← Book details Huyaam Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 35 OF 85

Sashe 35

Huyaam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

gama free pages Regular group akan naira 500 kacal idan kuma muka gama Free pages zai koma 700 ne.ga masu buk'atar Vip Kuma 2 pages a Rana zaku iya biyan nai 1000 kacal. ku hanzarta ku fara biya tun kafin mu gama free pages.zaku iya tura kud'in ta wannan account d'in 2270127432 Naja'atu umar Zenith bank Evidence of payment (shaidar biya )via 07066508376 Da zarar mungama free pages Kuma zamu sa duk Wanda ya biya kud'in sa a paid group, karku bari ayi wannan tafiyar Babu ku mutanan arziki. 07966598376________ Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/DC2ekqRnajZAQQvErdaWfD HUYAAM *NA* *__NAJA'ATU UMAR FAROOQ __* *__(MRS SARAKIES )__* PAGE 2 *Tallah! Tallah!! Tallah!!!* *Ina kuke hajiyoyin gidan nan,nace Ina kuke hajiyoyin gidan nan?to maza ku matso ga wata garab'asa ta zomu har inda kuke *Hajiya kaya Kikeso na fita kunya cikin taro ku Kuma so kike kallo ya koma akanki acikin Taron mata idan kika shiga biki ko suna ko Kuma Wani taro na musamman.to maza idan kina so ki kankarowa kanki mutunci kizo UK collection and gallery mu gwan gwajeki da kayanmu masu quality Wanda zaki gaji ki ajiye Dan kanki Amma badai ya mutuba Muna sai da kaya kamar haka *Atamfofi da lesses* *Abaya* *Shadda* *Hand bag* *Shoe* *Veil na manya Dana Yara* *Socks rin hands made d'in nan masu net*. *Hula ta 'yan Gayu* *Siyan D'aya ko sari* *Duk zaki samu kan Farashi Mai sauki kedai ki garzayo UK collection & gallery Kisha Mamaki* *Domin ganawa damu ko magana damu kai tsaye ku tun tub'emu kai tsaye ta wannan number kamar haka* 08135305790 *Sai mun jiku *Bismillahirrahmanirrahim* _____________ *Masarautar zazzau* Thursday day,11:20am Wata matashiyar yarinya ce k'arama wacce a shekaru a k'alla baza ta wuce 13 year's ba, Zainab kenan Mai sunan inna Babar Mai martaba wato sarkin masarautar zazzau na yanzu.saukowa take daga stairs d'in da zai SADA ta da k'aton falorn wannan b'angaren. dogowar rigar abaya ce a jikinta bak'a Mai adon stones sai Wani walwali suke Yi wacce ta fito da ainihin haskenta domin farace K'al kamar ki tsaga Jikinta kikaga jini haka fatarta take, wajen kyau kuwa kamar ki sace ta ki gudu Dan kyau, bak'in gashinta Wanda yake har saman goshinta Wanda ya K'ara fito da ainihin kyanta anyi mata parking d'insa anan tsakiyar kanta sai mayafin abayar data D'ora anan saman kanta Amma Kuma Hakan Bai Hana gashin kan nata lek'awa ta k'asan mayafin ba. hannunta Kuma rik'e yake da Wani glass bowel madai daici Dake shak'e da kayan fruits. sannu a hankali take tafiya cikin nutsuwa harta gama saukowa downstairs d'in, Wani D'an corridor tabi Wanda zai SADA ta da d'akin matar gidan wato amaryar Mai martaba Mai suna gimbiya Aysha!, Bud'e k'ofar bedroom d'in tai bayan ta isa tai knocking k'ofar. "shigo". haka aka fad'a daga ciki . bakinta d'auke da sallama ta shiga d'akin ta tarar da wata matashiyar mata wacce a k'alla a shekaru zatai 28 years haka.sai wacce ke kwance a saman gadon kanta saman filo an lullube'ta da bargo har saman kanta.kamar babu lafiya dai a yadda naga yanayin nata. "sai yanzu kika dawo?..." Matashiyar matar Dake zaune gefen gadon tai mata tambayar tana tsare Zainab wacce ake K'iranta da Anam da ido.Anam ta k'araso cikin d'akin bayan ta rufe k'ofar ta ajiye bowel d'in hannunta nan saman table d'in Dake gab da gadon kusa da matar ta marai Rai ce tace. "babu a kitchen d'in downstairs fa Saida na Haura sama". Ta fad'a tana fiki fiki da ido .Matar na kallonta tace. "ai dama bance kije kitchen d'in downstairs fa Anam haka nace Kije sama ki kawo mata,bance ki Daina zuwa kitchen d'in downstairs fa?..."Ta fad'a da sigar worning.Anam ta D'an rausayar da kanta tana kallan matar tace. Na manta ne Anty". Matar ta d'auke kanta daga kallanta ta d'auki bowel d'in ta rik'e a hannunta sannan ta kai hannunta ta yaye blanket d'in da matar take ciki ta kaishi dai dai kirjinta, Bud'e idon tai tana kallan anty Amina idanuwanta a kumbure bakinta a bushe kamar Wanda ba'a kula dashi ,sai dai a'a ba haka bane ba ana kula dashi har ita Kanta matar yadda ya kamata.anty Amina ta sakar mata murmushi tai k'asa da murya dai dai yadda zata jita tace cikin lallashi da kalamai masu da Dad'i da ratsa zuciya Wanda a kullum take mata su . "Yaya gimbiya ga fruits d'in an kawo Miki wanne zakici water milon ko Kuma bana nan?." Ta fad'a tana kallanta kamar Wanda zata ansa mata .sai kuma ta cigaba tace. "Anam ce ta yanko Miki da kanta Kamar yadda kika buk'ata".ta k'arasa fad'a tana sakar mata murmushi.gimbiya Aysha ta lumshe idonta.hakan yasa anty Amina ta Gane Mai take nufi bi ma'ana dai zata Sha d'in kamar yadda anty Amina ta tambayeta.mik'ewa Anty amina tai ta dag'o da Gimbiya Aysha sannan ta jinginar da ita jikin gadon bayan ta tokare ta da filos yadda baza ta fad'i ba. Ganin ta zaunarta dai dai yasa ta d'auki bowel d'in ta fara Bata water milon d'in a Baki Wanda da k'yar ma take Sha Dan Saida dabara inba haka ba gabad'aya zubewa zai dingayi tun kafin ma yaje bakin nata .Anam dai ta haura saman gadon tana zaune kusa da mamar tata ta rik'o hannunta tana kallan yadda take shan fruits d'in cikin tausayawa.kallanta kawai take kamar ta samu TV..Bata shanye fruits d'in ba ta lumshe idonta alamar ta takoshi Hakan yasa anty Amina ta ajiye a nan kan table d'in ta Kalli Anam tace. "Mik'o min tissue na goge mata bakin?..." Matsawa Anam tai daga kusa da maman nata ta Sauka Saman gadon ta k'arasa gaban mirror ta d'auko tissue ta dawo ta Mik'awa anty Amina.anty Amina ta karb'a ta goge mata Bakinta da duk inda water milon d'in nan ya Bat'a mata Jiki.knocking d'in k'ofar akayi anty Amina ta juya tana kallon k'ofar kafin tace. "Waye?....". Baba uwani ce tai magana da nice Hakan yasa anty Amina Bata iznin shigowa..... Da sallama a bakin Baba uwani ta shigo d'akin ta K'araso ciki tana kallon anty Amina da ladabi tace. "Yauwa gimbiya Amina nace na gama bari na shiga na Had'a ruwan wanka yanzu ko?..." Ta fad'a tana kallan anty Amina..Anty Amina tace. "Eh to baba jeki had'a d'in".baba uwani ta ansa mata da to Sannan ta shiga toilet d'in Dake cikin d'akin. Babu dad'ewa ta fito tana kallon anty Amina tace. "Na had'a". Anty Amina tace. "To zo mu kamata sai akaita ai matan". Babu musu baba uwani ta matso suka kama gimbiya Aysha wacce babu inda yake motsi ajikinta suka shigarta cikin toilet d'in da dabara da komai .kafin su fito har Anam tashi ta canza bedsheets d'in saman gadon tasa Wani ta graya d'akin ta kunna borner sannan ta fita da bowel d'in zuwa kitchen. Tana dawowa d'akin ta tarar har amfito da gimbiya Aysha anty Amina ma tana shiryata, k'arasawa tai cikin d'akin ganin ansa wa gimbiya Aysha wata doguwar riga marar nauyi Mai bala'in tsada sai gashinta Wanda har yau Yana nan saidai raguwar da yayi kad'an anty Amina ta gyara mata shi tanaso ne anjima ko Kuma gobe idan Allah ya kaimu zatai mata kalba.Anam ta k'arasa har gaban mirror ta d'auko turare ta fesa mata tana kallanta tana murmushi tace. "Mami kinyi kyau". ta fad'a tana kallanta". Gimbiya Aysha na kallan Anam ta lumshe idonta alamar taji Dad'i Amma Batai magana ba.anty Amina ta kwantar ta saman gadon bayanta ta D'ora kanta saman filon ta d'auko sabon blanket da Anam ta d'auko mata ta rufa mata dai dai k'ugunta. Anty Amina Tana kallan Anam tace. "bari naje gun sultan d'azu da kika lek'a ayaya kika sameshi?..." Ta fad'a da sigar tambaya.Anam tace. "Eh! na sameshi ya fito daga wanka Yana karanta Wani littafi". Anty Amina ta Sauke numfashi ta rik'e hab'a tace. "iKon Allah jiya fa haka muka kwana Yana ta ihu d'azu bayan ASuba Kuma Dana lek'a na samu Yana bacci ,gashi yanzu Kuma da kikaje kince wanka yayi harma Yana karatu". Anam na murmushi tace. "Wallahi Anty harda hira mukayi wai ranar Monday zai koma school". Anty Amina tai murmushi tace. "To Allah ya K'ara musu lafiya Baki D'aya". Anam tail ansa da Ameen jiki a Sanyaye........ Anty Amina ta fita daga d'akin Zuwa d'akin sultan.Anam Kuma ta koma saman gadon ta zauna kusa da maman nata tana tofa mata addu'o'in da duk ta iya kamar yadda Wani malamin islamiyarsu ya koyar da su indai suna tare da Marar lafiya .gefe D'aya Kuma ta tsura mata ido tana Kallanta haka take kullum inta zauna tare da ita tayi ta kallan mamar tata kenan kamar ta samu TV... Anty Amina tana shiga d'akin sultan ta tarar dashi Zaune saman gadon sa wanda yake a gyare tsaf dashi har ga hand out rik'e a hannunsa har lokacin Yana karatun kamar yadda Anam ta fad'a.d'ago da kansa yayi jin anbud'e k'ofar Yana kallan anty Amina harta k'arasa shigowa cikin d'akin, sauke idonsa yayi Daga kallanta da yake Yi Yana ansa mata sallamar tata .anty Amina na murmushi ta zauna gefen gadon da yake kai tana kallansa har lokacin tai k'asa da murya tace. "karatu kake sultan?.."Batare da ya dag'o ba ya gyad'a mata kai .anty Amina tai murmushi tace. "To ya jikin?..."nan ma da ka ya ansa mata. Tace. "Kai min magana mana sultan?..." Ta fad'a tana Marai raicewa.ya dago ya kalleta ya D'an ware mata ido Yana murmushi Amma baiyi magana ba .anty Amina tana k'ok'arin mik'ewa tace. "Tunda baza kai min magana ba sai anjima". Tana fad'ar haka ta Mik'e.sultan ya rik'o hannunta Yana d'an murmushi yad'an Motsa bakinsa kad'an yace. "Me kike so nace". Anty amina tace. "Dama so nake kai magana kuma gashi kayi,nifa nafison duk lokacin da nake maka magana ka dinga ansa min bawai kadinga ansa min da ka ba". Yana rik'e da Hannun ta har lokacin yace. "In Sha Allah" sannan ya saki hannun nata .anty Amina tace. "me kake so ai Maka for lunch?..'ya Dan d'age kafad'a yace. "Koma meye zanci". Tace. "Ok, Amma kafin nan ka kunna Karatun Al'qur'ani da Kuma addu'o'in yanzu kaga Rana tayi ?.."yace. "Ok" anty Amina tace. " To na tafi sai anjima". Yace. "good bye" daga
Chapter 35 · 0% Book details