← Book details Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 42 OF 105

Sashe 42

Mar’adam’s Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

idan tunaninta ya sakashi gaba jin zuciyarsa yake kamar zata buga hakan yasa yaki sauka parlour n gidan kamar yadda ya saba a duk sanda ya dawo . tsaki yaketa j yana qarawa domin tunaninta na damun kwakwaluwarsa,idan a son ranshi ne baya son yana damun zuciyarsa da kowa i irin tunani yana nan zaune a bakin gado yayinda kafarsa daya ke kasan tayis d ayan kuma ya tankwashe tare da dafe gaban goshinsa dake sara masa kad an kad an gefe guda kuma yana jin damuwar da ciwon abinda dakikiyar yarinyar nan tayi ,shi tunda yake babu wanda ya samu aiki da kamfaninsa yayi rejecting dinsa sai ita ,ai kuwa zata ga wahala ganin idanunta yana zaune maryam ta turo kofar d akin ahankali ta shigo bakinta d auke da sallama bai amsa mata ba haka zalika bai d ago ya kalli inda take ba . kusan minti biyar tana tsaye tana qare masa kallo sannan yaji sautin muryarta a sanyaye baby sannu da zuwa ! ta fad a ahankali tamkar wacce mako shinta Ke ciwo ya d ago a natse ya kalleta sanye take cikin kananan kaya wondo da riga maron colour mai ratsen fari ajiki yayinda jikinta ke fitar da kamshi hannunta rike da wani had den tray. bai amsa mata ba ,ya d auke kwayar idanunshi akanta zuwa wani bangaren yana jan tsaki dan ya tsani sunan baby din da take kiransa dashi ,bugu da qari bazai iya jurar cigaba da kallonta ba, dan babu macen data isa ya tsaya yana kallonta . banin ita daya rigada ya saba da kallo irin nata indai tana kusa dashi to fa dukkanin idanunta da natsuwarta suna kanshi ne bata damuwa da duk irin wulakancin da yake mata hassalima ya fahimci dadin kallonsa take ji dan ya santa farin sani babu yadda zaayi tana tsaye haka agabansa idanuwanta ba akanshi suke ba . daga sannu da zuwan da tai masa bata sake ce masa uffan ba ta ajiye tray hannunta ta soma hidimar zuba masa abinci bayan ta gama zuba masa ta sake motsa bakinta baby ga abinci !still bai ce mata komai ba sai ma haushi da ta sake bashi ta cigaba da kallonsa dan kallonsa ba qaramin jefata cikin nishadi yake ba ,kamar ta bud e baki ta tambayesa meke damunsa dan ta fahimci yanayinsa na yau ya canza fiyye da sauran lokutan daya saba kasancewa cikin miskilanci amman ta qasa tmbyrsa sbd gudun abinda zai je yazo .taga ya sake kallonta amman sai ta qasa d auke idanuwanta akanshi duk da ta fahimci shi hakan yake buqata daga gareta . madadin ta d auke kwayar idanunta kamar yadda yake buqata sai ta durkusa gabansa ta d auki glass cup ta had a masa coffe ta mika masa baby ga coffe ka sha nasan zaka fi buqatarsa a matukar zuciye ya kar bi cup din hannunta ya saita ta dashi zai kwata mata ruwan zafi tayi saurin zaro ido tare da yin gefe ,glass cup din ya samu bangon d akin, nan take ya tarwatse a qasa , ya mike a fusace sauran kad an ya taka wani bangaren na glass cup din dan har kafarsa ta sauka akan kwalba maryam ta saki qara mai sauti dole ya d aga kafarsa Ya koma ya zauna tana dafe goshinsa .ahankali ta juya ta fita da sauri bata jima ba ta dawo ta durkusa ta tattara dukkan wajen ta mike tana dubansa dan girman allah ka dinga bin komai ahankali kada kajiwa kanka ciwo ta furta cikin wata irin murya mai sanyi da tausasawa muga kafarka allah yasa bakaji ciwo ba yaji tana fad ya salam wannan wata irin mayya yarinya ce haka? ita sam bata damuwa da wulakancinsa ,har sai zuwa yaushe ne wuya zai sa ta gudu ta fita cikin rayuwarsa? yana son ta gaji dan kanta ,yana son hakurinta ya qare ta gudu da kafafunta ba sai ya sallameta ba amman da alamun shine zai gudu ya barta . bai ankara ba yaji ta kamo qafarsa data fi tunanin ita ce ta kusan taka kwalba ta sanya tafin hannunta karkashin tafin qafarsa ta soma murzawa ahankali Alhamdulillah babu abinda ya sameka kamar wanda ya farka daga wani mummunar mafarki ya fixge qafarsa da mugun sauri yana huci. numfashi ta sauke ta mike tsaye idanunta na kanshi miniti biyu tsakani ta juya adaidai lokacin da wayarsa ta soma ringing ta d an rage tafiyarta ya kai hannu ya d auka ya manna a kunnensa yaakayi ammar ?ya fad a yana furzar da numfashi ,dan girman allah bana ce ka rabani da maganar yarinyar nan ba? na rantse da girman allah zamu samu matsala da kai mutuqar baka rabu dani ba ,makaho ne ko me ?maryam ta kasa cigaba da tafiya ta tsaya cak zuciyarta na karkarwa eh haka n nasa a nemo min kwararun masu zane ban gane na fara ganinta kafin na anemo masu zane ba ? dan allah share yarinyar nan kwata kwata banason ganinta wace yarinya ce wannan da yaya ammar ya damesa daita ?tayiwa kanta tmbyr yanayinta na canzawa lallai akwai buqatar taga wannan yarinyar . ahankali suka cigaba da tautauna can yace dolen dolalo muna nan a yadda muke taki zuciya ta gudu ,wallahi ban soma jin komai akanta ba kuma bana fatan na so wannan yarinyar wannan magar da yayi ce tayi sauri dawo daita daga d an tunanin da kwakwaluwarta ta tafi na wuncin gadi .jiki a sanyaye ta cigaba da sauraronsa kai fa na fahimci baka son kaga ina cikin kwanciyar hankali ,wannan ba matsalata bace dan ni har yanzu ban maidaita matsayin mata ba ita .. tun kafin ya qarasa ta fice da sauri idanunta na kawo ruwan hawaye bata san me suka cigaba da tautauna ba amman kalma d aya zuwa biyu suka fi tsaya mata a kahon zuciya bai sonta da kuma tayin auren da yaya ammar yake masa anya kuwa bazata kai qarar yaya ammar wajen mami ba ta taka masa burki ?akan wani dalili zai dinga tursasa mata miji alhalin tana iyakar qoqarin taga ta shawo kansa sun zauna lfy?amman kuma da tayi tunanin hakan zai iya janyo mata gagarumin matsala da shi ta fasa gara ta nemi yaya ammar din tayi magana dashi . Bayan awa d aya da wasu mintuna ta sake dawo d akin ahankali ta qaraso ta tsaya nesa kad an dashi ta d auki kallonsa gabad aya yanayinsa ya koma na damuwa ,ta kalli abinci data kawo masa ga dukkanin alamun bai ci ba ,amman dai ta bud e taga bai ci din ba kamar yadda tayi zato har yayi sanyi me yasa bazaka barwa allah komai ba ?ka sani duk duniya nan idan suna son zamammu ma aurata ida allah bai hukunto hakan a tsakaninmu ba bazai kasance ba ,haka duk kinka da auren nan idan allah yaso mutuwa ce zata raba mu .idan kuma allah yayi iya rabon zama ne atsakaninmu dole za rabamu karka manta yadda baka son auren nan amman allah ya qaddara sai da akayi . Tai shiru tana dubansa sam bashi da alamun zai kalli inda take bare yace wani abu ,tunani rayuwarsa kawai yake ta ina zai cigaba da zama daita bai ta ba jin komai akanta ba ,shikenan mafarkinsa ya kasance karya ne kamar yadda aka sha fad a masa dan da gaskiya ne yadda yake qoqarin neman princess daya sameta nasan na dameka da magana kayi hakuri sannan dan allah kaci abinci . shiru ne stil ya biyo baya bata ji komai aranta ba dan wannan yana cikin halinsa rashin son magana ta numfasa tana cigaba da kallonsa idanunta cike da ruwan hawaye . dan allah kayi hakuri kaci wani abu ,rashin cin abincinka zai iya haifar maka da mummunar damuwa kuma bashi bane mafuta agaremu dan allah kaci wani abu tayi mgnr muryarta can kasa sannan cike da rawa . sai lokacin ya cire hannuwansa dake sarke cikin juna ya d an kalleta ,gabad aya ta dawo kalar tausayi amman ko kad an bai ji wannan tausayin ba acikin ransa . har sanda ta cigaba da magana nasan baka yarda da wannan aure ba ,sannan baka sona amman at least dan allah ka boye wannan rashin qaunar da kake min a idanun mutane, idan ya zama dole sai ka nuna ka nuna shi atsakaninmu ,saboda samun kwanciyar hankalin mami ,aunty shahida da sauran yan uwana bana son na gansu cikin damu I can t do it and I can t accept this marriage ban tsara rayuwata dake ba gbdy bakya cikin tsarin rayuwata. ya katseta ta hanyar fad ar haka why sweetheart ? me yasa kike son tursasa zuciyata?shiru tayi tare da runtse idanuwanta hawayen dake boye cikin kwarnin idanunta suka samu nasara zubowa,ba tayi yunkurin sake cewa komai ba ta bude kular abinci ta zuma masa wani ta mika masa ya adam eat your food zan juri komai amman bazan iya jurar rashin cin abincinka ba . kin amsar plet din hannunta yayi dan baya ji zai sauko haka cikin sauki ya rungume aurenta never yatsan hannunsa ya kai ya nuna mata bakin kofar fita please leave i don t want to see your face ya furta a tsawace ya Allah ta furta a fili tana sauke naunayen ajiyar zuciya sannan ta cigaba da kallonsa fuskar nan nashi a d aure kamar koda yaushe, amman yaya .. I said leave ya sake nuna mata hanyar fita daga d akin maryam kam gbdy ta rikice ta rasa abinda zatai jiki a sanyaye ta mike har tayi taku biyu tajiyo sautin muryarsa a kasalance tankar bashi ya gama rashin mutun ci ba ki d auke wannan banzar abincin naki ! lumshe idanunta tayi tana mai had eye kololun bakincikin daya tokare mata qirji ta dawo ta durkusa ta d auki tray ta fito ta shiga d akinta . A fusace ta dangwarar da tray a qasa ta d auki wayarta ta soma neman layin mahaifiyarta kira d aya ta d auka Umma akwai matsala fa, ta fad awa mahaifiyarta haka cikin tashin hankali da kidema. Akwai matsala kamar ya yaya Adam fa yau ma bai ci abincin ba ,coffe ma dana had a masa ya kwa be ban san me
Chapter 42 · 0% Book details