← Book details Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 104 OF 105

Sashe 104

Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

exactly laifin me kika min da kike bani hakuri ?ai nice yafi dacewa na baku hakuri ku da ake nema a wurinku ,amman ku kuwa wani irin tsarin ne da maakatarku hk ?a dauki mutun aiki rana daya da fara aikinsa a koresa ?kiyi hakuri maryam ki wuce kawai karma kisa rai ko a wani guri ma zaki samu aiki domin sir nada karfin iko a koina to ni laifin me nayi masa haka ?ki tmbyr min shi laifi me nayi masa haka ?tai mgnr tana kuka ai ban isa najewa sir da wad an nan tamvayoyin naki ba to shikenan amman wallahi kisani bazanje koina ba har sai naji dalilin dayasa ya koreni muddin bai fad a min laifin da nayi masa ba anan zan qarar da rayuwata .. ta samu guri ta zauna tana kuka mai matukar cin rai okay maryam bari na gwada saata ko allah zai sa ya saurareni ta juya da sauri ta fice yayinda maryama take zubar da hawaye masu zafi bata san sanda ta zamo kasa bisa gwiwowinta ba ta hade tafukan hannunta guri daya ya allah meke shirin faruwa dani kuma ?wani irin tashin hankali ne wannan ?daga zarar na fita cikin wata maseefar sai wata ta bullo ya allah ka taimakeni . a can gida ma hankalin aunty da umma har da granny duk a tashe yake umma ta qaraso da magani da ruwa a hannunta hajiya yau baki sha maganinki ba ga lokaci na wucewa ni gbdy na ma manta da wani batun shan magani dan bana da natsuwa ban san halin da maryama take ciki ba wallahi hakan nan nake jin damuwa ya allah ka taimake yarinyar nan kasa karshen wahalarta ne yazo karki damu in sha allahu alkhairi ne zai biyo ba tunda an dauketa aiki ai sai fatan albashi su fara shigowa to allah yasa alkhairi ne zai biyo baya . ameen ta karbi magani ta kai bakinta . ATA na tsaye har lokacin ya kasa zama sectary dinsa ta shigo sir na fad a mata hukuncinka amman tace baza tafi koina ba har sai ta gana da kai no way ! ya fad a yana jin wani irin faduwar gaba mai tsanani I won t meet her ki koma ki fad a mata haka sir na fad a mata taki tafiya ne wai sai an fad a mata laifin da tayi daaka koreta aiki daga farawarta yau kije ki fad a mata ta bar kanfanin nan dan bazan ganta ba kema da kika dawo min da banzar maganarta idan kika sake zuwar min da mgnrta zaki samu matsala dan kinfi kowa sanin laifin datai ko ba da kanta taki amsar aikin da muka bata a tun farko ba ? sannan na bukaci zanenta shima taki yarda ta ganni sau nawa ina kiran wayarta taki daga wa ta saurareni sannan nayi qoqarin tayi min aiki a ogun shima babu wani biyan bukata,yanzu kuma ta kwaso jiki tazo neman aiki kamfanina ?kema kinsan bazai yuwu ba ya fad a a matukar a tsawace . Nan take sectary ta kame jikinta na rawa dan duk lokacin da yake mgn cikin fushi itama fita haiyacinta take ya sauke numfashi kana ya dunkule hannunsa ya naushi iska aikin har yana arha haka ka kisa alokacin da kaso sannan ka samu alokacin da kaso idan ma baki fad a mata laifinta ba ungo nan ya zaro wata farar takarda ya mika mata kije ki bata amman ganina ko magana dani abu ne da zai mata wahala acikin wannan kafanin ke qarshen rayuwarta bazata sake ganina ido da ido ba okay sir tasa hannu ta karba ta juya ta soma tafiya idan aka sake halittarta a duniya aka bata aiki bazata ki karba ba nonsense girl kawai ya fad a yana furzar da iska . Da sauri sectary ta shiga office din da maryama take tana mai kiran sunanta ta mike da sauri ta qaraso gareta tana cewa laifin me yace nayi masa. mika mata takarda tayi tana qara mata da bayani abinda tayi hawaye ne suka zubo mata wayyo allah wallahi bana ki amsar aikin bane a wancan ranar dan yin kaina wata kawata ce tafi ni bukatar aiki shine na bar mata amman badan banason aikin bane wanna shine dalilin da yasa mr ATA ya koreki kema abinda kikayi bai kamata ba bayan shi ma akan zane shima haka kika masa wulakanci bayan saboda abinda ya faru aranar da kikazo kawo zanensa yaji babu dadi aransa shine ma yasa James yayita kiranki akarshe shima ya kiraki baki dauka ba ,da kuma kika dauaka me kika ce ? maryama tayi shiru tana dubanta kikace bazakiyi ba ! Muryarta a sanyaye tace am sorry ! Babu wani maganar sorry zaki iya tafiya dan bazaki samu wata dama ba is okay na gode Kwarai da gaske tunda da farko nice naki amsar aiki sannan nakiyin aiki daku yanzu kuma na dawo kuka kini bani da yadda zanyi tunda ku kuke da kamfaninku tana gama magana ta juya da niyyar barin office din idanunta ya sauka akan kawarta subaia kin rasa aikinki akaro na biyu maryama akaina ? karki damu subai ba akanki bane haka allah ya qaddaromin Kiyi min fatan alkhairi. dan allah kiyi hakuri nasan duk laifina ne nace karki damu ko na karba da farko haka zasu min dan da gani mai kanfani har wadan da suke aiki karkashinsa duk mahaukata ne na ma gode da ban samu aiki akarkashinsa ba suna cikin wannan halin sai ga yusura ta fito daga office din daakaita ,kusa da maryama taje ta tsaya tana tmbyarta aikinta ta rasa adalilina aikinta da bar min wata uwar harara yusura ta maka mata ai gsky ne adalilinki ta rasa wancan aikin yanzu ma ta rasa wanna kenan ?subai a ta gyada mata kai a wani dalili ? Ke !me ma ya kawoki ma tunda ai baa nan kike aiki ba ?karki manta da mai wannan kamfanin da A&Z duk mutun daya ne wani mahiman aiki ne ya kawoni karku tsya bata lokaci please zaku iya wucewa kuje kasa ku cigaba da magana inji cewar some maryama bari na dauko jakata mu tafi tare kawai zaman me zanyi ?no yusura karki damu kiyi zamanki bazan zama sanadin rugujewa farincikinki ba ,ina miki fatan alkhairi all the best to both of you tana gama fadar haka ta juya ta soma taku ,da kyar take iya d aga wafafuwanta saboda nauyin da suka mata ,wani matashin mutun ta gani tsaye bata bi ta kansa ba ta raba ta gefensa ta wuce shi tana sauke nikaf din fuskarta shi kam kamewa yayi ya kasa kwakkwaran motsi shin mafarki yake ko kuwa zahiri yake gani ?. ya kai second goma yana kallon bayanta har ta kusan bacewa ganinsa sannan ya juyo ya dubi some kinga wata doguwar yarinyar ta wuce yanzu ? yes sir ! da sauri yace mutun ce ko fataluwa ce ?mutunce sir sunanta maryam hussein .maryam hussein !? ya furta a dan razane adaidai lokacin da yusura ta fito ta tabi bayan maryama da sauri tana kiran sunanta hankalin salim a matukar tashe yace Adam ya ganta kuwa ?No sir aiki tazo nema har an dauketa yace akoreta da sauri yace kai bari naje na sake tabbatarwa itace ko kuwa dai kama ce ya bi bayanta da sauri ya sauka har kasan kamfanin yana nemanta bai ganta ba tsaki yaja yana cewa amman Adam ya cika hauka me yasa bai tsaya yaga yarinyar nan ba yana tsaye sai gasu ita da yusura maryama tana magana muryata da alamun tayi kuka sosai karki damu yusura ki tsaya Kiyi aikinki karki yi Kuskure irin wanda nayi ,kin dai ga yadda abun alkhairi ya zame min ko? to ki tsaya kiyi aikinki ina miki fatan alkhairi ta fad a tana tsaida yusura tare da rike hannunta cikin nata . Ahankali salim ya kara taku ya matso kusa dasu shikenan maryama naji kuma na gode da shawarki allah yasa haka shine mafi alkhairi arayuwarki sai mun hadu a gida dan allah karki saka damuwa aranki komai yana da lokaci kuma in sha allahu zai zama alkhairi . numfashi ta sauke sannnan ta saki hannun yusura dake cikin nata ta juya itama ta juya ta soma tafiya da sauri kawai taga mutun agabanta yana sauke numfashi bai tsaya wata wata ba kawai ya daga nikaf din fuskata tare tsura mata ido byn Kmr second biyu ya saki wani irin murmushi wanda bashi da maraba dana farinciki muryarsa cike da in.. ina.. ya soma mgn itace wallahi tabbas itace wallahi itace wacce danuwana ya dade yana nema yayi maganar yana riko tsintsiyar hannunta dan Allah kiyi hakuri mu koma ciki akwai wanda zan nuna wa ke . bai gama rufe bakinsa ba ta fixge hannunta tare da daukeshi da wani gigitaccen mari tana cewa itace wa ? Akan wani dalili zaka kai hannunka jikina ? ammm but da kin .. kar kace min komai bana bukatar jin komai dan baka zo da siffar da zan saurareka ba daga ganin mutun sai ka wani kai hannunka jikinsa kasani koni matar aurece ta fad a a fusace tana sake juyawa ya sake shan gabanta wallahi babu inda zaki sai na kai ki gurin .. wallahi ka sake kuskure tabani sai na maka wulakanci da har ka matu bazaka manta dani ba ,matsa ka bani hanya na qara gaba da rayuwata to to ki bani numberki ko address dinki i cant! ta fad a tana bin gefensa zata wuce shi sam sam marin da tai masa bai damesa ba kamar tafiyar da zatai Adam bai ganta ba da sauri ya sake shan gabanta kinsan allah bazaki bar nan ba batare da danuwana ya ganki ba wuce mu koma sama maryama ta dafe goshinta cikin tsananin tashin hankali wannan shine karo na biyu da ta fuskanci irin wannan matsalar kafin ta ankare taji ya rike tsintsiyar hannunta ya soma tafiya daita cikin sauri sauri gudu gudu ya dinga tafiya, tana ya sakar mata hannu amman yaki da kyar da bala i ya shigar daita lifter ya fad a office din ATA daita a tsaye ya gansa rike da kugu ya juyawa kofa baya yayinda cup din coffee ke rike a
Chapter 104 · 0% Book details