← Book details Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 89 OF 105

Sashe 89

Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

kanki da kuma mutuncina wani sabon kuka ta fashe dashi "ummah ta riko hannunta gam cikin nata itama kuka ta fashe mata dashi sosai cikin tsananin tashin hankali tana kiran sunan allah tana cewa "laifin me d'ana yayi masu wannan hukuncin yayi tsauri ga rayuwar sadam babu wanda zuciyarsa batai rauni ba aunty da wasu daga cikin yanuwa hawaye suke dan tausayawa ga umma d'aya bayan suka dinga barin dakin inda dakin ya saura daga aunty sai ummah da maryama "umma muje inda aka binne yaya sadam a fito dashi jikina na bani yana nan a raye ummah ki tausaya min wallahi bazan iya rayuwa babu shi ba "ki samu natsuwa maryama in sha allahu zamu je gobe"iya abinda ummah ta iya fad'a kenan bata sake cewa komai ba dan bazata iya magana mai tsawo ba ." washegari aka kai maganar gurin hukuma aka shigar da qara tare da nuna hoton yaya sadam daga nan aka yiwa maryama tambayoyin daya dace sannan aka saka maryama gaba sai hanyar ogun state tafiya suke tana share hawaye tana addua duk kwanar data gani sai ta rikice tace nan ne . sai an tsaya tace a a ba nan bane ahaka suka kusan kaiwa cikin ogun state dan daga inda suke suna iya hango sambaod din wel come to ogun state tayi sauri tace kamar kafin mu kawo wannna sambaod din ne . cak direba dake tukasu ya tsaya tare da juya Kan motar suka koma dayan hannun sun sha wahala sosai a qarshe dai ta gane daidai inda sojojin suka sha gabansu saka makon warin takalminta data gani yashe a gefen titi . jikinta na rawa ta soma kuka tana cewa "ku tsaya nan ne !"batare da bata lokaci ba suka firfito tabbas anan ne suka sha gabanku ta fad a tana kuka .daya daga cikin jami in tsoro yace a ina aka binnesa nan maryama ta hau zazzare ido tabbas daga nan suka rufe mana ido amman duk da haka jikina na bani wannan kwayar suka shiga damu basu mutsa mata ba suka shiga mota suka bi hanyar tafiya suke amman jikin maryama rawa yake dan bata son tayi kuskure wajen gano wajen . gabad aya babu inda baa duba ba ko zaa ga alamar tudun kasa amman babu ,jami'an tsoro suka tsaya suna kallonta "kin tabbatar nan ne?tayi shiru tana share hawaye dan gbdy ta rikice ummah Ummah duk ta rude sai zufa take fitarwa ta matso kusa daita tace maryama ki natsu da kyau a samu a gano inda suka binnesa tayi mgnr cikin rawar murya maryama ta fashe da kuka tare da zubewa kasa sakamakon ta rasa mafuta. dan kwakwaluwarta ta cunkushe waje d aya yadda maryama take kuka haka umma take kuka tana janyota jikinta gabdaya jikknta ya d auki zafi kamar garwashin wuta yayind jami an tsaro suka cigaba da dudduba wajen ko zasu ci karo da tudun kasa amman still dai babu wata alama inda aka binnesa ganin suna bata alokacin su ne yasa suka ce su wuce zaa zaa sanar a gidan radio da tv maryama kam duk ta gama rikice masu sai sunan yaya sadam dina kawai take kira ku nemo min shi dan Allah karku barni haka da kyar aka samu aka saka acikin mota suka kama hanyar gida . ****** Shabiyu ne na rana yana tsaye acikin office dinsa sanye da t shirt long sleeve light puppy da wondo baki sai tie baki zagaye da wuyansa ya tura hannuwansa duka cikin aljihun wondonsa wani irin kamshi jikinsa ke fitarwa mai sanya natsuwa da kwantar da hankali fuskar nan tashi a murtuke zariya ya soma yi acikin office din yana tunanin maryama wanda bai san dalili ba tunaninta yaki barinsa babu abinda zuciyarsa yake kwadayin sake gani kamarta kafin ahankali yayi burki a daidai mazauninsa turo kofar office din akayi batare da an nemi izinin shigowa ba ya kalli kofar ammar ya gani yanayin yadda yaga fuskarsa ya dan fahimci akwai wani abu yana gama shigowa ya soma magana cikin tsananin fushi "burinka ya cika maryama tayi aure so what idan tayi aure what s my business with her ?wai menene matsalarka adam ?"da nayi me kenan ?wallahi ban san baka da sa'a arayuwarka ba sai da maryama tayi aure "t ni menene damuwa ta da aurenta ?kaga dan Allah karka sake min maganar ta karka qara min damuwa akan wanda nake ciki "kai ne kuwa kake da damuwa daita ."hade rai ata yayi sosai yana yiwa amar wani irin mugun kallo mai bugar da zuciya "kasani inada dalilina na son ku hadu daita tun kafin tayi aure.ata yayi taku daya biyu yana mai juya masa baya wallahi da ka daure kaga maryama da zaka fahimci abinda na gani har yasa nake son ku hadu daita." juyowa ata yayi ya fuskancesa yana hura masa hanci tare da kai hannu yana sunce tie din wuyansa "kai ma tunda kaga na na nace ai ya kamata kayi amfani da sense dinka ,bazaka ta'ba jin dadin wata mace a duniya ba sama daita" look ammar bana son damuwa ,"my friend you have to use your common sense and think akwai dalili mai karfi dayasa naso ku hadu "ata ya sauke hanunsa daga wuyansa ya maida cikin ajihunsa yana nazarin maganar ammar "ba dai ka rasa maryama ba kasani zuciyarka zatayi nadama fiyye da kowani nadama da d'an adam keyi a rayuwarsa "ya d'ago ya tsurawa ammar idanunshi tare da cire hannunsa d'aya cikin aljihunsa ya rike kugunsa," wasu ma suna janyota jikinsu domin su amfana daita bare kai da ..."wai meye haka ammar ?ka dameni ka cika min kunne da surutun banza da wofi dole ne sai na aureta ko dole sai na janyota jikinta ?"kaga enough please ka rabani da maganar wata maryama din banza bana son jin ko sunanta bare na aureta "yayi maganar a tsawace yana furzar da iska mai zafi "ai kuwa ka shiryawa shiga tashin hankali da damuwa domin duk ranar da zaka ganta kuma amatsayin matar aure sai kayi nadamar rashin haduwarku akan lokaci ,kuma lallai bazan daina fad'a maka rashin haduwa daita damuwa ne akan damuwa kuma har qarshen rayuwarka bazaka daina da kasani ba kai in takaice maka zaka iya rasa ranka ". ata ya dafe goshinsa da hannunsa daya "ammar kana rikita min kwakwaluwa zuciyata tana tsinkewa magangunka gabad'aya suna nema tarwatsa min zuciya gabad'aya na kasa fahimtar abinda kake nufi yayi maganar kamar zai yi kuka tare da zama akan kujera yana kallonsu "you are mad adam yanzu abinda ya rage maka ka zauna kayi tunani akan maganganuna " yana gama fad'ar haka ya buga masa table din gabansa ya juya ya fita a fusace ." ata ya kai hannu goshinsa kafin daga baya ya soma jujjuya jikinsa akan kujera wani irin ihu yayi yana kai hannusa ya ture tarin file din dake Kan table sannan ya mike tsaye zambur Kmr zaki ya dafe kanshi gabad'aya ya rasa meke masa dadi dan wani irin abu yaji yana yawo acikin ilahirin jikinsa mai kama da abinda yake ji akan mafarkinsa yau shine karo na biyu da yaji wani abu wanda ya shafi mafarkinsa akan wata mace "wacece mai zanen creation wacece maryama datai aure coz the same abu yake ji akansu wanda yake da kusanci da abinda yake ji akan mafarkinsa karka matso kusa dani domin bazan ta'ba kasancewa cikin wawayen mata masu cin amanar mazajensu ba itama matar aure ce ya rabbi what s wrong with me ?yana cikin wannan halin james yayi knocking yana neman izinin shiga sai da ata ya dauki lokaci sannan yace "coming !" ya shiga cikin taka tsantsa "mai gida ina son nayi magana da kai ko zan iya magana ?" leave!" mai gida magana ce mai mahimanci "I said leave bana bukatar jin komai yanzu."da sauri ya juya ya fice .cikin company ranar kam kowa ya kama kanshi dan dukkanin alamun sun nuna an tabosa, duk kuma wanda yayi kuskuren shiga track dinsa zai sha bala'i idan ma bai ce ya kori mutun ba har ya dawo gida maganar ammar na damunsa cikin rai sai yayi kamar ya kirasa ya sake masa karin bayani sai muguwar zuciyarsa ta gargadesa " Bayan sati d aya wanda yayi daidai da kwanaki shabiyu da daura auren maryama da yaya sadam sultana ta dir a kasar kuma kai tsaye abdullahi estate aka nufo daita murna wajen aunty abida abun baa magana ,tun daga lokacin da sultana ta shigo estate din aunty abida ta fara aiwatar da shirinta kullum suna bangaren mami sai dai basa samun ganin ata suna samun sa banin shiyasa yau sukai sakamakon yau .ahankali yake ssukowa daga Kan step cikin shigarsa na kullum sai kamshi yake idanunsa bai sauka akan kowa ba sai akan aunty abida da sultana kallo daya yayi masu ya dauke idanunshi ya cigaba da taku har ya wucesu ta mike ta sha gabansa tana kiran sunansa adamcy barka da saukowa. ya tsaya kawai yana kallonta batare da yace mata komai ba ga sister ta kawo mana ziyara Ya ganta ta hadu ko ?still dai bai tanka mata ba tayi murmushin yake tana cewa daman nace bari na kawota ku gaisa sultana ga cup din tea dinsa can dauko ki bashi . jikinta na rawa ta juya ta dauko Orenge cup din dake ajiye wanda daman dan shi aka tanada ta mika masa ,sai dai bai kar ba ba yace "am okay coz am oready late zai wuce ta sake tsaidashi Ya tsaya cak yana duba agogon dake daure da tsintsi yar hannunsa kamr yadda kasani sultana kanwarmu ce kuma ta kware a harkar zane dan naji ance kana bukatar kwararun masu zane shiyasa nace tazo dan tasan Kan aikinta sosai idan bazaka damu ba ko zaka bata dama kaga irin nata kwarewar ?shiru yayi bai ce uffan ba nasan bazaka ta'ba zuba ma yaruwarka kasa a ido ba zaka gwada yaruwarka kaga irin nata baiwar bayan shi ma ina son ka taimaka ka bata aiki a maakatarku Z&A idan ma da hali ka barta a kusa kusa da kai wato P.A dinka dan na yi imani zaka ji dadin aiki daita dan .... duk naji bayaninki. ya katseta ta hanyar fad ar haka kafin ya cigaba
Chapter 89 · 0% Book details