Sashe 105
Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel · about 2 min read
hannunsa yana kurban coffe a hankali bai juyowa ba har sai da yaji salim ya soma mgn ya kira sunansa cikin wata irin muryar mai cike da tashin hankali ATA ya juyo a natse yana fuskatarshi alokacin da salim ya cire nikaf din fuskarta maryama yana rike a hannunsa wani irin bugu qirjinsa da zuciyarsa yayi alokaci daya bai san sanda cup din hannunsa ya subuce kasa ba. take ya tarwatse zuciyarsa ta tsaya cak ta daina aiki na wuncin gadi ,duk yadda ATA ya kai ga son motsa sassan jikinsa bun ya faskara,tamkar wanda bai da numfashi a ganganr jikinsa haka ya dawo saka makon wani yanayi mai sarkakiya da wuyar faasarawa ya ziyarci zuciya dama gangar jikin ATA abangaren maryama ma wani irin mummunar bugu zuciyarta keyi da mugu mugu sauri la haula wala kuwata illa billa babu tsumi babu dabara sai na Allah haka ATA yake ta faman ambata acikin zuciyarsa dake karkarwa yayinda maryama wacce bata san dalilin dayasa mutumin dake tsaye a gefenta ya shigo daita ba sai dai ganin fuskar mutumin dake tsaye a gabanta yasa ta nemi natsuwarta ta rasa . hakan nan damuwar dake cunkushe cikin ranta ta ninku yayinda soyayya da kaunarta ya dinga bin dukkan sassa na jikinshi ji yake kamar acikin mafarikinsa ya Allah kasa a zahiri nake ganin komai ba mafarkin dana sabayi daita bane ,wani irin so mai zafi ya dinga huda zuciyarsa yana bin jinin jikinsa wanda ma'abota so da shauki kadai ne suka san zakinta,yana son yarinyar kamar ranshi shikanshi yana mamakin zazzafar soyayyr da yake mata mai tafiya da dukkan wani motsi na bugun numfashinsa adam kayi maza ka dawo haiyacinka karka biyewa soyayya dake kutimemeniya da rayuwarka gizo ce ba zahiri ba to Salim dake tare daita fa ?shima gizo ne ko me ? tsaki taja tana duban fuskar salim a wulakance cike da tarin bakinciki mara misaltuwa muryarta cike da sheshekar kuka tace Allah ya isa tsakanina da kai bazan ta ba yafe maka ba .sautin muryarta ce ta dawo da mr ATA cikin haiyacinsa tun bai kai ga bawa kanshi amsa ba ya ware idanusnhi sosai ya zuba mata kwayar idanunshi yana kallonta tamkar zai cinyeta Alhamdulillah Anan zan dakata sai mun had u a littafi na uku wanda zai zama na qarshe ina maku fatan alkhairi Mmn suka SummaryInformation DocumentSummaryInformation WpsCustomData TECNO LD7 WPS Office Normal Times New Roman Times New Roman Calibri Calibri !%),.:;>?]} $([{ 447c6e3a5bf341fc9e77549cc1cd2797