Sashe 6
Ni Zan Ladabi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Asalamu alaikum Hajia" muryar wanda ya kawo mata agaji a dazu ta daki dodon kunnenta da yannayi na ja baya ba matsewar waje ba
Juyowa ta yi sai ta ga daya daga cikin ma'aikacin wajen rike da ledoji jigi jigi kusa da likitan
A tausashe sosai ya furta" ki yi hakuri na san ke matar aure ce, ba wani abu bane dama dan na tambaya ne Ina fata ya saurareki?"
Amina ta juyar da kanta tana shaƙar iskar magariba dake hurowa a sanyaye ta ce" Ban samu ganninsa ba, sia dansa, na fadawa ɗan nasa sakon na san zai sanar masa"
Dan jim ya yi , sai kuma ya ce" Dansa kuma?"
Amina ta gyada masa kai tana dubansa
A hankali ya ce" Ai shine mai wajen fa, shi daya muka baro a ciki"
Sai da ta saki baki da mamaki, ta waiga ta sake waigawa ta kuma kallonsa, ama sai ta barawa kanta abinda ya bata mamakin a zuciyarta , karshema sai zuba ido tana kallon yadda yake ta kokarin sai Hasan ya bashi hannu ama ina, a murtuke fuskar nan du inda rigima take ta tatare a saman fuskarsa, Husaini ne ya sake sosai da shi yana amsa tambayarsa, sai kuma ta juya ta fice gannin Aban saudat ashe dai bai tafin ba ta karasa tana kawar da fuskarta gannin ya fito a adaidaitar yana tambayar lafiya kamar wace ta yi kuka?
Gannin ana miko masa ledojin ta juyo da mamaki tana fadin"
Yaya kuke gannin salon zai je? Yaya kuke hangen cakwakiyar lamarin? Ku zo mu je sisters🥰🥰🥰🥰😍😍😍😍
🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️
_*NI ZAN LADABI*_
🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️
*NA*
*SAJIDA NIGER*
Asalamu alaikum wa rahamatullah, makaranta novel dina gani na dawo da sabon takarda, sabuwar tafia, sabon salo mai dauke da darusan rayuwa, da karfin ikon sunnah, da gwagwarmaya da kula kula, rayuwa ce irin ta talaka bawan Allah dake gannin hawa da sauka dan ya rayu da mutuncinsa, rayuwa ce ta Mace mai dauke da hatsari, sadaukarwa, Biyaya da karfi.......zai zo maku da shafuka na gyara tun daga kan fatar jiki, ppart, sirika irin na cikin kurya a gangaro kan sabulai na sana'a da kuma turaran HUMURA wace kowace mace zata iya yiwa kanta tsumamen hadin tada hankalin mai gida
Wannan Novel na kudi ne ba free bane
Yan Nigeria jama'ata ga naku : 500 Naira
account number: 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi GT Bank sai ka turo shedar biyanka ta numberta kamar haka +227 93811618 SAJIDA NIGER
Wa'inda suke da matsala da harkar banki zasu iya turo kati ta numberna, ko su yi pos in sha Allah, kuma a kan number nawa kamar haka 93811618..... Sai kun zo
Jama'ata yan NIGER ga naku : Dala dari , 500 francs cefa ta katin AIRTEL ko SAHELCOM ka turo ta numberna kamar haka 93811618 sai na saka ka
*NA gode sosai, Allah ya saka da alkhairi, sai kun zo🥰🥰🥰*
*Page 0️⃣4️⃣*
Da mamaki a saman fuskarta ta ce" Aa ba namu bane wannan fa"
Mutumen nan dai ne rike da hannun Husaini dan nesa da su kadan yana fuskantar Aban saudat aa tunaninsa ko mai gidanta ne ya ce" Asalamu alaikum, dan Allah na biyo bayansu dan na karra bada hakuri, sannan ku yi hakuri ku amshi kayan nan, an samu matsala ne na rashin fahimta in sha Allah hakan ba zata kuma faruwa ba"
Tsayen da take kallon bayaninsu take yi da mamakin ko menene abinda ya sa wannan mutumen biyosu mai daraja ne, shi din da kansa mai tausayi ne mutumen, a sanyaye ta girgiza kanta ta ce" Aban saudat ba zan amshi kayan nan ba, ga dai kudin a irga abinda suka kama sai a cire harda na biscuit din da ya ci"
A nutse ya ce" Ama ai Aban aboki yace ki amsa ki yi hakuri ki amsa "
Husain da sauri ya kalleshi yana fadin" Aa fa, ba abanmu bane wannan, akace abanmu ya rasu ko Mama?"
Shiru ta yi tana kallon bakin Husaini, yaron ba dai surutu ba , kuma ba rashin kwaba bace haka Allah ya halice shi da saurin sabo da shegen surutu Masha Allah
"Ay sorry ai na zata abanku ne , ama ki menene a dai yi hakuri, ni na kasa hakura ne dan na ga dan uwan aboki sai huci yake yi, "
Gannin baban mutun ba wani karamin saurayi ba yana ta masu magiya a kan abinda ba shi ya bata ba ya sakata dan rage tsayinta kadan ta yi masa godiya sannan ta shige adaidaitar ta jinginar da kanta a jikin abin adaidaitar ta yi ta lumshe idannuwanta, a haka take jin magangannunsu har ta ji ya tada babur din sun dauki hanya
Ana fitowa daga masalaci sunna karasowa kofar gidansu
A daidai lokacin ne matarsa watau innar saudat ta fito zubar da ruwan wankin da ta yi, kasancewr anguwar ba wai mai duhu ce cen ba ya sa idannuwanta duka sauka a kan mijinta dake sauko da ledojin nan yana ajiyewa a kofar gidan Amina
Baban abinda ya sakata sake zuba masu ido gannin Aminar na binsa da kudi tana magiya ama mijinta wanda ko tau naira dari da ashirin ce ya bara mata na cefanen safe da yama nata da ƴaƴansu yana nuna ba zai amshi kudin nan ba? Lalle yau abinfa take zargi ne zai tabata kennan?
Juyawa ta yi wuuuuu ta shige ciki zuciyarta cike da sake saken irin yadda zata bullowa al'amarin
Sunna shiga cikin gidan ta rufe ruf sannan ta bude baban dakin tana saka kayansu hadi da kunna wutar nepa da fatan samun wuta dan zafi take ji sosai
Du da alwallah suka shigo suka shinfida abin sallah, itama ta fice dan dauro tata alwallar
Tana zuwa ta shiga gabatar da sallarta a nutse, sai da ta gama sannan ta wuce ta bude kayan
Macaronin da ta siyo masu ta dauko ta shige kicin dinta ta kunna fitilar kwai domin kicin din bata da fitila ta shiga dahuwar gagawa ta hade komai ta tsayar da ruwan miya ta koma dakin tana idasa fitar da abubuwan dake ciki
Ido kawai ta zubawa garin kayan kwalam da makulashen da aka zuba a wata ledar shake, sai makaroni da shinkafa irin na leda masu tsadar nan kala daban daban a wasu ledojin shake summa wa'inda a sanninta dai ba ita ta saka a cikin kayansu ba
Ajiyar zuciya ta sauke ta mayar gefe tana sake duban Husaini gannin sai kallon ledar kwalam da makulashen yake
Bata bashi ba ta daure sosai ta ajiye gefe
Da wuri wuri ta gama girkin lokaci daya tana gyaran kayan miyar da danyen naman da kifin da zata yi anfani da su , so take ta gyara su tun yau kar su kai gobe su cenza warinsu domin bata da freeza bale ta saka
Juyewa ta yi a baban faranti ta ajiye masu karkashin karamar fankarsu da abin firfitu ta kama ruwan wanke hannu da na sha da yaren suka dibo ta ajiye
Hannayensu suka wanke suka shiga cin abincin bayan sun yi adu'a
Basu jima a kan cin abincin ba suka tatare ta kwashe komai da kanta ta darwaye abubuwan da suka yi amfani da shi da ruwan rijiyarsu mai kyan gaske sannan ta dawo ta zauna ta kirayi yaren
Gabanta suka zauna su biyun, ta tsura masu ido irin yadda suke kama ita da kanta ta yannayin girman jikinsu da kuma kamanin idannuwansu kawai take bambance su
A hankali ta ce" Waye ya baku izinin fita daga bayana bayan tafe muke tare da ku?"
A tare suka kwashi magana wannan na cewa dan uwansa ne wannan na nuna dan uwansa
Kausasa muryarta ta yi sosai ta ce" Ba zaku fadi gaskiya ba kennan?"
Jiki a sanyaye Hasan ya ce shine, sai kuma Husainin shima ya ce shine, lokaci daya kuma sai Husainin ya dora kansa a gefen kafadar dan uwansa ya fashe da kukan da ya kusan sakata karaya harma ta rarasheshi bayan ta dauri aniyar yi masu fada da nasiha ne, koda zata yi rarashin ba yanzu ba, dan haka ta jure sosai tana kallonsa ta ce" Kai mike daga jikinsa kuma ka kama min bakinka ka yi min shiru! Yaya nace maku a kan abinda aka bakuma bale wanda kuka gani kuka dauka? Yaya na ce maku a kan haka?"
Da sauri Husain ke rufe bakinsa dan kar ya kuma fashewa da kukan stlll yana son bada amsa ga kuka na hanna shi, dole Hassan ne ya ce" Kin ce ko bamu abu aka yi kar mu ci sai mun nuna maki, kin ce mu daina amsa bale idaan muka ga abu ko na waye kin ce kar mu yarda mu taba ko mu dandana , ba kyau, daukan abinda ba naka ba babu kyai, sata ne, sata kuwa kin ce haramun ne"
A sanyaye Amina ta ce" Ba nice nace haramun bane Fadeel, Allah ne ya haramta sata, du wanda ya yi sata a hukuncin adinin musulunci ance a datse gundugwuilar hannunsa, "
" Wayo Allahna hannuna, Mama walahi ni ba sata na yi ba, dauka na yi nace zaki biya shine na ji ina kwadayin abin na bude na diba kadan" Husain ya fada a raunane yana shirin kuma barke mata da kuka , abinka da wanda ya aikata laifin
Ajiyar zuciya ta dauke tana fuskantarsa ta ce" Farid babu kyau, haramun ne, Allah ya haramta, ko me kake so a duniya ka fada min, in dai bai fi karfina ba in sha Allah zan yi maka shi, ka ji?"
Kai yake gyadawa da sauri, hakama dan uwansa,
Sai da ta tabatar sun gane fushinta a kan wannan lamari, sannan ta dawo nasiha a tausashe sai kuma ta saka suka yi salar isha'i suka kwonta
Kamar yadda ta saba tunda ta salaci sallar asuba ta dora kaskon tuyarta a tsakar gidan ta shiga aikinta da murhu biyu da itace ba da gaz ba
Safiya na yi aka ringa buga mata gidan daidai ta taso biyu ta sakasu yin wanka d shiryawa
Zuwa ta yi ta tambayo waye, kafin ta bude
Da fara'a suka gaisa ta yi baya ta bata hanya ta shigo hannunta rike da Saudat da ko ido bata wanke mata ba
Juyowa ta yi sai ta ga daya daga cikin ma'aikacin wajen rike da ledoji jigi jigi kusa da likitan
A tausashe sosai ya furta" ki yi hakuri na san ke matar aure ce, ba wani abu bane dama dan na tambaya ne Ina fata ya saurareki?"
Amina ta juyar da kanta tana shaƙar iskar magariba dake hurowa a sanyaye ta ce" Ban samu ganninsa ba, sia dansa, na fadawa ɗan nasa sakon na san zai sanar masa"
Dan jim ya yi , sai kuma ya ce" Dansa kuma?"
Amina ta gyada masa kai tana dubansa
A hankali ya ce" Ai shine mai wajen fa, shi daya muka baro a ciki"
Sai da ta saki baki da mamaki, ta waiga ta sake waigawa ta kuma kallonsa, ama sai ta barawa kanta abinda ya bata mamakin a zuciyarta , karshema sai zuba ido tana kallon yadda yake ta kokarin sai Hasan ya bashi hannu ama ina, a murtuke fuskar nan du inda rigima take ta tatare a saman fuskarsa, Husaini ne ya sake sosai da shi yana amsa tambayarsa, sai kuma ta juya ta fice gannin Aban saudat ashe dai bai tafin ba ta karasa tana kawar da fuskarta gannin ya fito a adaidaitar yana tambayar lafiya kamar wace ta yi kuka?
Gannin ana miko masa ledojin ta juyo da mamaki tana fadin"
Yaya kuke gannin salon zai je? Yaya kuke hangen cakwakiyar lamarin? Ku zo mu je sisters🥰🥰🥰🥰😍😍😍😍
🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️
_*NI ZAN LADABI*_
🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️🙇♀️
*NA*
*SAJIDA NIGER*
Asalamu alaikum wa rahamatullah, makaranta novel dina gani na dawo da sabon takarda, sabuwar tafia, sabon salo mai dauke da darusan rayuwa, da karfin ikon sunnah, da gwagwarmaya da kula kula, rayuwa ce irin ta talaka bawan Allah dake gannin hawa da sauka dan ya rayu da mutuncinsa, rayuwa ce ta Mace mai dauke da hatsari, sadaukarwa, Biyaya da karfi.......zai zo maku da shafuka na gyara tun daga kan fatar jiki, ppart, sirika irin na cikin kurya a gangaro kan sabulai na sana'a da kuma turaran HUMURA wace kowace mace zata iya yiwa kanta tsumamen hadin tada hankalin mai gida
Wannan Novel na kudi ne ba free bane
Yan Nigeria jama'ata ga naku : 500 Naira
account number: 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi GT Bank sai ka turo shedar biyanka ta numberta kamar haka +227 93811618 SAJIDA NIGER
Wa'inda suke da matsala da harkar banki zasu iya turo kati ta numberna, ko su yi pos in sha Allah, kuma a kan number nawa kamar haka 93811618..... Sai kun zo
Jama'ata yan NIGER ga naku : Dala dari , 500 francs cefa ta katin AIRTEL ko SAHELCOM ka turo ta numberna kamar haka 93811618 sai na saka ka
*NA gode sosai, Allah ya saka da alkhairi, sai kun zo🥰🥰🥰*
*Page 0️⃣4️⃣*
Da mamaki a saman fuskarta ta ce" Aa ba namu bane wannan fa"
Mutumen nan dai ne rike da hannun Husaini dan nesa da su kadan yana fuskantar Aban saudat aa tunaninsa ko mai gidanta ne ya ce" Asalamu alaikum, dan Allah na biyo bayansu dan na karra bada hakuri, sannan ku yi hakuri ku amshi kayan nan, an samu matsala ne na rashin fahimta in sha Allah hakan ba zata kuma faruwa ba"
Tsayen da take kallon bayaninsu take yi da mamakin ko menene abinda ya sa wannan mutumen biyosu mai daraja ne, shi din da kansa mai tausayi ne mutumen, a sanyaye ta girgiza kanta ta ce" Aban saudat ba zan amshi kayan nan ba, ga dai kudin a irga abinda suka kama sai a cire harda na biscuit din da ya ci"
A nutse ya ce" Ama ai Aban aboki yace ki amsa ki yi hakuri ki amsa "
Husain da sauri ya kalleshi yana fadin" Aa fa, ba abanmu bane wannan, akace abanmu ya rasu ko Mama?"
Shiru ta yi tana kallon bakin Husaini, yaron ba dai surutu ba , kuma ba rashin kwaba bace haka Allah ya halice shi da saurin sabo da shegen surutu Masha Allah
"Ay sorry ai na zata abanku ne , ama ki menene a dai yi hakuri, ni na kasa hakura ne dan na ga dan uwan aboki sai huci yake yi, "
Gannin baban mutun ba wani karamin saurayi ba yana ta masu magiya a kan abinda ba shi ya bata ba ya sakata dan rage tsayinta kadan ta yi masa godiya sannan ta shige adaidaitar ta jinginar da kanta a jikin abin adaidaitar ta yi ta lumshe idannuwanta, a haka take jin magangannunsu har ta ji ya tada babur din sun dauki hanya
Ana fitowa daga masalaci sunna karasowa kofar gidansu
A daidai lokacin ne matarsa watau innar saudat ta fito zubar da ruwan wankin da ta yi, kasancewr anguwar ba wai mai duhu ce cen ba ya sa idannuwanta duka sauka a kan mijinta dake sauko da ledojin nan yana ajiyewa a kofar gidan Amina
Baban abinda ya sakata sake zuba masu ido gannin Aminar na binsa da kudi tana magiya ama mijinta wanda ko tau naira dari da ashirin ce ya bara mata na cefanen safe da yama nata da ƴaƴansu yana nuna ba zai amshi kudin nan ba? Lalle yau abinfa take zargi ne zai tabata kennan?
Juyawa ta yi wuuuuu ta shige ciki zuciyarta cike da sake saken irin yadda zata bullowa al'amarin
Sunna shiga cikin gidan ta rufe ruf sannan ta bude baban dakin tana saka kayansu hadi da kunna wutar nepa da fatan samun wuta dan zafi take ji sosai
Du da alwallah suka shigo suka shinfida abin sallah, itama ta fice dan dauro tata alwallar
Tana zuwa ta shiga gabatar da sallarta a nutse, sai da ta gama sannan ta wuce ta bude kayan
Macaronin da ta siyo masu ta dauko ta shige kicin dinta ta kunna fitilar kwai domin kicin din bata da fitila ta shiga dahuwar gagawa ta hade komai ta tsayar da ruwan miya ta koma dakin tana idasa fitar da abubuwan dake ciki
Ido kawai ta zubawa garin kayan kwalam da makulashen da aka zuba a wata ledar shake, sai makaroni da shinkafa irin na leda masu tsadar nan kala daban daban a wasu ledojin shake summa wa'inda a sanninta dai ba ita ta saka a cikin kayansu ba
Ajiyar zuciya ta sauke ta mayar gefe tana sake duban Husaini gannin sai kallon ledar kwalam da makulashen yake
Bata bashi ba ta daure sosai ta ajiye gefe
Da wuri wuri ta gama girkin lokaci daya tana gyaran kayan miyar da danyen naman da kifin da zata yi anfani da su , so take ta gyara su tun yau kar su kai gobe su cenza warinsu domin bata da freeza bale ta saka
Juyewa ta yi a baban faranti ta ajiye masu karkashin karamar fankarsu da abin firfitu ta kama ruwan wanke hannu da na sha da yaren suka dibo ta ajiye
Hannayensu suka wanke suka shiga cin abincin bayan sun yi adu'a
Basu jima a kan cin abincin ba suka tatare ta kwashe komai da kanta ta darwaye abubuwan da suka yi amfani da shi da ruwan rijiyarsu mai kyan gaske sannan ta dawo ta zauna ta kirayi yaren
Gabanta suka zauna su biyun, ta tsura masu ido irin yadda suke kama ita da kanta ta yannayin girman jikinsu da kuma kamanin idannuwansu kawai take bambance su
A hankali ta ce" Waye ya baku izinin fita daga bayana bayan tafe muke tare da ku?"
A tare suka kwashi magana wannan na cewa dan uwansa ne wannan na nuna dan uwansa
Kausasa muryarta ta yi sosai ta ce" Ba zaku fadi gaskiya ba kennan?"
Jiki a sanyaye Hasan ya ce shine, sai kuma Husainin shima ya ce shine, lokaci daya kuma sai Husainin ya dora kansa a gefen kafadar dan uwansa ya fashe da kukan da ya kusan sakata karaya harma ta rarasheshi bayan ta dauri aniyar yi masu fada da nasiha ne, koda zata yi rarashin ba yanzu ba, dan haka ta jure sosai tana kallonsa ta ce" Kai mike daga jikinsa kuma ka kama min bakinka ka yi min shiru! Yaya nace maku a kan abinda aka bakuma bale wanda kuka gani kuka dauka? Yaya na ce maku a kan haka?"
Da sauri Husain ke rufe bakinsa dan kar ya kuma fashewa da kukan stlll yana son bada amsa ga kuka na hanna shi, dole Hassan ne ya ce" Kin ce ko bamu abu aka yi kar mu ci sai mun nuna maki, kin ce mu daina amsa bale idaan muka ga abu ko na waye kin ce kar mu yarda mu taba ko mu dandana , ba kyau, daukan abinda ba naka ba babu kyai, sata ne, sata kuwa kin ce haramun ne"
A sanyaye Amina ta ce" Ba nice nace haramun bane Fadeel, Allah ne ya haramta sata, du wanda ya yi sata a hukuncin adinin musulunci ance a datse gundugwuilar hannunsa, "
" Wayo Allahna hannuna, Mama walahi ni ba sata na yi ba, dauka na yi nace zaki biya shine na ji ina kwadayin abin na bude na diba kadan" Husain ya fada a raunane yana shirin kuma barke mata da kuka , abinka da wanda ya aikata laifin
Ajiyar zuciya ta dauke tana fuskantarsa ta ce" Farid babu kyau, haramun ne, Allah ya haramta, ko me kake so a duniya ka fada min, in dai bai fi karfina ba in sha Allah zan yi maka shi, ka ji?"
Kai yake gyadawa da sauri, hakama dan uwansa,
Sai da ta tabatar sun gane fushinta a kan wannan lamari, sannan ta dawo nasiha a tausashe sai kuma ta saka suka yi salar isha'i suka kwonta
Kamar yadda ta saba tunda ta salaci sallar asuba ta dora kaskon tuyarta a tsakar gidan ta shiga aikinta da murhu biyu da itace ba da gaz ba
Safiya na yi aka ringa buga mata gidan daidai ta taso biyu ta sakasu yin wanka d shiryawa
Zuwa ta yi ta tambayo waye, kafin ta bude
Da fara'a suka gaisa ta yi baya ta bata hanya ta shigo hannunta rike da Saudat da ko ido bata wanke mata ba