiwa ma'aikata ziyara, ba dan ta so ba, a dole take binsa dan bata da yadda zata yi masa
Ya zamana a yanzu ABDUL kan ajiye fitar juma'a koda bayan sallar juma'ar ne ya yi tsaye daga dakinsa yana hangensu
Yakan yi murmushi mai taushi yana kallonta n cikinta
A irgensa, nan da wata biyu da yan kwanaki abinda ke cikinta zai fito duniya , shima zai rungumi baby a hannunsa daga Aminansa
Harta da ranar da aka bata a asibiti na haihuwa ya ware sati kafin ranar, da kuma sati biyu bayan ranar, koda takan haihu kafin lokacin, ko kuma bayan lokacin in sha Allah, ba zai fita ko nan da nan ba bi'izinillah, zai zauna kusa da ita har ta sauka ........ In dai yana raye
_________________________________
Kamar yadda aka saba, sabon sati na sabon watan watani takwas din Amina da ciki
A juma'ar yau falon nata ya dauki Harda ABDUL ne, sakamakon zazabin da ta tashi da shi, wanda Firsausi kafin ta fita ta sanar masa, domin jikinta da zafi sosai, gashi ba'a so mai ciki da irin haka, dan yana gagawar ratsa babyn da ita kanta, yana haifar da matsala
Daga kicin ta fito rike da plate din da ta je ta yanyankowa su Baba fruits ba tare da sun san abinda ta shiha yi kennan ba, da Hajiar da kanta ce zata hannata, domin Hajia bata hada cikin nan da komai a duniya
A hankali ya mike ya nufeta dan amsar plat din, domin baba ne ta ciko, kuma tafiyarta kanta wata iri ce baiwar Allah, gajiya na tatare da ita a bayane ba a boye ba
A hankali ya rike Plat din hadi da hannunta, hakan ya sa ta dago manyan idannuwanta ta saka cikin nasa, dama abinda yake bukata kennan
A saman lebensa ya ce" Yaya jikin ki?"
Amina ta lumshe idannuwanta itama a saman lebenta ta ce" Ya dameka ne?"
ABDUL ya tsatsareta da ido ya ce" Ya fi damuna fiye da kowa a duniya "
Amina ta tabe bakinta, kasa kasa ta ce" Ka fafi gaskiya , ko kana tunanin Risala ke gabanka?"
Idannuwanta ya tsatsare da ido, so yake yi ya ga abinda Mansur ke fada masa dangane da ita da shi, ama shi a kulun ganu yake yi bata ra'ayinsa bata ra'ayin kasancewa kusa da shi
A hankali ya budi Baki zai yi magana Kukan Fido ya karade wajen, ta shigo da gudu hannunta saman kanta tana kuka, ta rasa ina zata nufa domin Hajia dai ta san ba wace ke ra'ayin janta a jikinta bace
Da sauri ya Rike Amina gannin zata je da sauri Wajen Fidon da ta nufi Baba da ya mike yana kiranta da salalami yana tambayarta lafiya?
Zaunar da Amina ya yi saman kujera sannan ya dubi Fido dake kukanta hankalinta tashe tana wani irin haki
ABDUL ya ce" Firdausi menene kike kuka haka, zo nan taho nan na ji?"
Firdausi ta karasa inda yake ta duka kanta a kasa, Hajia dake dadana wayarta ta dan dago ta sake duban Fido, ta sake maida kanta kan wayar tana ci gaba da dadanawa
Firdausi na shashekar kuka ta ce" Dady, wai , wai Mudi ne ya tarda ni cen wajen koyon girkina, yau muna koyawa baki ne , muna tsakiya da aikinmu ya cewa security wai shi mijina ne, aka barshi ya shigo, a cikin mutane ya ringa zazagina yana ce min wai karuwa ce ni na kashe aurena ina yawon cakuduwa da maza, na kashe masa ya'yansa har biyu ina zaune ina yawon ta zubar, Dady ana rikeshi yana fadin a barshi sai ya yi ajalina, da kyar Bintu ta fitar da ni a motarta ta kawo ni gida "
Da mamaki ABDUL da ya mantama waye wai Mudi, dan shi ba wani rike sunnan yaron ya yi ba ya ce" Mudi? Tsohon Mijinki Kennan?"
Fido ta gyada kanta tana sake tare hawayenta
Amina haka jikinta ke rawa, wata irin dunkulaliyar Ashar ke makale a wuyanta, wace a zaunen da take gwara ta saka ihu da ta yita, domin irin zaburariyar ashar din nan ce mai sakawa a maka kallon lalatace komai girmanka da darajarka, ji take tamkar ta hira ta je inda yake yau ta kwakulo idon marar kunya!
ABDUL da bacin rai ya dubi Baba dake tambayarsa wai yaron nan bashida kunya ne ko me yake nema da mutane ne kuma?
ABDUL ya dan dantse lebensa na kasa, sannan ya saki ya ce" Bashida kunya, kuma bai gane an kyale shi ne dan takardar rashin kunyarsa bata kai inda za'a yi fito na fito da shi ba, ama yanzu na amshi tayin, ina zuwa!"
Mikewar da ya yi daga zaune ya saka Hajia mayar da wayar gefe tana kallonsa a tausashe ta ce" Honorable ina zaka je?"
ABDUL ya dakata dan ya dan shine ai Honorable din dai da Hajia ke kira kulun, Aminama da ta fara murmushi tana jin inama a je da ita ta ga yadda ABDUL zai ci uban dan iskan cen dakatawar ta yi tana kallonsa ta ji ya ce" Zan je na dawo ne"
Hajia ta yi murmushi tana fadin" Koma ka zauna, kai da matarka bata da lafiya?, Wannan ai ba aikinka bane, ka ga ya kule kansa fa yaron da kansa, tunda yace zai halakata a cikin jama'a, kuma ya je har wajen da yake na gidansu ya zageta, tunda wajenka ne kai kuma Uba kake a wajenta, sannan ya yi karyace karyace da yawa.......ka barshi kawai ya kule kansa ai"
Alkali ya zuba mata ido, yadda take maganarta a nutse hankali kwonce ya san abin kansa zai karkato
Ai kuwa ta dube shi tana daukan wayarsa da sam bai cika anfani da ita ba ta mika masa ta ce" Alkali kana ji jikarka za'a kashe, ka dan yi wani abu mana"
Amina dake zaune sai da ta ji kamar numfashinta zai katse dan wani abu dake ratsa mata zuciya da jiki
Alkali kuwa murmushi ya yi yana dan rage girman idannuwansa dan ya lalubo sunna, ama ya kasa a dole ya mikawa Amina da ta fi kusa da shi ya ce" Uman biyu, lalubo min DPO Mustapha na sojojin ba polisse ba"
ABDUL ya saki murmushi yana gannin yadda Amina ke danne dariyarta, wada karars ya fahimci dariyar farin ciki take son saki ama tana hanna kanta har ta lalubo ta dannawa Baba kira sannan ta kara matsawa tana sauraron maganar da Baba da DPO
Tsaf Baban ya gama bayaninsa, amsar da DPO ya bayar da tambayar su Hajia da Honorable ya saka ABDUL sake yin murmushi, watau gaba daya makaraban Hajia Honorable suke kiransa, bayan kasa ya gama nikawa wace zai watsa masu a ido, domin shi ba dan siyasa bane, ba kuma zai tsaya a takarar neman kujerar gwamna ba, bashida ra'ayin hakan gaskiya