Sashe 101
Dabiar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Lokaci yana tafiya" bata iya motsawa a wajen ba har ya bacewa ganinta,saita samu kanta da murguda baki,abinda ba al'adarta bace,yadda ya kashe mata duk wata laka ta jikinta bata jin zata iya ci gaba da aikin,amma kuma ta gefe daya har yanzu idanuwanta na ganinsa tsaye tare da jauhar.....anya a yadda takeji a zuciyarta kuwa zata iya jurar ganinsu a hakan?,wai me ma yasa takejin wannan zafin ne?,bata sani ba itace amsar,sai tana matattun qafafunta ta nufi hanyar gidan.
Tana shiga ta taras tuni bibi ta kusa kammala aikin,ta dubi kaltum din cikin fara'a
"Tunda naga wannan aikin nasan ke kika fara shi" saita maida mata da murmushi,ta samu waje ta zauna suna gaisawa,don bata jin zata iya ci gaba da aikin.
Duk inda bibi ta gifta binta kaltum take da idanu,tana wassafa ta tadda zata iya sanarwa da bibin cewa hajiya raihananta tana raye?,amma kuma wannan shine dai dai lokacin daya kamata ace ta sanar mata din,don haka ta miqe a hankali tabi bayan bibi,wadda ta bude backyard na kitchen din ta shiga tsinko lemon tsami.
"Kinga lemun nan kwana biyu da ba's tabashi sun qara kyau da yawa" bibi ta fada bayan ta waiwayo tana taga kaltum a tsaye,saita qaraso kusa da bishiyar,kamar tana taya bibin duba wadanda zata cira din
"Kinsan kuwa momin samir tana raye?" A bazata maganar ta zowa bibi,har sai da dan bowl din hannunta ya subuce daga hannun nata ya fadi qasa,sa'annan a razane ta juya tana duban kaltum
"Ke 'yar nan?,anya kuwa hankalinki daya?,kinsan kuwa abinda kike fada?,mafarki kikayi ko kuwa?,to idanma mafarkinne kiwa Allah ki yiwa ma'aiki ki shuru da bakinki ba tare da kin gayawa kowa ba".
Idanunta dake cike da qwarin gwiwa,tare da jin cewa zata iya tunkarar komai ta dubi bibi dasu
"Kiyi magana a hankali bibi,tunda bakison kowa ya jimu,a haka duk wanda ya taho zai dauka muna tsinkan lemo ne,zan shaida miki dukkan abunda baki sani ba,amma tabbas momin ya samir tana raye" da qyar bibi ta tattaro nutsuwarta,ta durqusa ta dauko bowl din,ta riqeshi a hannunta kamar yadda yake a dazun.
A nutse kaltum ta bayyana bibi dukkan wani abu da bata sani ba,saiga bibin taja da baya tayi zaman drishan a qasa tana ruwan hawaye,kafin ta zame bowl din daga cinyarta ta sulale goshinta zuwa qasa tayi sujjada,ta dago tana sake sakin kuka tare da kiran sunan Allah cikin girmamawa hamdala da kuma hailala,sai kuma ta taso ta rungume kaltum a jikinta gaba daya
"Tabbas alheri ce ke,ba shakka Allah ne ya jefo dake rayuwarmu gaba daya,don ki fitar damu daga duhu izuwa haske,na fiki shekaru,na fiki sanin duniya da gogewa,amma an sakamin waigin da bazan taba iya tasiri ba,sai gashi ke da qananun shekarunki sha takwas kinyi aikin da babbar mace ta kasa,tabbas ba shakka dukkan wani tsoro ya qare,tunda har muna da tabbacin hajiya raihana na raye....lokaci yayi da jidda zata kwashi kashinta a hannu,zata kuma girbi abinda ta shuka"
"Shine abinda nake tunani,ya kamata ta fito,ya kamata ta huta,ya kamata taga danta da aka rabata dashi tun bai mallaki hankalin kansa ba" kaltum ta fada cike da damuwa tana duban fuskar bibi,bibi data fada nazari........
Bakinsa dauke da sallama ya tura qofar dakin asibitin, professor rashid ya daga kansa yana amsa sallamar gudan dan nasa,fuskarsa ta wadata sosai da murmushi da ganin samir din,abinda daga shi har samir din suka manta yaushe rabonsu da ganin hakan.
Ta wani gefan shima samir din zuciyarsa fes take,cike kuma da farincikin ganin daddyn nasa zaune sosai,mutumin da suka fara debe tsammani da samuwar rayuwarsa,sai gashi a zaune tangargar,saidai yanayi da zai nuna maka cewa lallai yayi jinya,da kuma saran ciwuka qananu dake qafarsa da hannunsa.
Kai tsaye ya isa gaban daddyn,ya fara gaidashi yana tambayarsa jikin nasa,tare da dudduba ciwukan jikinsa
"Da sauqi sosai samir.....Allah yayi maka albarka" daga kansa yayi ya dubi daddyn kafin ya amsa,tunda ya farfado yake sanya masa albarkar da baisan ainihin meye ya kawota ba,abar daya jima rabon da ya jita daga bakin mahaifin nasa
"Kana mamaki ko samir?" Daddyn ya fada da wata karyayyar murya,wadda zata jefa tausayi a zuciyar duk mutumin da ya jita,kasa amsa masa shima yayi,sai tunani da lalube da zuciyar samir din ta tafi....laluben meye haka yaketa karya qwarin gwiwa da jarumatar mahaifin nasa?,kamar yasan tunanin da yakeyi sai yace dashi
"Hadamin ruwan shayi ka kawomin,kazo ka zauna muyi magana" bai musa ba,ya qarasa inda aka kammale duk wani kayan breakfast,tamkar a gida,duk kuma aikin asibitin ne,asibiti ne babba me tsadar gaske,suna da me jinyar patient,sannan duk wani abu da mara lpy xai buqata naci da sha su suke hidimar yi,saidai duk cikin kudinka,hakan ya sanya duk wanda zaka gani cikin asibitin to ba shakka yaci ya sha ya tada kai ne.
"Na gode" daddyn ya fada bayan ya karba cup din da ya tabbatarwa samir din zai iya sha da kansa,samir din na zaune har ya kammala,ya karba cup din ya bashi ruwa
"Sai zuwa anjima,zauna Muhammad" yayi kiransa da sunan da bazai iya tuna when last da yaji ya kirashi dashi din ba
" Da farko abunda zan fara cewa shine....ka yafemin abisa mummunar fahimta dana dinga yi maka tsahon rayuwata,bahagon kallo.....da kuma kallon da nake maka a matsayin da mara biyayya,wanda yake sabawa dukkan wata magana ko qudurina......" Hankalin samir din ne yaji ya tashi,jin mahaifin nasa wai yana neman gafararsa,saiya matso sosai yankama hannun professor din
"Daddy... Meye ya kawo wannan maganar?" Wani busasen murmushi daddyn ya yayi
"Samir....na dade ina jin haushi da takaicinka cikin raina,na dade ina tuhumar kaina ya akayi na haifeka,na dade ina maka kallon bijirarre,ban taba tsaiwa nayi dogon nazari akan hakan ba.....ashe duk abinda kake yi samir baka taba saukeni daga matsayin uba daka daukeni,ashe abubuwa masu yawa da kakeyi kana yine saboda ka gyara sunana ....rayuwata.....da kuma duniyata.....abinda ya faru shine.....lokacin da muke kan hanyar zuwa azare nida baka driver....sakamakon babu wani jirgi da zan samu da zai tashi a ranar,tun kafin mu nausa tafiya na siyi jaridun da suka fita a ranar donsu tayani debe kewa idan muka shiga inda babu service.......katsam ina tsaka da duba jaridun.....saina fara cikin karo da wasu ayyuka,masallatai,makarantu,asibitoci da hanyoyi da akayi a qauyuka masu tarin yawa.....wanda kowanne dauke yake da cikakken sunana, professor rashid azare,wanda kowa yasan duk wanda aka kira da wannan sunan wa ake nufi......nayi mamaki kamar yadda na shiga doubting din waye yake aiwatar da wannana ayyukan da sunana?,daga qarshe sai naga hotunanki a matsayin wanda yake zuwa dukka wadan nan qauyuka da kwangilar aikin.....ya kuma ce daga waje na aka aiko ayi aikin.....,mamaki ya kamani,ban tsaya sanya ba na daga waya,Allah ya taimaka da sauran network bai gama daukewa ba,na kira amiru,bai boyemin komai ba ya gayamin cewa kaine kake wannan ayyukan da sunana,dukka qauyen daka tafi kaje ne saboda kayi ire iren wannan aikin,da sunana bada sunanka ba.....a take abubuwa guda biyu suka sauko suka rufeni,har bansan sanda amiru ya gaji da dakona ba ya kashe wayar.
Abu na farko shine.....kaico da nadamar irin abubuwan da suka dinga faruwa tsayin shekaru,yadda na dinga yi maka.......,kai samir ya daga yana kallon daddyn,wani farinciki yana lullubeshi.
A hankali ta rufe katafariyar cupboard din tata ta alfarma,wadda take danqare da dukiya da kuma dukkan wani abu daya zama sirrin tane,ta waiwayo tana duban najwa dake shigowa
"Ke me yasa har abada idan zaki shiga waje ba zaki koda 'yar sallamar nan ba,na sha gaya miki ki daina min irin wannan shigowar ko?" Dariya ta saki,ta jawo pillow din gadon xata zauna a kai,ta dora saman cinyarta sannan tace
"Sorry" kai ta gyada tana takowa zuwa inda take,batasan me ya sauya najwa din ba gaba daya a 'yan kwanakin,ta lura akwai abinda take boye mata,take kuma nuqu nuqu akai,takardun hannunta ta aje sama madubi sannan tace
"Dama takardun wajenki zaki bani,da sarqoqinki,haka kawai jikina bai bani zamansu a gida nan ba,zan kai bank a ajjiye muku,ga na jawair duka" wani kallo najwan ta yiwa mummyn
"Haba mummy,mufa yanzu ba qananun yara bane da ba zamu iya kula da kayayyakinmu ba,mun mallaki hankalin kanmu,ya kamata a sakar mana mara muyi fitsari" galala tayi tana duban najwan,ta dade da sanin hutsuwa ce ta qarsge,wasu dabi'u da batasota dasu ba ta debo,ranta yadan baci da yadda ta gasa mata magana tana diyar cikinta,saboda haka ta fara magana cikin fada
"Duk hankalin da zakuyi ai baiki na uwarki bako?,to banason shashancin banza,ki tashi kije ki kawomin,tun kafin ranki ya baci" zumbur ta miqe tana cika tana batsewa
"Nifa mummy tsahon lokacin da na dauka ina biyayya tare da bin tsarinki....banga wata riba dana samu ba,a maimakon na zama magajiyar daddy....wadda duk inda yasa qafarsa ya cire zan maidata tawa kamar yadda kike kwadaita min....abun sai ya canza,na qare da komawa aiki a company qarqashi samir,kuma a gaban idahunki,sannan baki iya tabuka komai ba.....to na kwashe dukka takaddu suna wajen fawwaz,ya fara shirya min wasu plan,duk da basu tafi a yadda muka so ba amma na fara ganin alamun nasara" kallo mummy jidda tabi najwa dashi baki bude,gabanta yana faduwa,kada dai ace alaqar soyayyar data dade da guntuleta tsakanin najwan da fawwaz tana na ta sake dinkewa ba tare da saninta ba,ta yaya zata bar fawwaz dan hajiya shuwa ya shiga nasabarta?,kwata kwata basu kai tarin dukiya da arziqin da takewa diyoyinta fatan kasance familyn masu irin wannan dukiyar ba.
Bugu da qari kar tasan kar ne,yaya za'ayi ta tura diyarta cikin mutanen da suka san sirrinta?,kai......ta yaya ma hajiya shuwa zata yarda tabar danta ya auri najwa indai ba akwai wata manufa a qasa ba?" Cikin qarfin hali da zallan bacin rai mummy tace
"Ni mahaifiyarki kike gayawa haka?,wadda ba don naso ba da bakuzo duniyar ba,ba don naso ba kuma da baki cikin daular da kike magana akanta?,fawwaz?.....ban yanke alaqar dake tsakaninku ba?"
"Mummy muna son juna,yana sona ina sonshi,banga aibunsa baiga nawa ba,mahaifiyarsa aminiyarki ce?,me yayi saura banda musha soyayarmu hankali kwance?,gaskiya mummy saidai kiyi haquri,a wancan karon kin rabani da fawwaz....amma a wannan karon.....bazan iya rabuwa dashi ba" daga haka tayi gaba abunta.
Tana shiga ta taras tuni bibi ta kusa kammala aikin,ta dubi kaltum din cikin fara'a
"Tunda naga wannan aikin nasan ke kika fara shi" saita maida mata da murmushi,ta samu waje ta zauna suna gaisawa,don bata jin zata iya ci gaba da aikin.
Duk inda bibi ta gifta binta kaltum take da idanu,tana wassafa ta tadda zata iya sanarwa da bibin cewa hajiya raihananta tana raye?,amma kuma wannan shine dai dai lokacin daya kamata ace ta sanar mata din,don haka ta miqe a hankali tabi bayan bibi,wadda ta bude backyard na kitchen din ta shiga tsinko lemon tsami.
"Kinga lemun nan kwana biyu da ba's tabashi sun qara kyau da yawa" bibi ta fada bayan ta waiwayo tana taga kaltum a tsaye,saita qaraso kusa da bishiyar,kamar tana taya bibin duba wadanda zata cira din
"Kinsan kuwa momin samir tana raye?" A bazata maganar ta zowa bibi,har sai da dan bowl din hannunta ya subuce daga hannun nata ya fadi qasa,sa'annan a razane ta juya tana duban kaltum
"Ke 'yar nan?,anya kuwa hankalinki daya?,kinsan kuwa abinda kike fada?,mafarki kikayi ko kuwa?,to idanma mafarkinne kiwa Allah ki yiwa ma'aiki ki shuru da bakinki ba tare da kin gayawa kowa ba".
Idanunta dake cike da qwarin gwiwa,tare da jin cewa zata iya tunkarar komai ta dubi bibi dasu
"Kiyi magana a hankali bibi,tunda bakison kowa ya jimu,a haka duk wanda ya taho zai dauka muna tsinkan lemo ne,zan shaida miki dukkan abunda baki sani ba,amma tabbas momin ya samir tana raye" da qyar bibi ta tattaro nutsuwarta,ta durqusa ta dauko bowl din,ta riqeshi a hannunta kamar yadda yake a dazun.
A nutse kaltum ta bayyana bibi dukkan wani abu da bata sani ba,saiga bibin taja da baya tayi zaman drishan a qasa tana ruwan hawaye,kafin ta zame bowl din daga cinyarta ta sulale goshinta zuwa qasa tayi sujjada,ta dago tana sake sakin kuka tare da kiran sunan Allah cikin girmamawa hamdala da kuma hailala,sai kuma ta taso ta rungume kaltum a jikinta gaba daya
"Tabbas alheri ce ke,ba shakka Allah ne ya jefo dake rayuwarmu gaba daya,don ki fitar damu daga duhu izuwa haske,na fiki shekaru,na fiki sanin duniya da gogewa,amma an sakamin waigin da bazan taba iya tasiri ba,sai gashi ke da qananun shekarunki sha takwas kinyi aikin da babbar mace ta kasa,tabbas ba shakka dukkan wani tsoro ya qare,tunda har muna da tabbacin hajiya raihana na raye....lokaci yayi da jidda zata kwashi kashinta a hannu,zata kuma girbi abinda ta shuka"
"Shine abinda nake tunani,ya kamata ta fito,ya kamata ta huta,ya kamata taga danta da aka rabata dashi tun bai mallaki hankalin kansa ba" kaltum ta fada cike da damuwa tana duban fuskar bibi,bibi data fada nazari........
Bakinsa dauke da sallama ya tura qofar dakin asibitin, professor rashid ya daga kansa yana amsa sallamar gudan dan nasa,fuskarsa ta wadata sosai da murmushi da ganin samir din,abinda daga shi har samir din suka manta yaushe rabonsu da ganin hakan.
Ta wani gefan shima samir din zuciyarsa fes take,cike kuma da farincikin ganin daddyn nasa zaune sosai,mutumin da suka fara debe tsammani da samuwar rayuwarsa,sai gashi a zaune tangargar,saidai yanayi da zai nuna maka cewa lallai yayi jinya,da kuma saran ciwuka qananu dake qafarsa da hannunsa.
Kai tsaye ya isa gaban daddyn,ya fara gaidashi yana tambayarsa jikin nasa,tare da dudduba ciwukan jikinsa
"Da sauqi sosai samir.....Allah yayi maka albarka" daga kansa yayi ya dubi daddyn kafin ya amsa,tunda ya farfado yake sanya masa albarkar da baisan ainihin meye ya kawota ba,abar daya jima rabon da ya jita daga bakin mahaifin nasa
"Kana mamaki ko samir?" Daddyn ya fada da wata karyayyar murya,wadda zata jefa tausayi a zuciyar duk mutumin da ya jita,kasa amsa masa shima yayi,sai tunani da lalube da zuciyar samir din ta tafi....laluben meye haka yaketa karya qwarin gwiwa da jarumatar mahaifin nasa?,kamar yasan tunanin da yakeyi sai yace dashi
"Hadamin ruwan shayi ka kawomin,kazo ka zauna muyi magana" bai musa ba,ya qarasa inda aka kammale duk wani kayan breakfast,tamkar a gida,duk kuma aikin asibitin ne,asibiti ne babba me tsadar gaske,suna da me jinyar patient,sannan duk wani abu da mara lpy xai buqata naci da sha su suke hidimar yi,saidai duk cikin kudinka,hakan ya sanya duk wanda zaka gani cikin asibitin to ba shakka yaci ya sha ya tada kai ne.
"Na gode" daddyn ya fada bayan ya karba cup din da ya tabbatarwa samir din zai iya sha da kansa,samir din na zaune har ya kammala,ya karba cup din ya bashi ruwa
"Sai zuwa anjima,zauna Muhammad" yayi kiransa da sunan da bazai iya tuna when last da yaji ya kirashi dashi din ba
" Da farko abunda zan fara cewa shine....ka yafemin abisa mummunar fahimta dana dinga yi maka tsahon rayuwata,bahagon kallo.....da kuma kallon da nake maka a matsayin da mara biyayya,wanda yake sabawa dukkan wata magana ko qudurina......" Hankalin samir din ne yaji ya tashi,jin mahaifin nasa wai yana neman gafararsa,saiya matso sosai yankama hannun professor din
"Daddy... Meye ya kawo wannan maganar?" Wani busasen murmushi daddyn ya yayi
"Samir....na dade ina jin haushi da takaicinka cikin raina,na dade ina tuhumar kaina ya akayi na haifeka,na dade ina maka kallon bijirarre,ban taba tsaiwa nayi dogon nazari akan hakan ba.....ashe duk abinda kake yi samir baka taba saukeni daga matsayin uba daka daukeni,ashe abubuwa masu yawa da kakeyi kana yine saboda ka gyara sunana ....rayuwata.....da kuma duniyata.....abinda ya faru shine.....lokacin da muke kan hanyar zuwa azare nida baka driver....sakamakon babu wani jirgi da zan samu da zai tashi a ranar,tun kafin mu nausa tafiya na siyi jaridun da suka fita a ranar donsu tayani debe kewa idan muka shiga inda babu service.......katsam ina tsaka da duba jaridun.....saina fara cikin karo da wasu ayyuka,masallatai,makarantu,asibitoci da hanyoyi da akayi a qauyuka masu tarin yawa.....wanda kowanne dauke yake da cikakken sunana, professor rashid azare,wanda kowa yasan duk wanda aka kira da wannan sunan wa ake nufi......nayi mamaki kamar yadda na shiga doubting din waye yake aiwatar da wannana ayyukan da sunana?,daga qarshe sai naga hotunanki a matsayin wanda yake zuwa dukka wadan nan qauyuka da kwangilar aikin.....ya kuma ce daga waje na aka aiko ayi aikin.....,mamaki ya kamani,ban tsaya sanya ba na daga waya,Allah ya taimaka da sauran network bai gama daukewa ba,na kira amiru,bai boyemin komai ba ya gayamin cewa kaine kake wannan ayyukan da sunana,dukka qauyen daka tafi kaje ne saboda kayi ire iren wannan aikin,da sunana bada sunanka ba.....a take abubuwa guda biyu suka sauko suka rufeni,har bansan sanda amiru ya gaji da dakona ba ya kashe wayar.
Abu na farko shine.....kaico da nadamar irin abubuwan da suka dinga faruwa tsayin shekaru,yadda na dinga yi maka.......,kai samir ya daga yana kallon daddyn,wani farinciki yana lullubeshi.
A hankali ta rufe katafariyar cupboard din tata ta alfarma,wadda take danqare da dukiya da kuma dukkan wani abu daya zama sirrin tane,ta waiwayo tana duban najwa dake shigowa
"Ke me yasa har abada idan zaki shiga waje ba zaki koda 'yar sallamar nan ba,na sha gaya miki ki daina min irin wannan shigowar ko?" Dariya ta saki,ta jawo pillow din gadon xata zauna a kai,ta dora saman cinyarta sannan tace
"Sorry" kai ta gyada tana takowa zuwa inda take,batasan me ya sauya najwa din ba gaba daya a 'yan kwanakin,ta lura akwai abinda take boye mata,take kuma nuqu nuqu akai,takardun hannunta ta aje sama madubi sannan tace
"Dama takardun wajenki zaki bani,da sarqoqinki,haka kawai jikina bai bani zamansu a gida nan ba,zan kai bank a ajjiye muku,ga na jawair duka" wani kallo najwan ta yiwa mummyn
"Haba mummy,mufa yanzu ba qananun yara bane da ba zamu iya kula da kayayyakinmu ba,mun mallaki hankalin kanmu,ya kamata a sakar mana mara muyi fitsari" galala tayi tana duban najwan,ta dade da sanin hutsuwa ce ta qarsge,wasu dabi'u da batasota dasu ba ta debo,ranta yadan baci da yadda ta gasa mata magana tana diyar cikinta,saboda haka ta fara magana cikin fada
"Duk hankalin da zakuyi ai baiki na uwarki bako?,to banason shashancin banza,ki tashi kije ki kawomin,tun kafin ranki ya baci" zumbur ta miqe tana cika tana batsewa
"Nifa mummy tsahon lokacin da na dauka ina biyayya tare da bin tsarinki....banga wata riba dana samu ba,a maimakon na zama magajiyar daddy....wadda duk inda yasa qafarsa ya cire zan maidata tawa kamar yadda kike kwadaita min....abun sai ya canza,na qare da komawa aiki a company qarqashi samir,kuma a gaban idahunki,sannan baki iya tabuka komai ba.....to na kwashe dukka takaddu suna wajen fawwaz,ya fara shirya min wasu plan,duk da basu tafi a yadda muka so ba amma na fara ganin alamun nasara" kallo mummy jidda tabi najwa dashi baki bude,gabanta yana faduwa,kada dai ace alaqar soyayyar data dade da guntuleta tsakanin najwan da fawwaz tana na ta sake dinkewa ba tare da saninta ba,ta yaya zata bar fawwaz dan hajiya shuwa ya shiga nasabarta?,kwata kwata basu kai tarin dukiya da arziqin da takewa diyoyinta fatan kasance familyn masu irin wannan dukiyar ba.
Bugu da qari kar tasan kar ne,yaya za'ayi ta tura diyarta cikin mutanen da suka san sirrinta?,kai......ta yaya ma hajiya shuwa zata yarda tabar danta ya auri najwa indai ba akwai wata manufa a qasa ba?" Cikin qarfin hali da zallan bacin rai mummy tace
"Ni mahaifiyarki kike gayawa haka?,wadda ba don naso ba da bakuzo duniyar ba,ba don naso ba kuma da baki cikin daular da kike magana akanta?,fawwaz?.....ban yanke alaqar dake tsakaninku ba?"
"Mummy muna son juna,yana sona ina sonshi,banga aibunsa baiga nawa ba,mahaifiyarsa aminiyarki ce?,me yayi saura banda musha soyayarmu hankali kwance?,gaskiya mummy saidai kiyi haquri,a wancan karon kin rabani da fawwaz....amma a wannan karon.....bazan iya rabuwa dashi ba" daga haka tayi gaba abunta.