← Book details Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 99 OF 117

Sashe 99

Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Domin kuwa shekara daya tal da haihuwar jawahir.....na sake samun wani cikin,shima dai mai wahala kamar wancan,ni kadai nake wahalata nida zuwaira da harira,amma a gaban idanun mutane kuwa,ciki harda rashid.....tsinke jidda bata bari na daga,abun ya zame min jiki,ba baqona bane,don ta qware wajen iya wannan.

Kwatsam rana tsaka ina zaune da wani yammaci saiga rashid ya fadomin afujajan,jidda na biye dashi a baya cikin tashin hankali tana qoqarin riqeshi,tare da neman ya tsaya,amma yana qwacewa yana sake yin gaba,ina zaune a inda nake ban motsa ba har ya iso gabana

"Waye uban wannan cikin na jikinki?" Itace tambayar daya jeho min,tambayar data rudani har na miqe tsaye ba tare dana sani ba,saboda ban taba kawo fitar irin wannan tambayar daga bakin rashid ba,ko wanne irin xama kuwa muke,na maida masa da amsar cewa.....bashi da uba daya wuceshi,saiya jefomin takardar hannunsa,wadda ban iya dauka na duba ba,shima bai iya tsaiwa na duba din ba ya shiga bayanin

"Tun bayan buguwar da nayi watannin baya da suka shude aka yimin gwaji,wanda bai fito ba sai cikin satin nan,suka kuma shaida min akwai jijiyoyina da suka tabu,wanda bazan sake samun haihuwa ba sanadiyyar hakan,a ina kika samo wannan cikin?" Maganar data sanya jiri ua debeni ya maidani kan kujerar dana tashi a kanta,innalillahi wa inna ilaihi raji'un na dinga maimaitawa,ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba,ya kuma barmin gargadin cewa lallai ne na samo uban cikina.

Wannan shine abunda ya kusan tarwatsa rayuwata,ya kuma kaini kabari tun jidda bata gama shirin kaini ba,cikin gidan ya zame min tamkar sansanin yaqi,duk wani sauran farinciki da walwalata da nake tattali gaba daya suka yi nasu waje,babu mai kusantata da zuwa inda nake,hatta dasu bibi,duk da cewa su din jidda ce ta kafa musu dokar,matuqar suna son ci gaba da aiki a gidan,amma bibi da harira basu yarda ba,don suna biyo dare suzo su ganni,su kuma kawomin abinci,don bana iya ci,jidda kuma bata damu a bani ba,a sannan nayi burin akwai isassun kudi a hannu na,da babu shakka saidai a wayi gari a ganni a sudan cikin mahaifata,wadanda basu san halin da nake ciki ba,sakamakin bacewar wayata lokaci guda sama ko qasa,ni kuma ba fita nake ba a sannan,ko lecturing din da nake ban iya zuwa saboda azabar ciwo daya hadu da gagarumin baqinciki.

Duk wannan yanayin nida hafsa muke karbar takaicin,a haka ma ina boye mata wasu abubuwan bata sani ba,saboda banason na bata kyakkyawar alaqa da kuma dangantakar dake tsakaninta da dan uwanta,wadda dama tun aurensu da jidda yau shiri gobe fada,kuma duka a kaina ne,ya kuma koka da hakan shi kansa,kan cewa ina shiga tsakaninsa da 'yar uwarsa.

A irin wannan yanayinne wata rana ina zaune,na gama rubuta kan wani mummunan furuci da jidda tayimin daren shekaran jiya,makomata,da kuma hasashen abinda zaizo ya sameni nan gaba muddin naci gaba da irin wannan rayuwar......gidan babu kowa,don ko dama samir yana nan,zanga yana yawan kallona,amma yaqi zuwa inda nake,abun yana daya daga cikin abubuwan da suka sake kassaramin ruhina,gani nan ni ba mutun ba niba mutum mutumi ba,na fice daga kamannina,ina tsaka da tunani na naga inuwar jidda saman kaina,gabana yayi wata mummunar faduwa da ban taba jin irinta ba akan jiddan sai ranar.

"Tun ranar dana sanyo qafata cikin gidan nan zuciyata ke gayamin nazo inda zan huta,nazo inda zanyi kudi nima,nazo inda rayuwar talauci zata qaremin,daga randa nayi ido hudu da mijinki na sake tabbatarwa kaina na samu mijin aure,duk da cikin da nayi sau biyu aka ciremin,wanda baqincikinsa ya kashe kakata dake riqona,abun kunya da gudun talauci yasa na kasa komawa garinmu....cikin farar sa'a kika tsinceni,na gode da halaccin da kika yimin,karki dauka nayi amfani da sihiri ne zalla wajen zama dukkan abinda na zama cikin gidan.....a'ah,KISSA TAFI MAGANI AIKI,kina da kiyaye sallolinki da yawan ambatan sunan Allah koda zama zakiyi ko tashi,na tabbatar wannan kadai zai iya maidamin hannun agogo baya,hakanan sihiri bashi da tabbas,don haka na zabi tsarma shi kadan a guraren da na gaza juyawa, na dan wani lokaci,kafin na maye hikimata da basirata a gurbin wajen,ina me baki haquri da dukkan abinda zai biyo baya.....zan miki alqawari guda daya,ladan halaccin da kika yimin....zan bar danki ya rayu,amma ban miki alqawarin irin rayuwar da kika tsara masa ba......na gaji da ganinki cikin gidana raihana,nayi aiki tuquru na tsahon lokaci,nayi juriya na kuma yi haquri.......ya kamata ki matsa ki bani waje hakanan,albishir guda daya da zan miki shine.....bazan kasheki farat daya ba,amma zan miki daurin rai da rai,irin wanda alqali yakewa me laifi......"

Daga wannan ta fesa min wani abu,wanda ya sanyani ficewa daga hayyacina,na kuma taka da qafafuna na lalubi hanyar ficewa daga gidan,ina iya ganin sanda aka sauke samir daga makaranta,cikin qaramar motar da babansa ya siya masa ya mallaka masa ake kaishi makaranta da ita,wanda da daurin bayan jidda aka siya masa motar,ina iya jin sanda yake qwalamin kira,ganin ban waiwayeshi ba,yasha gabana,naji banason duk wani shamaki da xai tareni daga fita waje,nasa hannu na yageshi na jefar gefe,duk da zuciyata batason aikatawa,amma kawai ji nayi inason na aikata din,babu me gadi babu duk wasu masu tsoron qofar gidan,hakan shi ya bani damar fita ba tare da wani tarnaqi ba.

Ina fita naci karo da wata mota mai baqaqen glass tsaye qofar gidan,tamkar dama suna jiran fitowar tawa ne,suka kamani suka sanyani cikin motar,ban bude idona ba sai cikin wannan dakin da muke ciki a yanzu,wanda na gaza tantance inane?,sai bayan wani lokaci dana fara jiyo ifce ifce da maganganun zararru,sai kuma bayan wani lokaci da aka fara dirka min alluran da suka fara jirkita min kwanyata,da wasu alluran da suka matsantawa cikin jikina ficewa.........

Cikin lokaci kadan gaba daya na daina fahimtar komai,na daina gane dai dai daba dai dai ba,da zarar allura da magungunan da suka dirkamin ya sakeni.....suna fuskantar haka sai su sake danna min wasu,na rasa waye silar kawoni gidan?,wanne laifi nayi?,duk sanda sukazo zasuyimin nakan dage da roqonsu akan su barni,ni lafiyata qalau,ni kadai nasan irin azabar da nakeji,to amma sai naga ko a jikinsu,burinsu su aiwatar da abinsu su fice.

Tunda aka kawoni mutum uku ke shigowa inda nake,kuma har yanzu da nake wannan maganar sune dai babu canji,ban gane wanda ya kawoni ba sai bayan shekara guda sai ga jidda,ranar data zo sai naji sanyi a raina,nayi tsammanin cewa tazo ta fitar da nine daga inda nake din,amma maganganun da sukeyi ya tabbatar min da cewa wannan qaddarar data sameni itace sila,a gabanta aka hada alluran da sukafi qarfina aka danqaramin,tun ina iya ganinta da idanuna dishi dashi har duhu ya mamayeni,sai surutunta da take basu umarnin cewa,a qara yawa da qarfin alluran da ake mini,batason dukka wani hankali da yayi saura a jikina yaci gaba da aiki,daga haka muryarta ta soma cakude min na dinga jin kamar ana ihu saman kaina,alamar alluran sun fara min aiki.

Tun daga randa ta bada umarnin suka matsa qaimi kamar yadda tace,sai na daina ganewa gaba days,tsahon wasu shekaru bansan wacece ni ba,amma iko da hikima ta ubangiji,duk randa tazo kawomin ziyara ina ganewa,duk da zan ganta ne kamar irin a mafarki,saboda rashin wadataccen tunani da aka hargitsa min shi.

Tsahon shekaru masu yawa ina cikin wannaj uquba a wannan kurkukun da bana ganin kowa sai mutum uku,bansan ya akayi ba,cikin wani dare,cikin baccina me kama da mutuwa naji kamar an tasheni,kamar ance TASHI KIYI SALLAH! cikin sautin tsawa.

Ina farkawa na ganni a nan,na soma bin dakin da kallo,ina tuna wasu abubuwa da suka faru dani,ina ganinsu kamar cikin dogon barci me cike da mafarkai,na dinga taba jikina,inason naji a kabari nake ko a duniya nake?,idan a duniya ne ta yaya na farka cikin hankalina?,ya akayi hankalina ya dawo jikina?,ruwan dana gani a gefe na jawo,wanda ba tantama shi nake sha,na daura alwala duk da bani da tabbacin tsarkin jikina dana ruwan,na fuskanci gabas,na dinga salloli,banji na gaji ba tsahon lokaci kafin na xauna ina hutawa,a nan gyangyadi ya fusgeni,a nan wajen na fara mafarkin qaramar yarinya tana jan hannuna zata fiddani daga wani rami,wanda wannan mafarkin shi ya zame min qa'ida kusan kullum.

Na jima ina juya wanda xai xama silar fitata daga wajen,ina juyayin ta yaya yarinya zatayi silar fitata a nan?,amma daga baya nayi istigfari.....na tubarwa Allah,saboda shi din me yin yadda yaso ne a duk sanda yaso,shi ya bani kariya tsahon shekarun da akayi ana dibgamin Alluran da a qa'ida ya kamata ace na rasa hankalina gaba daya ko kuma na mutu......amma ya dawo dani cikin hayyacina,ya kuma dawomin da hankalina,lallai shike raya matacce.

Ban yarda na nuna musu farfadowata ba,wani hikima ta ubangiji.....duk sanda sukazo sukamin alluran da suka saba,zanji babu dadi,zan fita hayyacina.....saidai bana wuce minti ashirin sai ta sakeni,bansan daga ina ubangiji ya saukarmin da wannaj ni'ima tasa ba,ban sani ba ko addu'ar da nakeyi ne?,ban sani ba ko a rayuwata ta baya ina da wani kyakkyawan aiki da Allah ya duba ya bani wannan kariyar?,wannan itace rayuwata tsahon shekaru ashirin da wani abu da nayi cikin wannan gidan.......

Wani irin dummmm gaba daya kaltum taji kanta yayi,hawaye ne kwance shabe shabe saman fuskarta,kallon baiwar Allahn take tana mirgina kai hagu da dama,ta kasa fadin komai,ta kasa cewa komai,tausayinta dana samir ne fal cikin zuciyarta,yayin da tsanar mummy ta cika mata zuciya,ashe tata rayuwar ita da ummans a aljannar duniya suka yita?,ashe duk inda rayuwarka takai ga tsanani akwai wanda ya fika?,ashe wani maras imanin idan yaga wani saiya nemi tsari dashi saboda gawurtar wancan a zalunci?

58

Tamkar wata mashahuriyar barauniya haka ta dinga bibiyar bango cikin sanɗa sanda take baro dakin da momma raihana ke ciki,hikimar ubangiji ce ta sanya ranar gidan kamar anyi shara,duhun magrib yana shigowa zirga zirga ta ragu sosai,qwalla fal idanunta,zuciyarta na mata wani irin ciwo da quna take tafiya,babu abinda ke amsa kuwwa cikin kanta illa labarin momma.

Fuskarta a lullube kanta a qasa ta giftasu,kyauro ne,ya wuce yana sababin bala'i da masifa kan barin qofar dakin da akayi a bude har kawo wannan lokaci,sai data fita wajen gate din gidan sannan ta saki qatuwar ajiyar zuciya,ta tabbatar tayi escape,saura next step kenan.
Chapter 99 · 0% Book details