← Book details Huyaam Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 24 OF 85

Sashe 24

Huyaam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

ruwa kafin mu fito".ko kula ta Huda batai ba ta shige kitchen d'in...... *China Dawowarsa kenan daga companyn dayaje ya duba kayan da zasuyi order Wanda za'a kai musu can Ingiland d'in.gabad'aya a gajiye ya dawo gidan Dan jiya basu suka iso china ba sai wajen k'arfe D'aya Saura na dare direct hotel d'in da Yay mana tun acan ya sauka . Koda ma'aikatan suka kai masa kayansa ciki iya wanka kawai ya iya yi saboda gajiya yana Yi kuwa ya haye saman gadon ya kwanta ko abinci Bai ciba da yake dama shi abincin dare Bai Wani dameshi ba Barshi da Shan coffee ko tea idan yasha ya isheshi . washe gari Kuma Daya tashi bayan yay sallahn ASuba Bai koma bacci ba wanka kawai yayi ya shirya ya fita daga hotel d'in gabad'aya ya tafi inda zasu had'u da a bakon business d'in nasa .daga nan Kuma suka je company da zaiyi order kayan nasu Daya zo yi.to tunda yaje shine fa Bai dawo ba sai yanzu bayan sallahn isha'i wajen k'arfe 9 saura na daren ranar kenan Dan ma duka yayi sallolinsa a hanya. Wanka Yay kawai ya shirya cikin pajamas d'insa masu taushi Wanda ko ba'a fad'a miki ba ido ma kad'ai ya isar ya tan tance Miki cewar kayan nan masu bala'in kyau ne da tsada ne. Fitowa Yay daga d'akin rik'e da wayar sa ya k'arasa falon ya zauna saman kujera ya Bud'e wayar tasa ya tura Sak'o Sannan ya ajiye nan Saman kujerar ya mik'e ya k'arasa wajen socket ya kunna sannan ya d'auki remote yay powering TV ya koma ya zauna a inda yake Zaune. babu dad'ewa Yana Zaune akai knocking d'in k'ofar falon ya d'aga kai ya Kalli k'ofar sannan ya Bada iznin shigowa.wata ma'aikaciyar hotel d'in ce tashigo falon hannunta rik'e da tray ta k'arasa har Cikin falon ta ajiye tray d'in nan kan center table d'in Dake tsakiyar falon bayan ta ajiye ta d'ago da kanta ta Kalli Afeef tace. "Good evening sir ur dinner is here".ta fad'a cikin girmamawa .Batare da Afeef ya K'ara kallan taba idansa Yana kan TV dan tunda ya kalleta saud'aya data shigo Bai K'ara kallantaba ya Motsa bakinsa kad'an yace. "Okay". A tak'aice.ta juya ta fita daga falon ta kullo masa k'ofar.sai wajen 40 seconds da fitarta sannan Afeef ya iya jawo table d'in zuwa gabansa ya tsaya Yana kallan tray d'in,cup d'in coffee ne Wanda sai turiri yake saboda zafinsa sai milky donot d'in da aka d'oro akai.ya sauke numfashi iya cup d'in coffee d'in kawai ya d'auka ya kai bakinsa.ya fara sipping a hankali Bai shanye duka ba ya ajiye ragowar nan saman tray d'in ya d'auki wayarsa Yana Kallan time furzar da huci Mai zafi yay daga bakin sa ganin dai dole sai yayi two days a china baiso zai kai har Friday a china ba yaso ace ayau zai koma Amma Kuma Hakan Bai yuba dole sai dai gobe idan Allah ya kaimu,goben ma yasan bazai gama abinda yake da wuri ba Dan jirgin dare zaibi zuwa ingiland daga can Kuma yace zaiyi shirin tafiya Nigeria Dan dole sai ya koma tacan ingiland d'in yaga kayan da aka kai musu sannan ya wuce Nigeria.numfashi ya Sauke Yana cigaba da lissafin yadda zaiyi squeezing time a ranar Saturday ya isa Nigeria.wayarsa ya d'auka ya duba jirgin da zai tashi aranar Saturday d'in da Kuma time k'arfe biyu yaga jirgin zai tashi a ranar asabar Kuma iya na lokacin ne daga shi Babu wani take yay booking sannan ya Maida wayar ya ajiye sai Kuma ya mik'e ya kashe TV sannan ya shiga d'aki ya kulle k'ofar.k'arasawa yay cikin d'akin har inda kayansa suke brave case d'insa ya d'auka ya Bud'e ya ciro laptop d'in shi aciki sannan ya k'arasa saman gadon ya zauna ya fara duba abun da aka tura masa d'azu daga can Ingiland d'in ko mintuna 20 baiyi ba ya kashe laptop d'in sannan ya rufe ya Maida inda ya d'aukota ya haye saman gadon ya kwanta ya lumshe idonsa Yana karanto addu'ar bacci Ahaka nan da Nan baccin kuwa ya d'auke shi ASuba ta gari Afeef....... _____________ *Nigeria k'asa ta *Friday 4:10pm* Huda ce zaune a d'akin HUYAAM Dan yau anan tazo ta tare tana gaban mirror idar da sallahn ta Kenan ta mik'e ta zauna kan stool d'in mirror tana kwalliya. Bude k'ofar toilet d'in d'akin akayi Huyaam ce ta fito d'aure da towel sai hijab Data D'ora akai. daga wanka ta fito Dan naga sai d'igar ruwa takeyi ta tsaya daga nan Bakin toilet d'in Bata k'araso ciki ba tsaya tana kallan Huda da mamakin haryanzu bata bar d'akin ba ta Bat'a Rai ta tura Baki gaba tace. "Meye haka Huda? dama Baki Fita daga d'akinba kinsan fa wanka nashiga fa ko".ta fad'a tana kallan Huda.batare da Huda ta jiyo ba ta k'arasa gaban wardrobe ta Bud'e ta d'auko Irin karan data sa ajikinta doguwar rigace ta atamfa Irin tata sak da tasa ta ajiye nan saman gadon sai Kuma ta juyo tana kallon Huyaam tace. "To dana San zaki shiga wanka sai akai yaya ?. Ta fad'a tana Bud'e ido.. Huyaam ta karasa cikin dajin tace. "Ban saniba ai kinsan dai idan na fito shiryawa Zanyi dai koh?.."Huda ta d'auki mayafinta ta nufi k'ofar fita daga d'akin tace. "Da kinyi hak'uri ma kinsan ba zama Zanyi ba uwar iya".tana fad'ar Hakan ta fice daga d'akin HUYAAM ta murgud'a mata Baki kamar Huda na kallanta sai kuma ta tafi ta kullo k'ofar sannan ta dawo ta zare jihab d'in jikinta ta Mai da toilet d'in sannan ta fito ta k'arasa gaban mirror ta fara Shafa lotion d'inta .bayan ta gama ta shafa powder kafin ta k'arasa inda Huda ta ajiye mata kayan Data fito mata dashi tasa San ta dawo gaban mirror tai d'auri bayan ta gama ta d'auki lip balm ta shafa a lips d'inta sannan ta d'auki turare ta fesa ajikinta ta tsaya tana kallan kanta a mirror. "ya Allah". haka na ambata araina Huyaam she looks more gorgeous dan ba k'aramin kyau tai ba ko yaya tai kwalliya sai kinga tayi kyau sosai A rayuwar ta tana San kwalliya ko kad'an Bata tab'a zama da datti Babu laifi tana da tsafta sosai kai bama ita kad'ai ba har Hudan dukansu suna da tsafta iyaka yadda ake San mace da ita .matsawa tai daga gaban mirror ta k'arasa kan gadon ta d'auki mayafinta Irin na Huda Wanda ta ajiye mata sannan ta nufi k'ofar fita daga d'akin ta jawo k'ofar ta rufe.ta tabi Wani corridor Wanda zai sada ta ta d'akin Ammie saida tai knocking k'ofar kafin ta tura ta shiga d'akin Bakinta d'auke da sallama.Ammie ta tarar tana zaune kan darduma tana karatun Al'qur'ani tunda ta idar da sallahn ASR Bata tashi daga gunba . Ammie ta d'ago bayan ta kai aya ta amsa sallamar Huyaam tana kallanta . Huyaam tai murmushi ta k'arasa kusa da ita ta zauna k'asan carpet d'in d'akin tace. "Ammie Ina wuni". Ammie ta ansa mata tana kallanta kafin tace . "An shirya kenan?..."ta fad'a tana murmushi.Huyaam ta gyad'a mata kai.sai Kuma tace. "Ina Hudan take?.." tun kafin Ammie ta rufe Baki Huda tai sallama daga bakin k'ofar tana shigowa ta kalli HUYAAM tace. "Na shiga d'akin ba kyanan Ashe nan Kika zo to ki taso mutafi ke muke jira tun d'azu fa". Ammie tace. "Tashi kuje sai Kun dawo ku gaida mutanan gidan dukansu".suka ansa mata kafin Huyaam tabi bayan Huda wacce har ta fita daga d'akin. Ammie ta Maida kanta ta cigaba da karatunta. Koda suka fita daga b'angaren nasu ya Zarah ce agaba tana rik'e da Hannun muneefa D'aya hannun kuma tana rik'e da wayarta bayanta Kuma Huda da Huyaam ne suna tafiya suna hira k'asa k'asa harda murmushi da kin gansu gwanin sha'awa twins sak.har suka isa b'angaren fulani Salamatu suka k'arasa shiga falon bakinsu d'auke da sallama Babu kowa a falon sai hadimar ta guda d'aya wacce ta shigo falon yanzu Jin sallamar tana kallansu ta risina tace. "Allah ya taimakeku Barkanku da zuwa gimbiyoyin masarautar kano"ta fad'a cikin kirari ya Zarah tace . "Baba karima Ina mummyn take?...." Baba karima data d'ago da kanta k'asa tace. "eh to,sun fita d'azu Babu dad'ewa gabad'ayansu kuma ni bansan inda suka tafi ba".ya Zarah tace. "shikenan Bari mutafi idan sun dawo kice mata munzo sannan Ammie tana gaida ta". baba karima tace. "To to Shikenan zan fad'a mata in Sha Allah takawarku lafiya 'ya'yan sarki Kuma jikokin sarki ".ya Zarah ta ansa suka fita daga falon .bayan sun bar b'angaren su Aziza part d'in su ikleema suka shiga nan ma dai Basu Dad'e ba suka fito Dan Irin tarb'ar da aka Saba musu ita akai musu wannan Karan ma inda sabo su kan ai sun Saba ma ikleema ce kawai ta sake dasu har ta rakosu Bak'in part d'in sannan ta koma daga nan b'angaren antynsu ikleema suka shiga nan ma dai Basu Dad'e ba suka fito sai suka k'arasa last part wato part d'in su safnah. Sun shiga sun Tarar da gabad'ayansu zaune a falon har lamid'o Wanda ke zaune suna magana da umminsu atare suka ansa musu sallamar su har suka k'araso suka zauna suka gaida ummi ummi ta ansa musu da kulawa kafin su gaida ya lamid'o. Lamid'o ya ansa musu da murmushi a fuskarsa Yana kallan Huyaam kafin ya janye idonsa ya mik'e Yana kallan umminsu yace. "Bari naje na dawo ummi".ummi tace. "shikenan sai ka dawo".sai Kuma ta Maida kallanta kan su ya Zarah ganin sun zauna k'asan carpet tace. "Ku tashi ku hau kan kujera mana ku Zauna Zarah".cikin Jin kunya suka mik'e suka hau saman kujerar ta Kallesu da murmushi tace. "Ina Ammie?...".ya Zarah tace. "Tana gaishe ki ". Ummi tace . "Ina ansawa". Sai Kuma ta kalli HUYAAM tace. "ya jikin daughter?jiki ya warke ko?.."Huyaam tai murmushi tace . "Da sauk'i ummi". Ummi tace . "Allah ya Kara lafiya naje jiya ai kina bacci". HUYAAM tai murmushi Amma batai magana ba.ruwa da drink's safna ta kawo musu kafin ta koma ta zauna kusa dasu HUYAAM Suna hira.sun Dad'e a b'angaren su safna kafin suyiwa ummi sallama su tafi ganin ana K'iran sallahn magrib...A hanya suka had'u
Chapter 24 · 0% Book details