← Book details Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 59 OF 117

Sashe 59

Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Kana tunanin zan iya hada jiki da wannan yarinyar?,kai anaka tunanin yarinyar ma dukanta ta isa wani moro ne?" Kai ya kada
"Ba haka nakeson matata ta kasance ba,baya ga haka ta yaya zan cutar musu yarinya?,na karbe mata darajarta kuma na rabu da ita alhalin bata yimin komai ba?"

Gira amiru ya dage
"Ok,kawai ka gama bude school din muyi tafiyarmu,dole idan suka gaji da nemanka su warware abinsu su ba wani" fuska saraki ya matse yana dubansa

"Ya kakeson canzawa daga amirun dana sani ne?,ka manta who iam?" Shuru ya sake biyo baya,idanunsa ya janye ya dauki cup dinsa ya sake kurban tea sannan yace

"Zanje kawai na basu haquri kan ban shirya ba na karbi aurenta,zan rubuta mata takardarta na bata kawai shikenan an wuce gurin,ba wani yaudara ko kwana kwana" kai amiru yake jinjinawa,yasan halin samir,dama ba zaya dauki shawararsa ba,yana tarar komai gaba da gaba ne,bai iya boye boye ko qumbiya qumbiya ba,idan kuwa har kaga yayi hakan,to ba qaramin abu bane.

Sanin cewa koda ya sake cewa wani abun,hakan bazaisa samir ya sauka daga ra'ayinsa ba,saiya miqe yaci gaba da shiryawa,dai dai sannan umar yayi sallama ya shigo

"Ka dauki kayanmu duka ka saka a booth,get ready....ana gama bukin bude makarantar gida zamu wuce direct,ya kamata nayi facing my agendas"

"Ok sir" umar ya fada yana jan babbar jakarsa daya zuba komai nasa a ciki yayi waje da ita.

Taro akayi sosai na bude babbar makarantar primary da secondary ta me tafasa,wadda aka canzawa suna,kamar yadda samir din yakeyi a duk sanda yayi wani aiki.

Bangaren primary daban,na secondary daban,ga bandakuna da offices na malamai,abun dai masha Allah gwanin sha'awa,za'a iya gabatar da karatun boko da kuma islamiya duka a ciki.

Duk wani motsinsa yaro daya ya tsaye masa a rai wato bilal,ya dinga kallon guraben dayafi yin aiki a guraren,a irin wannan ranar yayi masa tanadin abubuwa masu yawa da zasu inganta masa rayuwa,saboda yadda ya karanci yana da buri kan yayarsa da mahaifiyarsa,saidai tsarin ubangijinya danne,ya kuma shafe tsarun dukkan wani me tsari.

Farincikin daya gani saman fuskar al'ummar mabuqata,talakawa bayin Allah shi ya dasa nasa farincikin da walwala kan tasa fuskar,har cikin zuciyarsa ya dinga jin farinciki da nishadi,he believes a rayuwa babu abinda yafi ka farantawa wanda yake da buqata ta hanyar biya masa tasa buqatar,yana jin abu daya ne a yanzu ya rageshi a duniya,RASHIN UWA MAHAIFIYA DAURA DASHI,KO TANA INA???,itace tambayar da yake yawan yiwa kansa,yana da tabbacin tana raye,saboda karo na barkatai da yasha yin mafarkinta tana gaya masa cewa tana raye,amma wani SHAMAKI data sanyawa zuciyarsa yasa ya kasa yunqurin komai wajen isa gareta.

*_WAIWAYE......ADON TAFIYA inji masu salon iya magana_*

*ZAFAFANKU BIYAR 🔥🔥🔥🔥sune suka sake dawo muku da wasu nau'in QAWATATTU kuma TSARARRUN LABARAN,masu dauke da SABBIN JIGO na MABANBANTAN LABARAI masu tsuma ZUCIYA*

*_SANIN HALI.....yafi sanin kama,indai kasan TAFIYAR ZAFAFA babu dana sani ko nadama cikin zuba kudi wajen siyan litattafansu,koda jin sunan ma kasan cewa tafiyar ta dabance_*

*GWADA IDAN BAKI TABA BA!!!,HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKAN SAN NA ƘWARAI,burinmu kowa ya shigo cikin tafiyar a dama dashi*

*JERIN SABABBIN LITATTAFAN NASU NA WANNAN KARON SUNE*

*_DEEN MARSHALL👉🏾 Mamuhghee_*

*_HALIN GIRMA👉🏾hafsat rano_*

*_TAKUN SAƘA👉🏾billyn abdul_*

*_SO DA ZUCIYA👉🏾miss xoxo_*

*_ƊABI'AR ZUCIYA👉🏾huguma_*

*DUKKAN WADAN NAN LITATTAFAN ƊAI ƊAI HAR BIYAR...ZAKU SAMESU AKAN KUDI NAIRA 1K KACAL*

2👉🏾400
3👉🏾500
4👉🏾700
5👉🏾1000

*Zaku saka kudinku ta wannan asusun bankin*
6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number

08184017082

*IDAN KATIN WAYA NE KO VTU,SAIKU TURA ZUWA GA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYANKU*

09134848107

*_HAR KULLUM MUNA MARABA DA ALFAHARI DA MASOYANMU_*🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽
#team zafafa biyar

34

Kamar wadda ta tashi jinya haka take tafiya salalo salalo zuwa sashen kawu iliya,hannunta dauke da botikin qarfen inna laure da umma ta bata takai mata,yara suka kawo nan sashen ta suka ajjiye.

Sau biyu tana sallama,saidai kallo daya asiya dake tsakar gida saman kujera 'yar tsuguno fesa kwalliya tayi mata ta baiwa banza ajiyarta taci gaba da kwalliyarta,tana sa ye da wani tsalelen lace,har sai da inna laure dake daki ta fito,tana sanya slippers dinta da asiyance ma ta siya mata

"Au...au ashe amarya ce,amarya manya,amarsu kin sha qamshi,amarya bakya laifi ko kin kashe dan masu gida" kamar hadin baki sai suka kwashe da dariya gaba dayansu,asiya ta fara tsaida tata dariyar

"Ni wallahi Allah har mamaki nake ma yadda kattume ta fito tatsatsanmu,kaf yaran gidan nan babu wanda ya kaita baqi da muni,kiyi haquri fa gaskiyata nake fada,koda yake ma ke da kika kusan tafiyarmi gidan miji....au na manta ban miki Allah ya sanya alkhairi ba,kada ace kana baqinciki,duk da ma kafi qarfin ka yiwa mutum baqinciki,Allah ya sanya alheri,ya kawo tsala tsalan yara" dariya suka sake kecewa da ita

"Ga munu ga talauci,ta ina tsala tsalan yara zasu samu?,don nasan duk wanda ya dauketa dai ajin rayuwarsu daya,tun daga suffa zuwa wadata,ai yara tsala tsala saiku a gidan alhaji uba" farrrr asiya tayi da idanu,kafin su sake cewa wani abu kaltum ta ajjiye botikin ta juya da hanzari,duk yadda taso maida amsa amma ta gagara,kalamansu sun mata muni sosai da bazata iya juresu ba.

A qafa suka tako shida amirun,tun daga makarantar har zuwa qofar gidansu kaltum,amirun yanata mitar yasa takalmansu duk sunyi qura,me yasa bazai bari a qaraso dasu a mota,bai kulashi ba har suka qaraso qofar gidan.

Qarqashin bishiyar dake basa iska a wajen ba kowa sai kawu ado da babban dan yakumbo indo,a nutse suka qarasa da sallamarsu,saiya miqe daga kashingidar da shi kawu adon yayi ya zauna sosai yana amsa sallamar,tare da basu damar zama.

Takalmansu suka tube sannan suka zauna din,sukayi musabaha mai cakude da gaisuwa ya amsa musu,shuru ya ratsa na sakanni,sai amiru yace

"Wajen mai gidan mukazo"
"Wanne daga ciki?"kawu ado ya tambaya yana kallonsu sosai,sabida baqin fuska ne a wajensa

"Baban kal.....kal" samir ya fadi yana kakarewa,saboda son tuna sunan da yake qoqarin yi

"Baban kaltume?" Kawu ado ya qarasa masa,sai amiru ya gyada kansa yana cewa eh

"Ko kaine mijin kaltumen?" Kawu ado ya tambaya yana duban amiru,sai yadan daririce,hakan yasa samir ya nuna kansa

"Nine" kallonsa ya dauke daga kan amiru ya maida ga samir yana qare masa kallo,gami da fadin

"Ma sha Allahu,sannunku dan samari,dama ina bidar ganinka kuwa" kawu ado ya fada yana gyara zamansa sosai.

Kwarjini yadan yiwa samir din ganin yadda kamalarsa ta sake fitowa bayan ya zauna sosai yana fuskantarsu,sai shima ya gyara zamansa yana cewa

"Ma sha Allah,nima magana ce ke tafe dani dama"

"To bismillah mana" kawu ado ya bashi dama

"A'ah baba,ba damuwa,ina saurarenka".

"To alhmadlh,nasan dai baka sanni ba,bakuma kasan alaqata da kattume ba,kattume kamar diya take a wajena,diyar yayata ce,banu wani boye boye a tsakaninmu,tunda an riga da an zama daya,duk da dai kai din da alama baquwar fuska ne,to amma kattume marainiya ce duk da tana da uba,sannan ita da dan uwanta gaba daya rayuwarsu ta kawo yadda take akaine a yanzu aboda huwacewar ubangiji kawai,yarinya ce da gwara wani marayan da ita,don Allah,don son annabi,ka riqeta bisa gaskiya da amana,saboda tasha wahalar rayuwa,tun batakai haka ba take ci da kanta danuwarta dama qannenta,tana buqatar matallafi,tana buqatar bangon da zata jingina dashi,munso yi mata hakan,amma bamu samu hadin kai daga wajen ubanta ba,sai muka rakata da addu'a,saboda munsan cewa ita din diya macace,kuma komai daren dadewa zata samu miji ne tayi aure,wala'alla wannan shine silar hutawarta daga dukkan wani qunci da matsi,ka duba darajar fiyayyen halitta kayi mata ruqo na mutunci da adalci.....kai din asalin da inane?" Ya zarce da tambayar samir,bayan yakai qarshen kalamansa da suka sauke duk wani shiri na samir din ba tare daya shirya hakan ba,ya buda baki da niyyar magana hayaniyar yaran data tunkarosu ta mamaye wajen,hayaniyar taja hankalinsu,ya daga kai yana duban yaran da suka taso wani saurayi a gaba

"Kaga da wanda akayi shirin bata nan,Allah ya dubu irin maraici da girman biyayyarta ga mahaifiyarta ya musanya mata,tunda kai din muna kyautata maka zaton alkhairi"

A hankali ya daga idonsa yana dubansa,shine wannan saurayin daya kubutar da ita daga hannunsa

"Meye alaqarsu?" Ya samu kansa da tambayar kawu ado sanda yaga auwalun ya shige cikin gidan,bayan badaru dan yakumbo indo ya kora gayyar yaran

"Dan qanin babanta ne,kuma ba haka suka so ba,don ko a yau auren kattume ya mutu sai sunsan yadda sukayi suka liqa mata shi" ya fada cike da takaici,shuru yadan sake giftawa,saiya sake maimaita tambayarsa

"Yaro dan inane kai?" Kansa yadan saddar qasa,yana tunanin yadda zai yiwa mutumin dake a karkara irin wannan bayanin mahaifinsa

"Ni dan garin azaren jihar bauchi ce,amma kuma a kano nake zaune,anan na taso"

"To...to ma sha Allah,to ta yaya yaro zamu iya samunka kenan?" Shuru ya sake biyo baya kafin ya samu abun fada

"Unguwar makwarari,duk wanda ka tambaya gidan malam nura zai kaika,ka cewa malam nura kana neman samir ko saraki,zai kawoka inda nake"

"Samir,saraki....to to....to shikenan,babu damuwa" ya fada yana jin gamsuwa a ransa,bayan ya hada wannan bayanan,da kuma bayanin da malam amadu yayi masa a tsaitsaye kan cewa su aka turo sukayi ginin makarantar da ake budewa yau,haka kawai yakejin wata gamsuwa da nutsuwa kan yaron,yasan unguwar daya fada din,yakan shiga cikin gari,kuma yana da abokima a anguwar,dake zuwa sari wajensa duk qarshen wata na kayan hatsi.

"To malam samiru banji naka batun da kazo dashi ba".

Shuru ya danyi,yana jin dukkan wani bayani da quduri nasa da yazo dashi yana saraya gami da bin iska,tamkar bayanin da kawu ado yayi masa ya warware komai daki daki ne,sai yaji nauyin mutumin,a yadda kamalarsa take,da irin roqon daya dinga masa da fatan alkhairi,yanzu shi kuma ya buda baki yace yazo sakin diyarsa ne?.

Muryar malam amadu ta ratsa tsakiyar tunaninsa ta tsinka zaren

"Tun yaushe kuka iso malam muhammadu?,kada dai ace daukar yarinyar nan kukazo yi aka barku a nan?" Kallon takaici kawu ado yake bin malam amadu dashi,shi sam.bai damu da sanin komai akan yaron ba?,sai qoqarin cusa masa yarinya yake kamar yar tsuntuwa ba diyar cikinsa ba

"Amm....malam amadu,ni a ganina daukar yarinyar nan yana da buqatar nutsuwa ko kuwa?" Dubansa yayi
Chapter 59 · 0% Book details